← Book details Naga Ta Kaina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 62

Sashe 4

Naga Ta Kaina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wani irin murmushi daya fi kuka ciwo Naseer yayi ya d'auke hawayen fuskarsa ya kalli Hajara Yana " Ba mutuwa tayi ba ta dai tafi ta bar miki gidan Kamar yanda kikeso ta tafi da Waleed ta bar sauran yaran"

Hajara Kara dudduba d'akin tayi Wai Dan ta gaskata maganar da kunnenta ke jiyo mata

Naseer kuwa yanda Safiyya ta washe baki murnarta na fitowa fili yasa ya fara jifanta da wani irin kallo tayi waje da Sauri

Hajara kuwa ta fito ta lek'a koina taga dagaske dai Naeema Bata Nan ta koma d'akin taja Tsaki Tana "Ni zaku rainawa Hankali yau ta Saba guduwan ta Kuma dawowa Naga Haka kuka rainamin hankali na gano kuna taren yanzu ta Inda kuka Kara b'ullo wa kenan ta tafi idan an kwana biyu sai ka bita Kai da yaran ko"?

"Umma Naeema ta tafi idan da hada Baki mukayi da ita wlh bazaki gani a d'akin Nan Ina kuka ba da ace hada Baki mukayi bazata bar min yaran Nan ba barin yaran Nan da tayi ya Isa yasa kigane gajiya tayi da abinda kike Mata Umma sanin kanki ne banida komai Naeema ita ke rike da gidanan daidai da abincin da zamu ci ita take bamu yanzu data tafi daga Ina Zan fara Umma Ni Kam bansan Mai na Miki a rayuwata ba bansan Mai yasa kike San ganina a kuncin rayuwa ba"

"Ba abinda kamin Dan albarka Naeema ce kawai na tsana karka wani damu da tafiyar da tayi dama so take kawai ta gudu Dan taga ka talauce iya tafiyar da tayi yaci Yasa kagane ba Dan Allah take zaune da Kai ba karka wani damu da ita take komai a gidanan Nima Zan cigaba daga Inda ta tsaya markade ne na iya zobo da ruwa nima na iya k'ulawa ai Dan Haka Kar ka wani damu Dan albarka idan Allah ya yarda da kaina Zan Nemo maka matar da zata zauna da Kai Dan Allah Mai ake da Naeema"

Ta karashe tana yin waje cikin tsananin farinciki kamar wacce akayiwa bushara da gidan Aljanna.

Naseer Bai iya ce Mata komai ba har ta fice Zahira kuwa ta matsa daga kusa dashi ta fita d'akinsu ta cigaba da kukanta Su Nadeeya na k'ok'arin fitowa daga d'akin Dan su shiga d'akin Naeema Suka hadu da Naseer a bakin kofa hakane yasa Suka koma ciki Naseer ya shiga d'akin ya zauna a tsakiyarsu Yana Jin zuciyarsa na Masa wani irin Nauyi Raheema da ke da shekara hudu ya kala ya d'auketa ya dorata a cinya Yana maida hawayen dake neman zubo Masa ya hau magana a fili Yana "Baki kyauta min ba Naeema baki min adalci ba da Kika gudu Kika barni da yaran Nan Mai yasa Kika gudu a lokacin da muka fi bukatarki?Mai na Miki da zafi Haka zakimin Haka"? Kinsan banida kowa sai Allah sai ke sai yarana ku nake gani naji dadi Amma Naeema Kika Shure Kika tafi sabida Mahaifiyata Tana Miki ba daidai ba duk hakurin Dana ringa Baki akan kiyi hakuri da halinta Nima addua nake Akan Allah ya shiryeta Naeema baki zabi guduwa ba sai a irin wanan lokacin ? akanki Mahaifiyata tamin Baki har yau bana ganin daidai duk kudin Dana rik'e basa albarka na zabi Zama dake a kowane Hali na zabi nayi rayuwar talauci Dan kawai na zauna dake Bayan irin kudaden Dana Kama a baya duk ban damu da rasa sun danayi ba sabida ke Amma yau sabida tsangwamar da Mahaifiyata ta Miki Kika gudu Kika barni da Yara Mai yasa Naeema Mai kikeso nacewa yaranmu"?

