Sashe 1
Naga Ta Kaina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
[6/27, 10:46 PM] Zannura: *NAGA TA KAINA*
*NA SADNAF*🌸🌸
®️ *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_
*Free Novel*
Hannuna har karkarwa yake wajen d'ago da jaririn Dan na tabbatar da Namijin ne.
Take na hau hawayen farinciki na Kara kwantar dashi a kirjina inata Godewa Allah da Wanan kyautar da yamin a cikin jaririn Nan ne kawai ban saka Rai da samun namiji ba Amma sauran duk saka Rai nake da maza ne sai gashi a lokacin da ban kawo ba na cire Rai da haihuwa Namiji Allah ya bani.
Kasa d'auke idona nayi daga kansa har Nurse din ta saka Mai Kaya bayan ta goge Mai jiki da man zaitun
Yanda taga Ina binsa da Ido Ina murmushi yasa tace halan ban taba haihuwa d'a namiji ba gyada Mata Kai nayi a lokacin da take sake mikomin shi na karbe shi da Sauri na tashi zaune na zuba Masa Ido ba Inda ya baro Naseer kamar an tsaga Kara Haskena kawai ya d'auko.
Sosai na ringa Jin kaunar jaririn a Raina inajin nurse din na Bari tayiwa Naseer albishir tayi waje da Sauri Dan tasan indai ta Gaya masa kila ya mata kyauta
A bakin kofa ta tada Naseer din kamar zai fado d'akin Ana bud'e kofa yyi Kan nurse din da Sauri.
Ita kuwa ta mik'a Masa hannu tana ya Bata goron albishir
Washe baki yayi daya ga alamar Naeema ta sauka lafiya addua ya hau yi Yana "Na Riga da nasan Mai ta Haifa Allah yayiwa rayuwarta albarka"
Murmushi nurse din tayi tana mamakin yanda daga Naeema har Naseer din suka cire Rai da haihuwar da namiji
"Sai dai Allah ya Masa albarka Dan namiji ta Haifa katoto"
Naseer Ido ya gwallo Yana me kikace.
Kafin ma ta bashi amsa ya fada d'akin da Sauri har Yana tuntub'e.
Daga yanda yaga Naeema na murmushi yasa ya Isa wajenta da Sauri tare da saka hannu ya karbi jaririn Bakinsa har kunne sai hamdala yake Yana kamkame jaririn a kirjinsa.
Sai albarka yake shiwa Naeema ji yake kamar baa Tab'a Masa haihuwa bama inama lokacin da yake da kudi Naeema ta haifi namiji da yaron ya Sha Gata.
Bakinsa ya kafa a kunnen jaririn ya Masa huduba ya d'ago ya kalli Naeema Yana "Allah ya raya Naseer sunana na saka mishi"
Murmushi na saki Ina Jin dadin sunan daya saka mishi nace "Allah yasa ya gaji halin Mai sunan ya bashi ilimin addini irin na Mai sunan insha Allahu addua kawai ce tsakanina da yarana Allah Kar ya jarrabceni da fushi dasu"
Na tsinci kaina da fad'a duk da kallon da Naseer kemin yasa na hadiye sauran maganar.
Karfe takwas na safe aka Sallame mu daga asibitin bayan Naseer ya biya kudin komai.
Hamdala kawai yake a Ransa da Allah yasa Naeema nada kudi da yau asirinsa ya tonu ta Ina zai samu wanan kudin da suka kashe a asibitin.
Naeema sai data saka ya siyi kayan shayi da sauran Abubuwan a zata bukata kamar yanda yake siya idan ta haihu shi kuwa sai dari dari yake baya San kashe kudin Wai Dan Kar ya kare.
