← Book details Naga Ta Kaina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 37 OF 62

Sashe 37

Naga Ta Kaina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sai dai kafin gari ya wayewa na Gane Kamar kwakwalwar Zahira ta tab'u Dan sau biyu Tana kashin amadadin taje bandaki na biyun a kitchen tamin na ukun Kuma a daya dakin da yarana suke kwana tana ta Abu Haka kamar mage tana kalle kalle abinan ya dagamin hankali daya saka ni kuka har garin Allah ya waye da asussuba na bazama neman Mai taimakamin Dan Kamar Mallam bazai iya da.larurar Zahira ba

Bansan k'afata ba takalmi ba Ina tafe hannuna Dora akaina Ina kuka

Ko ni bansan Ina na nufa ba sai danayi Karo da wata makociyarmu dake can kasan layinmu na dawo hankalina

Rikeni tayi da hannu biyu tana "Lafiya kuwa mmn Nadeeya"?

A sabon unguwar.mu da Sunan Nadeeya ake kirana sabida yanda take da farin jinin mutane sosai

Zubewa nayi a kasa na rik'e kafar matar da ta kasance bafulatana ana ce Mata yaddiko tunda Muka zo unguwa na lura tana da balain kirki ba laifi Dan tasan hakkin makotaka

"Ki taimakamin yaddiko yata zata mutu yata ta samu tab'in hankali"

"Subhanallahi Mai kike cewa Haka Mmn Nadeeya

Ta dagoni Ni kuwa na ja hannunta na cigaba da sheshek'ar kuka Ina bukatar Mai taimakamin Ina bukatar agaji Ina bukatar taimakon jamaa Dan ji nake kamar nayita kwalla ihu yarana ma zagaye suke da Zahira na fito neman taimako bansan Mai yasa nake Jan hannun.yaddiko.dan.tazo taga halin da 'yata take ciki ba kawai Ina bukatar taimakone

Har d'akina na Shiga da ita a madadin Naga Zahira akan gado Kamar yanda na barta acan Gefen sip Dina naganta Tana kashin kannenta sun zagayeta suna kallonta Waleed ne kawai a waje sabida tsoronta da suke ji

Sai wuwurga Ido Zahira keyi Kamar dai mage

Zubewa nayi a kasa na Nuno zahiran da hannu Ina "Yadiko Kinga yanda yata ta dawo Kinga yanda aka dawomin da ita yadikko Kan yata ya tab'u kinga Inda take Kashi ki taimakamin yadikko idan akwai Wanda Kika sani na Kai Zahira wajensa ya Mata addua yaddiko ki taimakamin bansan kowa ba babansu Baya Nan Yana Abuja ba ta hanyar da Zan same shi na sanar Masa halin da muke ciki"

Kuka nake sosai

Yadiko ma Ina gani ta zub'e a kasa sabida tashin hankalin ganin yanda Zahira ta dawo Dan ta San Zahira sosai sosai take Santa sabida kyaunta har tana yiwa Dan autansu shaawarta Dan ya Aureta idan ta Gama makaranta

Cikin tashin hankali tacemin "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun mmn Nadeeya akwai Wanda nasani zai iya taimaka Miki Bari na Kira mota mu tafi Amma fa wani kauye ne can gaba da jigawa Nima akwai kanwata datayi fama da Aljannu sai shi ya iya cire Mata su ko baa fada ba Zahira Aljannu ne a jikinta Kinga yanda ta dawo fa Ina zuwa yanzu nan kina da jan miski"?

Girgiza mata Kai nayi da Sauri

Tayi waje Ni Kuma na nufi wajen Zahiran na dagata nayi bandaki da ita na wanke Mata jikinta Nadeeya ta kwashe kashin ta goge

Duk Kayanta sun Mata yawa yawo take a ciki daidai da kayan Raheema da take karamarsu ya Mata yawa sai a Haka na saka Mata pant kuwa Bai zai saku ba Dan ba kugun duk Inda Zan kwatanta muku yanda 'yata ta dawo wlh bazaku gane ba sai wayanda Suka Santa lokacin da abun ya sameta.