Naseer ya karashe muryarsa na rawa magana yake shi kadai kamar da Naeema yake magana

Nadeeya da Minal kuwa cewa suke Ina ummansu taje.haka Suka lek'a d'akin Suka dawo Suma Suka hau kukan.

Hakane yasa Naseer ya share hawayensa Yana Zahira ta tashi ta Dora musu abinci su tafi makaranta.

Zahira hka tayi waje tana share hawayenta.

Naseer kuwa ya warware takardar da Naeema ta ajiye Mishi ya fara karantawa *NASEER KAYI HAKURI DA MATAKIN DANA D'AUKA NA RABUWA DA KAI NAGAJI DA ABINDA UMMA DA AUNTY SAFIYYA KEMIN NAGAJI NASEER UMMA TACE NI MAYYA CE TACE NI KARUWA CE BA IRIN ABINDA UMMA BATAMIN INA SHANYEWA AMMA YANZU NAGAJI DAN NAGA KIYAYAR DA TAKEMIN KARUWA YAKE BA RAGUWA BA KIYAYYAR DA TAKEMIN YA SHAFI YARANA GABADAYA DAN HAKA KAFIN NA HAIHU NA MATA ALKAWARIN RABUWA DA KAI INDAI ALLAH YA SAUKENI LAFIYA HAKANE YASA NA CIKA MATA WANAN ALKWARIN DANA D'AUKA NA TAFIYA NA BAR RAYUWARKU NA HAR ABADA ZAN RINGA ZUWA GANIN YARANA INSHA ALLAHU KASA KANKA A MATSAYINA KO KAINE MATAKIN DA ZAKA DAUKA KENAN A KARSHE NASEER NA HADAKA DA GIRMAN ALLAH KA KULARMIN DA YARANA KARKA BARI A CUTARMIN DASU NASEER BAZAN YAFE MAKA BA IDAN WANI ABU YA SAMESU NASERR UMMA TA TSANI ZAHIRA ITA DA AUNTY SAFIYYA NA BAKA LABARIN YANDA SUKE CIN ZALINTA A GABAN IDONA NASAN ZASU IYA KOMAI YANZU A BAYAN IDONA NASEER YARAN NAN AMANA NE A WAJEN MU KARKA BARI MAHAIFIYARKA TA CUTARMIN DASU NASEER KASAN YANDA NAKE KAUNAR YARANA BA ASAN RAINA NA TAFI NA BARSU BA DAN ALLAH KA KULARMIN DA SU NA BAKA AMANARSU AN FI TSANAR ZAHIRA KA SA IDO AKAN SU NA AJIYE MAKA KUDI A KARKASHIN KATIFA MAI YAWA ZAI ISA KAJA JARI KA KULARMIN DA YARANA NA SIYAR DA INJINA NA GUDA BIYU SABIDA NA HADA DA KUDIN WAJENA NA JA JARI NIMA KAYI HAKURI HAKA ALLAH YA KADDARA MANA RABUWAR MU SHI YAFMIN ALHERI DAN UMMA KARFI DA YAJI TAKE SAN KASHENI KAYI HAKURI BA A SAN RAINA NA GUDU BA NGD DA KAUNARKA A GARENI DUK.LOKACIN DANA TASHI ZUWA GANIN YARANA ZAN TAHO DA WALEED KA GANSHI*

cukwikuye takarda Naseer yayi batare da ya karasa karanta Takadar ba sabida yanda jikinsa ke rawa zuciyarsa tayi balain nauyi a fili yace "Ni kuma tawa kaddarar kenan Allah ka bani ikon cinye wanan jarrabawa ka bani ikon sauke nauyin daka doramin na yarana.

