Sashe 35
Naga Ta Kaina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wanda Sam Naseer Bai Gane zuwan da ake ba har sai da ciniki ya kankama
Naeema ke Gaya masa matakin data dauka na siyar da gidan Dan ta bar unguwar.
Naseer sosai yaji zuciyarsa ta sosu da hukunci da ta yanke batare da ta shawarce shi ba sosai yaga Dan tana takamar gidanta ne hakane yasa tayi Masa Haka Amma kasan zuciyarsa Kuma sai yake ganin Dan tsira da lafiyar yayansu yasa kila takeso su bar unguwar
shima kansa hakan yaso yayi dan so yake ko haya ne ya Kama musu acan Abuja su koma can da Zama inyaso ko aike ne ya ringa yiwa Hajara Amma tunda ma Naeema ta Riga da ta yanke siyar da gidan shikenan
Dashi akayi cinikin gidan da ba laifi an siye shi da daraja da saka hannun Naeema aka siyar da gidan
Masu siyen Kuma suka bada kudi tare da notice din wata guda.
Kayan shagon Kuma tayi niyyar siyarwa wani Mai shago dake can bakin titi da har Naeema ta Masa magana.
Da injin markadenta kawai zata tafi
Sai da Naseer ya tambayeta Inda take so su koma ta ce Masa garinsu zasu koma gabadyaa yanda su Hajara ma bazasu San Inda suke ba sosai Naeema ta shirya Yana Mata gardama tace ya Bata takarda sakinta Dan har ga Allah ta gaji sosai
Naseer kuwa take takenta ya gani ya hau lallaminta akan ba sai ta Kai ga barin Kano ba ta nemi wani unguwar ko Dan makaranta yaran nasu
Dak'yar da sidin goshi ya shawo Kan Naeema Dan tuburewa tayi bazata zauna a kano ba duk Abubuwan dake ciciyar ta a zuciya ta hau amayar dashi har da cewa ita dai ta gaji da aurensa indai wani Abu ya Samu yaranta bazata yafe ba Naseer Haka ya Shanye duk maganganun data ringa kwaba Masa har ya samu kanta
Abinka da tsakanin Mata da miji tuni dai ya shawo kanta ya kwantar Mata da hankali Inda ya Kuma Bata shawarar Inda ya kamata ta samo.karamin gidan unguwa ne nesa sosai da Inda su Hajara suke.
Hakane yasa Naeema ta sakar wa Naseer ragamar komai Inda ya nemo.mata karamin gidan Kamar dai wancan data siyar sai dai wanan Din ya Dan fi girma kawai matsalar ba shago a gaban gidan
Sai da Naeema taje taga gidan taga komai yayi suka biya kudin gidann
Cikin sati biyu suka dawo kawo dake unguwar hotoro Bayan anyiwa su Nadeeya transfer zuwa wani makarantar
Zahira kuwa boarding Naseer ya dage zata tafi a fadarsa.
Hakane kawai zai saka masu sintirin zuwa nemanta su daga kafa Zahira Kuma zata maida hankali tayi karatu sosai tunda yanzu zata tafi ss1
Nadeeya Kuma ta tafi jss.2
Dayake da Yan canji a hannun Naseer shi yayi cuku cukun sabon makarantar dasu Nadeeya suka koma dake unguwar da suka koma.
Zahira kuma.aka hau Mata siyayyan boarding Dan itama an Mata komai.ta fanin registration.
Har ga Allah ba a San Raina Zahira zata tafi boarding ba Dan dai Naseer yamin fin k'arfi ne kawai a matsayinsa na Mahaifin zahiran a rayuwata banasan abinda zai nesanta Ni da yarana nafiso ko yaya ne na ringa ganinsu a gabana har ya fara shirye shiryen Kai ta jikina a sanyaye yake ita kuwa zahira murna take sosai tana doki data ga yanda babanta ke mata siyyaya
Nidai addua kawai nake akan Allah ya karemin ita Dan har yanzu gani nake su Umma zasu iya jefo min wani masifar amma.ina gayawa sarkin sarakuna duk gudun da zanyi nasan sai dai idan Umma basu so cutar damu ba kasan zuciyata Kuma sai nake ganin zuwan Zahira boarding zai.nisanta ta daga sharrinsu umman.