Lokacin da muka Isa gida Naseer ne ya rungume jaririn a kirjinsa daya hannunsa d'auke da kayayakin mu Ni Kuma Ina biye dashi a baya Ina takawa a hankali kamar iska zai d'aukeni nakeji sabida rashin kwarin jiki banida burin daya wuce na kwanta sabida ciwon baya danake yi
Bakin Naseer a washe ya Shiga palon
Da Sallama Umma da Safiyya kawai muka samu a palon Umma ta hade Rai tana ta jijjiga k'afa Ina ganin Haka nasan wani rashin mutunci Umma zatayi.
Naseer kuwa tuni Naga ya nutsu duk da gabansa sai daya Fadi da ganin Umma Amma Haka ya nufi wajenta ya tsugunna Ya hau gaisheta.
Wani irin kallo ta Masa ta d'auke kanta batare da ta amsa ba
Shi kuwa ya Kara gyara Jaririn a hannunsa Yana "Umma Naeema fa ta haihu Kinga"
"Sai me dan ta haihu yau ta fara haihuwan?Mai abin murna a haihuwa Naeema da take cike.maka gida da tarin Mata"
"Umma wanan Namiji ne wanan Karin Allah ya azurtamu da Samun namiji"
Ina dab da Isa k'ofar karamin Palo Amma sabida Naga ya Umma zatayi idan taji Namiji na Haifa yasa na tsaya.
Mik'ewa tayi da Sauri ta lek'a fuskar jaririn da Naseer ya juyo dashi Sabida Umma ta ganshi sosai ta gaskata maganar da yake.
Ja da baya tayi tana "Kuma sai ka yarda wanan danka ne.
Sai ka yarda wanan Jininka ne?
Watanmu kusan hudu a gidanan tunda muka zo Maza suke sintiri a gidanan wayanda zasu Zo da safe daban wayanda zasu Zo da Rana daban Sabida Kai dakiki ne an asirceka idonka ya rufe shine zaka ringa murnar ta haifo maka namiji.
Kar idonka ya rufe ka kasa gane gaskiya har Ina Naeema zata samu kudin da zata gyara gidanan Bata tsaya iya Nan ba ta siyi engine biyu Kai Kaga irin kudin datake rik'ewa kuwa Amma dayake zuciyarka ta mace idonka ya rufe duk baka gani ba ka hau rawar kafar ta haifo ma namiji indai Jininka ne ai mace zata haifo iya wanann ma ya Isa yasa ka Gane Dan Nan ba naka bane"
Yanda nakejin zuciyata da jirin dake d'ibana sabida tsananin bakinciiki sheganta min da da Umma keyi da kazafin da take neman yimin yasa.na shige palon Dan Ina cigaba da tsayuwa zuciyata zata iya bugawa Ni Kam wane irin nauyin kiyaya Umma zata gwadamin Wanda Bata gwadamin ba ya isa Haka ai batare aka halliceni da Naseer ba tafiyar Naseer ban fasa numfashi da rayuwa ba Dan Haka barin rayuwar Naseer na huta bazai Hana shi rayuwa ba Haka Nima idan akwai abinda ke damuna Bai wuce yarana ba Dan Ni nasan matsawar na tafi dasu kamar inasan Naseer ya dawo rayuwata ne.
D'akina na Shiga na kwanta ganin Banga kayan makarantarsu Zahira da jakunnan makarantarsu ba yasa nasan sun tafi makaranta.
Hawaye kawai nake Ina tunanin hanyar da Zan bi wajen barin rayuwar Naseer na har abada.
Allah yasan Ina kaunarsa Amma ya zama Dole mu rabu idan kuwa ya zargeni sabida bashida kudi na rabu dashi baimin adalci ba Dan ko kanwarsa ake matsawa Haka ya Bata shawarar ta hakura da auren.
Ina jiyo Naseer na Mata kana Nan rantsuwa Akan yasan Halina ko shekara goma zaiyi Zan rik'e Masa amanar aurensa wlh Dan Nan NASA ne Dan Allah ta karbi jaririn taga yanda Suke kama.