Yadiko Bata fi minti talatin da fita ba sai Gata ta dawo da Mai mota datayi shatarsa.

Ni kuwa karkashin gadona na d'aga a cikin kudin sana'ata na dauko kudin da Dan yawa na rik'e a hannuna

Muka fito na roki Nadeeya data kularmin da gidan har ta rame itama.

Idonta yayi jawur dan kuka..

Muna fitowa muka dau hanya

Bamu Isa kauyen ba sai wajen karfe uku shima sai da muka hau machine Nadeeya na zaune a cinyata muka Isa gidan Mallam Mai sallati Haka ma Naga an saka daga wajen gidan

Ga almajirai Nan birjik suna ta karatu

Bamu Sha wahalar samun sa ba Bayan mutane biyu da suka Shiga ciki suna fitowa muka Shiga

Muna Sallama ya d'ago Suka had'a Ido da Zahira Zahira ta kwalla wani mugun. Ihu daya saka kunnena Yinn wani iri

Riketa nayi Kamar jaririya sai gashi ta duro da ga jikina ta hankadani tana k'ok'arin Yin waje.

Da mugun k'arfi na riketa Amma ga mamakina wani irin tureni tayi yadiiko itama tayi saurin riketa Dan Kar dai ta fita a gujen

Shafa Mata Jan miskin Nan a goshi Yi sauri

Mallamin yace Yana k'ok'arin mik'ewa sai dai kafin yaddiko ta bud'e kwalbar miskin Zahira ta Kara sakin wani mugun Karan ta zub'e a kasa ta hau wani jijjjiga hankali a tashe na fara k'ok'arin yin kanta Mallam Mai sallati ya hanani akan Kar na sake na tab'ata
Wani irin iska ne ya kaure a d'akin lokaci guda Kuma komai ya baje Naga Zahira ta bar jijjigan.

Mallam Mai sallati ya tsuuggna a gaban zahiran ya shafa Mata Jan miski tare da daure kanta da farin kyalle yace na ja ta gefe.

Da Sauri na dauki yata na Dora a cinya Dan tsayin kafafune kawai zai saka kasan babba ce amma ya dawo kamar dai yarinya siffar.dai Gata ga kamarta
Kukan da nake Bai saka na iya ce Masa komai ba sai yaddiko ce ta Dan Masa bayani

Shima Bai ce komai ba illa kasko Dana ga ya d'auko ya zuba wani hayaki a ciki ya hau bayani Yana "Kuna shigowa nasan turen bakakken Aljannu arna akayi Mata da har zai rabata da numfashinta zakuji jikinta na d'aukar zafi Bata iya bacci zatayi ta Abu kamar Mai tab'in hankali yanzu Kuna shigowa ma sun San ko yayane sai mun faffata dasu hakane yasa Kuna shigowa suka bar jikinta duk abinda zaayi yanzu basa jikinta Kuna tafiya zasu dawo jikinta Aljannu sun fi su ashirin kowane da aikin da yakeyi a jiknta.

Zaki kashe kudi baiwar Allah Dan yanka zamuyi muyi ta Basu hakuri har mu samu nassarar Mai dasu wajen wayanda Suka Mata turen bakakken Aljannun
Jiki na rawa na Ciro kudadeen Dana saka a Leda na mik'a.masa.

Bai karba ba ya Kira baban Almajiransa akan ya karba ya siyo.masa katon bijimin saa.a daure Masa daddare akwai aikin da zaiyi

A takaice Anan yadikko ta barni da Zahira tare da alkwarin duba min yarana

A ranar a gidan Mallam Mai sallati na kwana matansa sai tausayina suke karfe daya daidai Naga an yiwa Zahira alwala Dan har lokacin Bata bud'e idonta ba Almajirai sama da goma suna zagaye da ita Mai sallati Ma na d'aga gabanta suna ta karatu Yana Yi Yana yarfa mata ruwan addua Yana goge mata jikinta da wani ganye Zahira dai Bata motsa ba Ina kallonsu har sai da Mai sallati yasa aka kawo Masa kasko ya watsa wani irin magani Mai kamar borkono ko mu damuke nesa sai da mukaji zafinsa ya hau shigar mana hanci