Hakane yasa na kwantar da hankalina nayiwa zahira komai na jawota jikina na Bata shawarwari yanda zata kame.kanta da dagiya da addua
A Haka nida Naseer muka Kai Zahira makaranta yata ta rungumeni muna kukan rabuwa dak'yar Naseer yaja hannuna Muka tafi
Kamar Mara lafiya dai na dawo sai Dana fi sati kafin na fara Dan sabawa da rashin zahiran
A Haka na maida hankali na fara tunanin Sana'ar da Zan Kama Kuma bayan.markaden Dan da alama unguwar akwai.masu markade.da.yawa ba shago a k'ofar Gidan ballantana nace Zan zuba provision kamar wancan unguwar da muka baro
A Haka dai na yanke siyar da Zobo kafin na samu babba Sana'ar da zan ringa yi tunda kudin Sana'ar tawa suna ajiye
Ba laifi kuma Ina Dan cinikin zobon
Naseer wata biyu ya min ya koma Abujan.
Ni kuwa na cigaba da kula da yarana sau biyu Ina zuwa ganin Zahira ba laifi hankalina ya kwanta da yanda naganta kawarta ma da kusan dabiarsu daya sunanta jameela sosai na yaba da hankalinta hakane yasa na Kara samun kwanciyar hankali.
A Haka rayuwar ta ringa tafar Mana ban taba sakin jikina ba kullum cikin addua nake Dan nasan duk da anyiwa su Umma gargadi nasan halin su kila idan sun ga an kwana biyu zasu iya waiwayomu da sharri kullum cikin sadaka nake Dan nasan sadaka maganin masifa ce
A Haka su Zahira sukayi first term dinsu a ss1 sukayi hutu suka dawo
Fes Zahira ta Kara Yi kyaunta ya Kara fitowa tabarkallah Masha Allah Dan acan ma Mallamai santa sukeyi.
Hakane yasa na yanke a Raina indai ta Gama din mu aurar da ita kawai inyaso ta cigaba a gidan mijinta
Naseer shima a daidai lokacin da sukayi hutu ya dawo
Cikin farincikin kudin daya samo inda yake cemin fili xai siya da kudin sosai na Taya shi murna Dan Kamar Wanda Bai taba gidan kansa ba yake murna da filin da yake San siya
Gaba da gidana wajen bakin titi ya siyi katon filin a ranar ko baccin kirki baiyi ba sabida murna.
Ahaka ya Mana sati biyu ya koma.batare da waiwaiyar umma ba
A Haka aka Gama hutu Zahira na rakata makaranta
Sati.uku da komawarta na fara mugayen mafarkai akan Zahira
Daya dagamin hankali na hau sadaka Ina Addua Haka kawai naji Kamar wani Abu ne zai sameta daga yanayin danake.ganinta a mafarkina hakane yasa naji Sam na kasa samun kwanciya hankali na fara shirin zuwa dubo ta a ranar Dana shirya da sassafe Dan na dubota a ranar da bazan taba mantawa ba a rayuwata Mallamai biyu ne maza da mallama Mace daya sai kawar Zahira jameela da wata da suka ruk'o zahira Kamar matacciya suka shigomin da ita Suka shimfida min ita a tsakiyar gidana.
Juyawar da kaina keyi da kirjina da nakeji kamar zuciyata ce zata fito yasa na kasa motsi na daskare a tsaye
Kwantar da Zahira da akayi yasa na rik'e zuciyata tare da kallon zahiran.
Abinda na gani ne yasa jiri d'ibana na zub'e a gefen zahiran.......
Kuyimin.hakuri abubuwa ne Suka Sha kaina sai Sunday Zan dawo daidai ayi maneji pls.