Waje ya fita yaga Safiyya na shara tana wake wake su Nadeeya sunyi cirko.kamar marayu

Zahira kuwa Tana Kitchen ta kurawa waje daya Ido

Kitchen din ya Shiga ya cigaba da girkin yacewa zahira ta shirya kannenta kafin ya Gama

Yana gamawa a faranti ya juye musu ya Kai abincin har Palo ya zaunar da Raheema a cinyarsa ya hau Bata a baki Nadeeya da Zahira kuwa kasa cin abincin sukayi duk yanda yayi dasu kuwa Akan suci abincin.

Ahaka suka fito Bayan ya d'auki naira Hamsin ya rakasu har bakin makaranta sai daya ga shigarsu ya koma gida.

Sai dai tundaga nesa ya hango Hajara taci uwar damara ta Hana a fita da engine da wasu maza Suka zo dauka sai balai take tana tsalle tana hango shi ta nufo wajensa da Sauri tana "Kajimin shegu tsinannu Haka kawai suka zo d'aukar engine Wai wacce ta siya ce tace su zo su dauka Naga engine Naeema ne wacce matar Kuma suke magana kaji barayi"

"Naeema ta siyar da engine yanzu ba nata bane masu shine suka zo d'aukar kayansu"

Naseer yace tare da cewa.mazan su dauka su tafi

Ya shige gidan ya bar Hajara na balai bazata yarda a fita da engine ba Samarin kuwa ganin er tijara ce da k'arfi Suka fita da engine Hajara data tare hanya suka hankadata gefe ta zub'e a kasa

Safiyya itama ta hau rantsuwar bazaa fita da engine ba Dan sosai suka.gama lissafa yanda zasu samu kudi da engine Umma har da lissafin zata siyi fili Dan sunga yanda Naeema ke samun kudi da engine markaden sosai suka tiki rawa a dakin Dan murnar tafiyar naeema.sai gashi Ashe ma ta siyar da engine

Suna ji suna gani aka tafi da engine Hajara Kamar tababbiya ta nufi d'akin da Naseer ke kwance.........

*Comment*

Nikuwa aganina batayi kuskure ba
Ayadda Dan Adam,musamman ma mace take da rauni ai baza'ace ma naeema komi ba Dan kuwa tayi balain kokari...
Awajena bunda ya dace tayi kenan adaidai wannan gabar. Ki duba fa
Da can sunce arxikin shi yasa ta makale masa Amma yanzu itace mai rufin asirin Amma kuma sunce kudin karuwanci ne Kuma dan naseer na taimakonta da aikin gida sunce tayi kudi ta mai dashi boyi boyi.
Haba jamaa abun Sam babu dadi gaskiya ko mai tsananin Imani ne saiya raunana..

Tunda har ba ita da bakinta ta nemi saki kotayi fitar fushi wallhy harga Allah batada wani lpya
Her decision was based on nazarin data rinka yi ba acikin son zuciya da gaggawa ta yanke shi..
Inhar da ace nice naseer wallhy zan kyaleta hakanan itama taje ta huta Amma bazann taba in saketa ba,ai zataje din Kuma itama zataji abunda yaji aransa lokacin dayayi tunanin guduwa ya barsu acikin ukubu shine mafita.
Hanklinta na kwanciya zakiga ta dawo ,but ni banga lefinta ba kokadan
Every body derserve a break and refilled.
In dauriya yayi yawa sheidan yakan saurin batar da mutum ta hanyar rusa masa aikinsa da mugayen tunani har akaiga kayi asarar tulin hakuri da jajircewan da kayi,Is best dat she leave queitly gaskiya.👍🏻
[6/29, 10:22 PM] Zannura: *NAGA TA KAINA*

*NA SADNAF*🌸🌸

®️ *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_

*Free Novel*

*Page 35*

"Kana kallo Suka fita da engine baka hanasu ba yanzu ta Ina zamu ringa samun kudin da zamu kashe"?

"Toh Mai engine ta siyar da kayanta Mai shi yazo ya d'auka ta Ina Zan Hana Umma abinda ba nawa ba"
Chapter 4 · 0% Book details