Ita kuwa Umma dagewa kawai take Tana rantsuwar ba dansa bane Wai Ni Mata nake Haifowa inaji tana balai Yana Bata hakuri.
Inaga Safiyya ce ta saka Baki naji ya daka Mata wani uban tsawa daya saka jaririna razana ya saka kuka.
Naseer kuwa kukansa Bai sa ya bar wanke Safiyya.kamar zai ajiye jaririn ya rufeta da duka ba yayi ta cewa ta Kai shi bango wlh xai koreta daga gidansa Dan bazata Zo tana hura Masa wuta a gida ba shiyasan wani zubin ita ke zuga Umma.
Ita kuwa Umma cewa take "Kar ka wani wayance Ni zaka yiwa fada ba ita ba tunda Ni nake Maka magana"
Kukan Jaririn yasa Naseer bai ce wa Umma komai ba ya nufo d'akina Ransa a balain b'ace Yana shigowa d'akin.
Ya mikomin shi na karbe shi take kuwa yayi shiru na Ciro abincinsa na saka Masa a baki tare da bismillahi ya kuwa cafe da Sauri a fili nace "Allah ya rayaka Walid ya shiryaka bisa tafarkin musulunci"
Ameen Naseer yace can kasar murya idonsa ya kad'a yayi jawur ban nuna Masa naji Haushin abinda umma tamin a fuska ba Amma ya juyo ya hau bani hakuri Yana na taimaka masa mahaifiyarsa ce babu yanda zaiyi da ita Yana Nan Yana gayawa Allah.
Murmushi kawai nayi Dan daya bani hakuri da Kar ya bani hakuri na Riga da na yanke hukunci a raina.
Ce Masa nayi ba komai kar ya damu.
Sai a lokacin ya saki ajiyar zuciya masu markade da suka zo yasa ya mik'e Yana Bari ya markada musu.
Amma kafin Nan Bari ya saka Safiyya ta dafamin ruwan tea da Sauri na ce ba sai ya sakata ba ya Bari na Gama bashi Zan fito na Dora ruwan da kaina tunda Dama Ina bukatar ruwa Mai yawa sabida ma nayi wanka na wanke Walid.
Har zai Musa min Kuma ya fasa Yana bari ya fara doramin ruwan inyaso sai ya fara markaden.
Nima.fada kawai nayi bazan iya tashi ba sabida jirin danake ji.
A kitchen ya tarar da Safiyya itama ta juye musu ruwan zafi a jug ga kwai ta soya a faranti duk a kudin Naeema da suke Mata fin k'arfi su kwace.
Yanda Naseer ya hade Rai yasa ta fice daga kitchen din da Sauri.
Tana fita ya Dora ruwa a babban tukunya ya fito ya kunna engine ya fara markaden.
Yana cikin yi ma Isihu ya shigo ya fara markaden.
Shi kuwa Naseer ya koma.dakin ya d'auko ledar zanin da Naeema ta Bata ya zuba a katon baho dayake akwai Omo da dettol a bandaki ya zuba ya koma kitchen
Ganin ruwan yayi zafi sosai yasa ya cika flask ya Kai daki ya juya sauran a katon Bokiti.
Duk abinda yake Umma da Safiyya binsa kawai suke da kallo.
Umma kuwa kamar ta fashe Dan bakin cikin yanda Naseer yake neman Zama bawan Naeema
Shayi Mai kauri ya hadamin ni kuwa na fara sha
Ganin Yana k'ok'arin fita yasa nace Masa Dan Allah ya bawa Isihu kudi idan ya gama markaden ya siyo.min nama bakina ba dadi.
Zama yayi a gefena Yana "Naeema ba asan Raina Kika haihu banida ko sisi ba wlh bana Jin dadi Amma ba yanda zanyi Haka Allah ya hukunta Naeema na baki labarin ban zo gidanan da ko biyar ba Kar muzo muyita kashe kudin ya Kare kiyi maneji da Abunda Kika samu gaba idan Allah ya hore duk Zan Miki Abunda ban miki ba a haihuwar Nan"
*NA SADNAF*🌸🌸
®️ *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_
*Free Novel*
Hannuna har karkarwa yake wajen d'ago da jaririn Dan na tabbatar da Namijin ne.