A next episode insha Allahu Zan k'ok'arin Yi dayawa Dan muyi mu Gama ngd
[8/1, 5:30 PM] Zannura: *NAGA TA KAINA*
*NA SADNAF*🌸🌸
®️ *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_
*Free Novel*
*Page 53*
Na saki ihu tare da dagota Ina "Mai ya samu 'yata Haka Mai ya sameta waye ya kwakulo Mata idonta waje Haka Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun"
(Nafeesa sai dai na takaita Miki wuyan da Zahira ta Sha a cikin irin kaddarar data budemin daga auren Naseer wahalar da Zahira ta Sha yafi komai bani wuya tunda Nima sai Dana Zama tamkar tab'abb'iya wuyan data Sha shima labarine Mai zaman kansa sai dai na takaita Amma kyakyawan zuciya irin nata cewa take ta yafe musu abinda Suka Mata ko yanzu da Zan baki labarin wuyan da yata ta Sha ni kadai nasan Mai nakeji a Zuciyata ko nida Zahira mun yafe Sai Allah ya Mana sakayya"
Ta fashe da kuka labarin da baa bani ba kenan a ranar sai washegari)
Badan nasan Zahira 'yata bace bazan yarda ita Suka kawomin ba Dan gabadaya hallitar Zahira ta canja cikin sati uku kawai da Zahira tayi da komawa makaranta ta dawo kamar kwarangwal idonta ya firfito waje gabadaya wuyanta kuwa ya wani irin kumburo waje kallo daya zaka Mata ka d'auke idonka daga kanta sabida Dole ka tsorata da yanda ta dawo
Ihun dana cigaba da yi Ina tattab'a zahiran da ba magana takemin ba illa manyan idon da kamar Kara Mata su akayi kawai take kallona hawaye na zararo mata
Wuyanta daya kumburo kuwa sai motsi yake kamar ta hadiyi wani Abu kanta da jikinta kuwa har wani hucci yake sabida tsananin zafi
Cikin azabar kuka yata rungume dani a kirjina na kalli mallaman da suka kawomin ita Ina "Ku min bayani Mai ya samu 'yata ta dawo Haka Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun na Shiga uku na lalace jameela Mai ya samu kawarki Haka ki gayamin jameela"?
Nace Ina Kara tab'a wuyan Zahira daya ke numfashi shi kadai
Zahira kuwa har lokacin Bata cemin A ba sai kallona take da idonta tana zubar hawaye
Daya mallamin ne yayi karfin halin magana Dan dukansu kuka sukeyi jikinsu a sanyaye suna kallon Zahira da Bata da bambanci da mataciya sai numfashi kawai da takeyi
"Washegarin da suka koma hutu daddare wajen karfe Tara Zahira ta tafi bandaki ita da jameela Wai zasuyi fitsari
Jameela ce ta fara Shiga ta fito kafin Zahira ta Shiga
Zahira na Shiga ba dadewa sai ihunta jameela taji da ba iya jameelan ce taji ihun zahiran ba har b'angaren Mallamai munji wanan ihun hakane yasa duk muka bazama mukayi b'angaren daliban sai dai muna zuwa muka ganta shame shame a kwance tana wani irin jijjiga hakane yasa mukayi tunanin ko Aljannu ne suka shafeta a band'akin.
Da addua muka fito da ita daga band'akin hankalinmu a balain tashe mun Saba ganin cases na dalibai masu Aljannu sai dai na zahiran sai ya bamu tsoro Dan bayan mun fito da ita daga band'akin wani irin zafi jikinta ya d'auka Kamar garwashin wuta idonta ya Zama kamar jini jikinta kuwa Banda rawa ba abinda keyi
Mallamin Dake karantar dasu ta fanin islamiyya muka Kira Dan indai case ya taso irin Haka shi yake yiwa dalibai rukiyya sai dai duk Inda ya Kai da rukiyya ba alamar sauki kwana mukayi a kanta sai gabanin asuba Muka ga ta daina girgiza ta rufe idonta.