Ahaka.yasa.mazan Nan suka d'ago.zahira da tana fara shak'ar hayakin ta bud'e Ido ta fara k'ok'arin fusgewa.ya da Danna kanta akan kaskon Yana saka kaskon a daidai hancinta ta kwalla wani irin Kara ta hau mimikewa idonta duk.ya yo waje

Bulala Naga mallamin ya d'auko ya hau zabga Mata Wai zasu yi.magana ko bazasu Yi ba

Tuni naji muryar yata ya dawo daidai ta hau ihun "Umma Dan Allah kizo ki.kwaceni daga hannunsa wlh Tallahi nice Umma Ni yake.duka"

Aguje na Isa wajensu shi kuwa Mai sallati ya daka min tsawa.akan Kar.na matso.kusa dashi ba Zahira bace Aljannu ne "(Ashe dgsk zahiran ce yake duka ya d'auka.aljannu.ne Dan Wasa sukayi ta Masa da hankali Yana Dan da rukiyya suke.fita idan suka.ga zaiyi wani Abu sai su.shiga jikinta su Yi abinda zaa dauka sune.

Ahaka yata ta Sha bulalai da hayakin Dake juyar.mata da.kai idan akayi har muka samu kwana uku ahaka a Rana na hudu da yace na Kara kawo kudi.

A ranar Naseer ya duro gidan Mai sallati hankalinsa a balain tashe Yadiko ta rakasho

Wanda zuwansa kenan su Nadeeya suka Gaya masa yaje har gidan yaddiko.ya rok'eta ta rakashi.

Ina ganinsa na fashe da kuka Bai kalli inda.nake ba ya nufi wajen Zahira dake shimfide a kasa kamar gawa idonta kawai manya.datake wurgawa tana kalle kalle yasa zaka San tana rayye

Tunda nake ban taba ganin Naseer a cikin tashin hankali Dana ganshi ba a lokacin Daya xube a gaban zahiran jikinsa na wani irin karkarwa cikin wani irin murya yace "Zahira"

Zahira siririn hannunta ta mik'a Masa cikin muryar Yara tana "Abba kayimin addua mutuwa Dan Allah Abba jikina konewa Yake kamar an hura garwashin wuta a wuyana"

Da hannu daya ya wawuro Zahira ya hadata da kirjinsa Yana "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Allahuma ajirni fi musibati wa aklifnin khairin minha
Allâhumma lâ sahla illâ mâ ja'altahu sahlan, wa anta taj'alu-l-hazana idhâ shi'ta sahlan.

Addua kawai yake Yana kamkame da Zahira a kirjinsa dayake Jin fatarta na kona Masa jiki

Cikin kuka nace "Naseer Dan Allah Dan annabi dan darajar Muhammad sallahu alaihi wa kaje wajen Umma da Safiyya ka Basu hakuri su kyallemin yata Bata musu komai ba ba abinda Zahira tayi data cancanci Haka daga wajensu kazo muje Naseer bana San na rasa yata ni suka tsana sumin hukunci Dan Allah Naseer kaga yanda suka dawomin da Zahira Zahira yanzu Kamar Mai tab'in hankali Naseer ka taimakamin muje na Basu hakuri kaga Zahira yanda ta dawo su sake min ita Dan Allah"

Na karashe Ina kuka

Mik'ewa yayi da zahiran a jikinsa Yana muje banyi gardama ba nabi bayansa

Ko sauraren Mai sallati bamuyi ba Dan nidai a idona Banda dukarmin ya da yayi ba abinda ya iya min sai kudadena daya cinyemin gabadaya Dan sai da na tattaro sauran kudin nasa Nadeeya ta bawa. Yaddiko ta kawomin ta hanyar Mata wasika

Shatar mota mukayi Naseer na rik'e da Zahira jikinsa Yana ta hawaye nidai burina nagani a wajensu Umma na kwanta nayita Basu hakuri

Sai dai muna isowa Kano Naga Naseer na cewa driver ya Kai mu station Inda na Kai kararsu Umma Ni kuwa cikin tashin hankali nace Mai zakayi
Chapter 37 · 0% Book details