Take na hau hawayen farinciki na Kara kwantar dashi a kirjina inata Godewa Allah da Wanan kyautar da yamin a cikin jaririn Nan ne kawai ban saka Rai da samun namiji ba Amma sauran duk saka Rai nake da maza ne sai gashi a lokacin da ban kawo ba na cire Rai da haihuwa Namiji Allah ya bani.
Kasa d'auke idona nayi daga kansa har Nurse din ta saka Mai Kaya bayan ta goge Mai jiki da man zaitun
Yanda taga Ina binsa da Ido Ina murmushi yasa tace halan ban taba haihuwa d'a namiji ba gyada Mata Kai nayi a lokacin da take sake mikomin shi na karbe shi da Sauri na tashi zaune na zuba Masa Ido ba Inda ya baro Naseer kamar an tsaga Kara Haskena kawai ya d'auko.
Sosai na ringa Jin kaunar jaririn a Raina inajin nurse din na Bari tayiwa Naseer albishir tayi waje da Sauri Dan tasan indai ta Gaya masa kila ya mata kyauta
A bakin kofa ta tada Naseer din kamar zai fado d'akin Ana bud'e kofa yyi Kan nurse din da Sauri.
Ita kuwa ta mik'a Masa hannu tana ya Bata goron albishir
Washe baki yayi daya ga alamar Naeema ta sauka lafiya addua ya hau yi Yana "Na Riga da nasan Mai ta Haifa Allah yayiwa rayuwarta albarka"
Murmushi nurse din tayi tana mamakin yanda daga Naeema har Naseer din suka cire Rai da haihuwar da namiji
"Sai dai Allah ya Masa albarka Dan namiji ta Haifa katoto"
Naseer Ido ya gwallo Yana me kikace.
Kafin ma ta bashi amsa ya fada d'akin da Sauri har Yana tuntub'e.
Daga yanda yaga Naeema na murmushi yasa ya Isa wajenta da Sauri tare da saka hannu ya karbi jaririn Bakinsa har kunne sai hamdala yake Yana kamkame jaririn a kirjinsa.
Sai albarka yake shiwa Naeema ji yake kamar baa Tab'a Masa haihuwa bama inama lokacin da yake da kudi Naeema ta haifi namiji da yaron ya Sha Gata.
Bakinsa ya kafa a kunnen jaririn ya Masa huduba ya d'ago ya kalli Naeema Yana "Allah ya raya Naseer sunana na saka mishi"
Murmushi na saki Ina Jin dadin sunan daya saka mishi nace "Allah yasa ya gaji halin Mai sunan ya bashi ilimin addini irin na Mai sunan insha Allahu addua kawai ce tsakanina da yarana Allah Kar ya jarrabceni da fushi dasu"
Na tsinci kaina da fad'a duk da kallon da Naseer kemin yasa na hadiye sauran maganar.
Karfe takwas na safe aka Sallame mu daga asibitin bayan Naseer ya biya kudin komai.
Hamdala kawai yake a Ransa da Allah yasa Naeema nada kudi da yau asirinsa ya tonu ta Ina zai samu wanan kudin da suka kashe a asibitin.
Naeema sai data saka ya siyi kayan shayi da sauran Abubuwan a zata bukata kamar yanda yake siya idan ta haihu shi kuwa sai dari dari yake baya San kashe kudin Wai Dan Kar ya kare.
Lokacin da muka Isa gida Naseer ne ya rungume jaririn a kirjinsa daya hannunsa d'auke da kayayakin mu Ni Kuma Ina biye dashi a baya Ina takawa a hankali kamar iska zai d'aukeni nakeji sabida rashin kwarin jiki banida burin daya wuce na kwanta sabida ciwon baya danake yi
Bakin Naseer a washe ya Shiga palon
Da Sallama Umma da Safiyya kawai muka samu a palon Umma ta hade Rai tana ta jijjiga k'afa Ina ganin Haka nasan wani rashin mutunci Umma zatayi.