Naeema ke Gaya masa matakin data dauka na siyar da gidan Dan ta bar unguwar.
Naseer sosai yaji zuciyarsa ta sosu da hukunci da ta yanke batare da ta shawarce shi ba sosai yaga Dan tana takamar gidanta ne hakane yasa tayi Masa Haka Amma kasan zuciyarsa Kuma sai yake ganin Dan tsira da lafiyar yayansu yasa kila takeso su bar unguwar
shima kansa hakan yaso yayi dan so yake ko haya ne ya Kama musu acan Abuja su koma can da Zama inyaso ko aike ne ya ringa yiwa Hajara Amma tunda ma Naeema ta Riga da ta yanke siyar da gidan shikenan
Dashi akayi cinikin gidan da ba laifi an siye shi da daraja da saka hannun Naeema aka siyar da gidan
Masu siyen Kuma suka bada kudi tare da notice din wata guda.
Kayan shagon Kuma tayi niyyar siyarwa wani Mai shago dake can bakin titi da har Naeema ta Masa magana.
Da injin markadenta kawai zata tafi
Sai da Naseer ya tambayeta Inda take so su koma ta ce Masa garinsu zasu koma gabadyaa yanda su Hajara ma bazasu San Inda suke ba sosai Naeema ta shirya Yana Mata gardama tace ya Bata takarda sakinta Dan har ga Allah ta gaji sosai
Naseer kuwa take takenta ya gani ya hau lallaminta akan ba sai ta Kai ga barin Kano ba ta nemi wani unguwar ko Dan makaranta yaran nasu
Dak'yar da sidin goshi ya shawo Kan Naeema Dan tuburewa tayi bazata zauna a kano ba duk Abubuwan dake ciciyar ta a zuciya ta hau amayar dashi har da cewa ita dai ta gaji da aurensa indai wani Abu ya Samu yaranta bazata yafe ba Naseer Haka ya Shanye duk maganganun data ringa kwaba Masa har ya samu kanta
Abinka da tsakanin Mata da miji tuni dai ya shawo kanta ya kwantar Mata da hankali Inda ya Kuma Bata shawarar Inda ya kamata ta samo.karamin gidan unguwa ne nesa sosai da Inda su Hajara suke.
Hakane yasa Naeema ta sakar wa Naseer ragamar komai Inda ya nemo.mata karamin gidan Kamar dai wancan data siyar sai dai wanan Din ya Dan fi girma kawai matsalar ba shago a gaban gidan
Sai da Naeema taje taga gidan taga komai yayi suka biya kudin gidann
Cikin sati biyu suka dawo kawo dake unguwar hotoro Bayan anyiwa su Nadeeya transfer zuwa wani makarantar
Zahira kuwa boarding Naseer ya dage zata tafi a fadarsa.
Hakane kawai zai saka masu sintirin zuwa nemanta su daga kafa Zahira Kuma zata maida hankali tayi karatu sosai tunda yanzu zata tafi ss1
Nadeeya Kuma ta tafi jss.2
Dayake da Yan canji a hannun Naseer shi yayi cuku cukun sabon makarantar dasu Nadeeya suka koma dake unguwar da suka koma.
Zahira kuma.aka hau Mata siyayyan boarding Dan itama an Mata komai.ta fanin registration.
Har ga Allah ba a San Raina Zahira zata tafi boarding ba Dan dai Naseer yamin fin k'arfi ne kawai a matsayinsa na Mahaifin zahiran a rayuwata banasan abinda zai nesanta Ni da yarana nafiso ko yaya ne na ringa ganinsu a gabana har ya fara shirye shiryen Kai ta jikina a sanyaye yake ita kuwa zahira murna take sosai tana doki data ga yanda babanta ke mata siyyaya
Nidai addua kawai nake akan Allah ya karemin ita Dan har yanzu gani nake su Umma zasu iya jefo min wani masifar amma.ina gayawa sarkin sarakuna duk gudun da zanyi nasan sai dai idan Umma basu so cutar damu ba kasan zuciyata Kuma sai nake ganin zuwan Zahira boarding zai.nisanta ta daga sharrinsu umman.
Hakane yasa na kwantar da hankalina nayiwa zahira komai na jawota jikina na Bata shawarwari yanda zata kame.kanta da dagiya da addua
A Haka nida Naseer muka Kai Zahira makaranta yata ta rungumeni muna kukan rabuwa dak'yar Naseer yaja hannuna Muka tafi
Kamar Mara lafiya dai na dawo sai Dana fi sati kafin na fara Dan sabawa da rashin zahiran
A Haka na maida hankali na fara tunanin Sana'ar da Zan Kama Kuma bayan.markaden Dan da alama unguwar akwai.masu markade.da.yawa ba shago a k'ofar Gidan ballantana nace Zan zuba provision kamar wancan unguwar da muka baro
A Haka dai na yanke siyar da Zobo kafin na samu babba Sana'ar da zan ringa yi tunda kudin Sana'ar tawa suna ajiye
Ba laifi kuma Ina Dan cinikin zobon
Naseer wata biyu ya min ya koma Abujan.
Ni kuwa na cigaba da kula da yarana sau biyu Ina zuwa ganin Zahira ba laifi hankalina ya kwanta da yanda naganta kawarta ma da kusan dabiarsu daya sunanta jameela sosai na yaba da hankalinta hakane yasa na Kara samun kwanciyar hankali.
A Haka rayuwar ta ringa tafar Mana ban taba sakin jikina ba kullum cikin addua nake Dan nasan duk da anyiwa su Umma gargadi nasan halin su kila idan sun ga an kwana biyu zasu iya waiwayomu da sharri kullum cikin sadaka nake Dan nasan sadaka maganin masifa ce
A Haka su Zahira sukayi first term dinsu a ss1 sukayi hutu suka dawo
Fes Zahira ta Kara Yi kyaunta ya Kara fitowa tabarkallah Masha Allah Dan acan ma Mallamai santa sukeyi.
Hakane yasa na yanke a Raina indai ta Gama din mu aurar da ita kawai inyaso ta cigaba a gidan mijinta
Naseer shima a daidai lokacin da sukayi hutu ya dawo
Cikin farincikin kudin daya samo inda yake cemin fili xai siya da kudin sosai na Taya shi murna Dan Kamar Wanda Bai taba gidan kansa ba yake murna da filin da yake San siya
Gaba da gidana wajen bakin titi ya siyi katon filin a ranar ko baccin kirki baiyi ba sabida murna.
Ahaka ya Mana sati biyu ya koma.batare da waiwaiyar umma ba
A Haka aka Gama hutu Zahira na rakata makaranta
Sati.uku da komawarta na fara mugayen mafarkai akan Zahira
Daya dagamin hankali na hau sadaka Ina Addua Haka kawai naji Kamar wani Abu ne zai sameta daga yanayin danake.ganinta a mafarkina hakane yasa naji Sam na kasa samun kwanciya hankali na fara shirin zuwa dubo ta a ranar Dana shirya da sassafe Dan na dubota a ranar da bazan taba mantawa ba a rayuwata Mallamai biyu ne maza da mallama Mace daya sai kawar Zahira jameela da wata da suka ruk'o zahira Kamar matacciya suka shigomin da ita Suka shimfida min ita a tsakiyar gidana.
Juyawar da kaina keyi da kirjina da nakeji kamar zuciyata ce zata fito yasa na kasa motsi na daskare a tsaye
Kwantar da Zahira da akayi yasa na rik'e zuciyata tare da kallon zahiran.
Abinda na gani ne yasa jiri d'ibana na zub'e a gefen zahiran.......
Kuyimin.hakuri abubuwa ne Suka Sha kaina sai Sunday Zan dawo daidai ayi maneji pls.