Naseer kuwa tuni Naga ya nutsu duk da gabansa sai daya Fadi da ganin Umma Amma Haka ya nufi wajenta ya tsugunna Ya hau gaisheta.
Wani irin kallo ta Masa ta d'auke kanta batare da ta amsa ba
Shi kuwa ya Kara gyara Jaririn a hannunsa Yana "Umma Naeema fa ta haihu Kinga"
"Sai me dan ta haihu yau ta fara haihuwan?Mai abin murna a haihuwa Naeema da take cike.maka gida da tarin Mata"
"Umma wanan Namiji ne wanan Karin Allah ya azurtamu da Samun namiji"
Ina dab da Isa k'ofar karamin Palo Amma sabida Naga ya Umma zatayi idan taji Namiji na Haifa yasa na tsaya.
Mik'ewa tayi da Sauri ta lek'a fuskar jaririn da Naseer ya juyo dashi Sabida Umma ta ganshi sosai ta gaskata maganar da yake.
Ja da baya tayi tana "Kuma sai ka yarda wanan danka ne.
Sai ka yarda wanan Jininka ne?
Watanmu kusan hudu a gidanan tunda muka zo Maza suke sintiri a gidanan wayanda zasu Zo da safe daban wayanda zasu Zo da Rana daban Sabida Kai dakiki ne an asirceka idonka ya rufe shine zaka ringa murnar ta haifo maka namiji.
Kar idonka ya rufe ka kasa gane gaskiya har Ina Naeema zata samu kudin da zata gyara gidanan Bata tsaya iya Nan ba ta siyi engine biyu Kai Kaga irin kudin datake rik'ewa kuwa Amma dayake zuciyarka ta mace idonka ya rufe duk baka gani ba ka hau rawar kafar ta haifo ma namiji indai Jininka ne ai mace zata haifo iya wanann ma ya Isa yasa ka Gane Dan Nan ba naka bane"
Yanda nakejin zuciyata da jirin dake d'ibana sabida tsananin bakinciiki sheganta min da da Umma keyi da kazafin da take neman yimin yasa.na shige palon Dan Ina cigaba da tsayuwa zuciyata zata iya bugawa Ni Kam wane irin nauyin kiyaya Umma zata gwadamin Wanda Bata gwadamin ba ya isa Haka ai batare aka halliceni da Naseer ba tafiyar Naseer ban fasa numfashi da rayuwa ba Dan Haka barin rayuwar Naseer na huta bazai Hana shi rayuwa ba Haka Nima idan akwai abinda ke damuna Bai wuce yarana ba Dan Ni nasan matsawar na tafi dasu kamar inasan Naseer ya dawo rayuwata ne.
D'akina na Shiga na kwanta ganin Banga kayan makarantarsu Zahira da jakunnan makarantarsu ba yasa nasan sun tafi makaranta.
Hawaye kawai nake Ina tunanin hanyar da Zan bi wajen barin rayuwar Naseer na har abada.
Allah yasan Ina kaunarsa Amma ya zama Dole mu rabu idan kuwa ya zargeni sabida bashida kudi na rabu dashi baimin adalci ba Dan ko kanwarsa ake matsawa Haka ya Bata shawarar ta hakura da auren.
Ina jiyo Naseer na Mata kana Nan rantsuwa Akan yasan Halina ko shekara goma zaiyi Zan rik'e Masa amanar aurensa wlh Dan Nan NASA ne Dan Allah ta karbi jaririn taga yanda Suke kama.
Ita kuwa Umma dagewa kawai take Tana rantsuwar ba dansa bane Wai Ni Mata nake Haifowa inaji tana balai Yana Bata hakuri.