A next episode insha Allahu Zan k'ok'arin Yi dayawa Dan muyi mu Gama ngd
[8/1, 5:30 PM] Zannura: *NAGA TA KAINA*
*NA SADNAF*🌸🌸
®️ *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_
*Free Novel*
*Page 53*
Na saki ihu tare da dagota Ina "Mai ya samu 'yata Haka Mai ya sameta waye ya kwakulo Mata idonta waje Haka Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun"
(Nafeesa sai dai na takaita Miki wuyan da Zahira ta Sha a cikin irin kaddarar data budemin daga auren Naseer wahalar da Zahira ta Sha yafi komai bani wuya tunda Nima sai Dana Zama tamkar tab'abb'iya wuyan data Sha shima labarine Mai zaman kansa sai dai na takaita Amma kyakyawan zuciya irin nata cewa take ta yafe musu abinda Suka Mata ko yanzu da Zan baki labarin wuyan da yata ta Sha ni kadai nasan Mai nakeji a Zuciyata ko nida Zahira mun yafe Sai Allah ya Mana sakayya"
Ta fashe da kuka labarin da baa bani ba kenan a ranar sai washegari)
Badan nasan Zahira 'yata bace bazan yarda ita Suka kawomin ba Dan gabadaya hallitar Zahira ta canja cikin sati uku kawai da Zahira tayi da komawa makaranta ta dawo kamar kwarangwal idonta ya firfito waje gabadaya wuyanta kuwa ya wani irin kumburo waje kallo daya zaka Mata ka d'auke idonka daga kanta sabida Dole ka tsorata da yanda ta dawo
Ihun dana cigaba da yi Ina tattab'a zahiran da ba magana takemin ba illa manyan idon da kamar Kara Mata su akayi kawai take kallona hawaye na zararo mata
Wuyanta daya kumburo kuwa sai motsi yake kamar ta hadiyi wani Abu kanta da jikinta kuwa har wani hucci yake sabida tsananin zafi
Cikin azabar kuka yata rungume dani a kirjina na kalli mallaman da suka kawomin ita Ina "Ku min bayani Mai ya samu 'yata ta dawo Haka Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun na Shiga uku na lalace jameela Mai ya samu kawarki Haka ki gayamin jameela"?
Nace Ina Kara tab'a wuyan Zahira daya ke numfashi shi kadai
Zahira kuwa har lokacin Bata cemin A ba sai kallona take da idonta tana zubar hawaye
Daya mallamin ne yayi karfin halin magana Dan dukansu kuka sukeyi jikinsu a sanyaye suna kallon Zahira da Bata da bambanci da mataciya sai numfashi kawai da takeyi
"Washegarin da suka koma hutu daddare wajen karfe Tara Zahira ta tafi bandaki ita da jameela Wai zasuyi fitsari
Jameela ce ta fara Shiga ta fito kafin Zahira ta Shiga
Zahira na Shiga ba dadewa sai ihunta jameela taji da ba iya jameelan ce taji ihun zahiran ba har b'angaren Mallamai munji wanan ihun hakane yasa duk muka bazama mukayi b'angaren daliban sai dai muna zuwa muka ganta shame shame a kwance tana wani irin jijjiga hakane yasa mukayi tunanin ko Aljannu ne suka shafeta a band'akin.
Da addua muka fito da ita daga band'akin hankalinmu a balain tashe mun Saba ganin cases na dalibai masu Aljannu sai dai na zahiran sai ya bamu tsoro Dan bayan mun fito da ita daga band'akin wani irin zafi jikinta ya d'auka Kamar garwashin wuta idonta ya Zama kamar jini jikinta kuwa Banda rawa ba abinda keyi
Mallamin Dake karantar dasu ta fanin islamiyya muka Kira Dan indai case ya taso irin Haka shi yake yiwa dalibai rukiyya sai dai duk Inda ya Kai da rukiyya ba alamar sauki kwana mukayi a kanta sai gabanin asuba Muka ga ta daina girgiza ta rufe idonta.