Inaga Safiyya ce ta saka Baki naji ya daka Mata wani uban tsawa daya saka jaririna razana ya saka kuka.
Naseer kuwa kukansa Bai sa ya bar wanke Safiyya.kamar zai ajiye jaririn ya rufeta da duka ba yayi ta cewa ta Kai shi bango wlh xai koreta daga gidansa Dan bazata Zo tana hura Masa wuta a gida ba shiyasan wani zubin ita ke zuga Umma.
Ita kuwa Umma cewa take "Kar ka wani wayance Ni zaka yiwa fada ba ita ba tunda Ni nake Maka magana"
Kukan Jaririn yasa Naseer bai ce wa Umma komai ba ya nufo d'akina Ransa a balain b'ace Yana shigowa d'akin.
Ya mikomin shi na karbe shi take kuwa yayi shiru na Ciro abincinsa na saka Masa a baki tare da bismillahi ya kuwa cafe da Sauri a fili nace "Allah ya rayaka Walid ya shiryaka bisa tafarkin musulunci"
Ameen Naseer yace can kasar murya idonsa ya kad'a yayi jawur ban nuna Masa naji Haushin abinda umma tamin a fuska ba Amma ya juyo ya hau bani hakuri Yana na taimaka masa mahaifiyarsa ce babu yanda zaiyi da ita Yana Nan Yana gayawa Allah.
Murmushi kawai nayi Dan daya bani hakuri da Kar ya bani hakuri na Riga da na yanke hukunci a raina.
Ce Masa nayi ba komai kar ya damu.
Sai a lokacin ya saki ajiyar zuciya masu markade da suka zo yasa ya mik'e Yana Bari ya markada musu.
Amma kafin Nan Bari ya saka Safiyya ta dafamin ruwan tea da Sauri na ce ba sai ya sakata ba ya Bari na Gama bashi Zan fito na Dora ruwan da kaina tunda Dama Ina bukatar ruwa Mai yawa sabida ma nayi wanka na wanke Walid.
Har zai Musa min Kuma ya fasa Yana bari ya fara doramin ruwan inyaso sai ya fara markaden.
Nima.fada kawai nayi bazan iya tashi ba sabida jirin danake ji.
A kitchen ya tarar da Safiyya itama ta juye musu ruwan zafi a jug ga kwai ta soya a faranti duk a kudin Naeema da suke Mata fin k'arfi su kwace.
Yanda Naseer ya hade Rai yasa ta fice daga kitchen din da Sauri.
Tana fita ya Dora ruwa a babban tukunya ya fito ya kunna engine ya fara markaden.
Yana cikin yi ma Isihu ya shigo ya fara markaden.
Shi kuwa Naseer ya koma.dakin ya d'auko ledar zanin da Naeema ta Bata ya zuba a katon baho dayake akwai Omo da dettol a bandaki ya zuba ya koma kitchen
Ganin ruwan yayi zafi sosai yasa ya cika flask ya Kai daki ya juya sauran a katon Bokiti.
Duk abinda yake Umma da Safiyya binsa kawai suke da kallo.
Umma kuwa kamar ta fashe Dan bakin cikin yanda Naseer yake neman Zama bawan Naeema
Shayi Mai kauri ya hadamin ni kuwa na fara sha
Ganin Yana k'ok'arin fita yasa nace Masa Dan Allah ya bawa Isihu kudi idan ya gama markaden ya siyo.min nama bakina ba dadi.
Zama yayi a gefena Yana "Naeema ba asan Raina Kika haihu banida ko sisi ba wlh bana Jin dadi Amma ba yanda zanyi Haka Allah ya hukunta Naeema na baki labarin ban zo gidanan da ko biyar ba Kar muzo muyita kashe kudin ya Kare kiyi maneji da Abunda Kika samu gaba idan Allah ya hore duk Zan Miki Abunda ban miki ba a haihuwar Nan"