Sashe 50
Naga Ta Kaina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Idona na Kan kofa tunda su Naseer suka fita da Nadeeya nemo Waleed bani da burin daya wuce irin naga sun dawo tare dashi dan yau ma ban saka shi a idona ba.
Ina Jin Zahira a d'aki da Naseer ya kulleta tana kananan surutai
Ni nasan da ikon Allah kawai nake numfashi har yanzu zuciyata bata buga ba idan na dubi Zahira 'yata da nake jinta duk a yarana sabida hankali da tarbiyya ta na ga yanda ta dawo yanzu yarinya fitsarariya sai naji kamar na cire zuciyata na Yar sabida ciwon da yake min a haka ma Wai dan Inna Amina na iya k'ok'arinta a kaina da yarana da babu ita bana Jin Zan kawo yanzu
Waleed dana daya tilo da yayi hannu Riga da duk wani Abu Mai kyau ya koma Mara kyau ganinsa a Wanan halin kawai na iya sawa zuciya ta ta buga lokaci guda
Na gwammaci ni su Umma suka hukunta suka ma kasheni da barina da sukayi a rayye da banida bambanci da mataciya sabida halin da yarana ke ciki.
Sun watsa min rayuwar yarana da Karfin addua Yata Zahira ta tsaya a iya bin kawaye bata hada da bin Maza ba
da Karfin addua Waleed ke rashin ji da bai had'a da sata da shaye shaye ba.
Nakan hararo da yarana Basu hadu da wanan jarrabtar ba da kila Zahira ta Dade a gidan aure ko tana mataki na biyu a babban makaranta sai dai Kash gata a gabana ko secondary bata gama ba an susutar min da ita.
Shigowar Nadeeya aguje tana ihun kuka yasa ni mik'ewa tare da dafe kirjina da na ji kamar an soka min kibiya.
"Umma 'yan sanda sun tafi da Waleed station saboda ya fasawa wani yaro kai da kwalba Abba yace idan Suka tafi dashi Kar a sake shi"
Tunda ta fara magana naji gidan na juyamin har Naseeru shima ya shigo a daidai lokacin dana tafi Zan zub'e a kasa ya taroni da sauri.
Sai da na jima Ina sallati kafin naji kaina ya daina juyamin
Maganar Nadeeya na Kara maimaituwa a kaina
Ido na sauke akan Naseer Ina "Wai an tafi da Waleed station Kuma kace Kar a sake shi"?
Kamar wanda na kwarawa ruwan zafi ya mike da Sauri yana "Duk ranar da Waleed ya taka kafarsa gidanan sai na raba shi da numfashinsa tunda ya zabi ya Zama dan iska gwara ya je ya cigaba da iskancinsa Kuma ban yarda wani yaje station dan yayi belinsa ba gwara suyita rikeshi acan"
Yana gama fadar haka yayi daki a fusace
Ni kuwa Zan iya cewa tunda ya fara magana nayi suman wucin gadi na kasa yarda Naseer ke furta kalmomin nan daga bakinsa.
Na dauka zai fi kowa Shiga tashin hankali da halin da Waleed ya tsinci kansa lura da irin Kaunar da yake Masa ga mamakina Dan namu yake cewa Dan iska
Bansan yanda akayi na mik'e na isa d'akin da ya Shiga ba yana Gefen gado a zaune
Ban karasa ciki ba daga bakin kofa na Kira sunansa da Naseer dan Abban Waleed nake ce Masa tunda na haifi Waleed na bar ce Masa Abban Zahira.
Indai na Kira sunansa toh ba karamin magana zamuyi dashi ba
dagowa yayi da jajjayen idonsa Yana kallona
"A hayyacin ka kake kuwa Naseer Waleed aka tafi dashi station a gaban idonka baka yi komai ba kace Kuma a idan an tafi dashi Kar a sake shi"?
"Eee Ni nace Kar su sake shi Naeema Kuma ban yarda wani yaje belinsa ba dan bazai yiwu ya ringa jawo mana magana ba yaje can ya karaci iskancinsa"
"Waleed kake jifa da munanan kalamai Naseer waye silar zaman Waleed haka?Mahaifiyarka da kanwarka su suka Zama silar gurbacewar tarbiyyar da na yiwa yarana Naseer Waleed da haka yake?Zahira da haka take a yanzu daka dawo daya Kamata mu had'a hannu wajen ceto yarana daga halaka Amma Kaine na farko wajen cewa yarona Dan iska? Tunda na aureka nake cikin tashin hankali ban taba samun nutsuwa ba daga wanan sai wanan yanzu Kuma an bar kaina an dawo Kan yarana Naseer na gaji wlh Tallahi na gaji idan har yarana basu dawo hayyacinsu ba bazan tab'a yafewa Mahaifiyarka da kanwarka ba"
"Ke ya isa haka akan Waleed Kike jifana da maganganun banza ke yanzu ko tuntub'e kikayi sai kice mahaifiya ta ce,kin ma bar yarda da duk abinda ya Sameki yin Allah ne komai komai mahaifiyata ce da kanwata ki Shiga hankalinki Naeema Kar San Yara ya susutaki bin abokanan banza ya jefa danki a halin da yake ciki da kinsa Ido akansa da duk baa Kai ga haka ba lokacin da nake gari Mai yasa duk hakan bai faru ba sai da bana nan "?
Zuwa yanzu shi kansa Naseer din na fara ganewa ba'a hayyacinsa yake ba yanda ya hayyayako min yasa naji na zo wuya na hau jifansa da maganganu masu zafi dan a lokacin zuciyata gayamin take kamar da biyu ma Naseer yake haka dan Yana ganin ya ruko canjina a hannu.
Musayan kalmomin da muke ne ya dagawa yarana hankali suka hau k'ok'arin janye ni daga wajensa
Amma fir naki na cigaba da jifan Naseer da magangunan da suka shake min wuya har sakina nace yayi idan yasan shi dan.halak ne dan aurensa bai kareni da komai ba sai wahala da nake sha tunda mukayi aure dashi bamu tab'a irin fadan da mukayi dashi ba ban Kuma tab'a ganin ya rufe Ido Yana cimin mutunci ba sai a wanan lokacin
Kukan da inna Amina ta saka yasa na ja bakina nayi shiru zuciyata na wani irin k'unna
Wa'azi ta hau yiwa Naseer
Ni kuwa na saka hijabina nayi waje da Nadeeya dan ta rakani gidansu yaron da Waleed ya fasawa Kai tunda tacemin ta san yaron.
Ga mamakina Ina zuwa ma nagane nasan mahaifiyar yaron.
Cikin kuka na hau bata hakurin abinda ya faru na rik'e hannun dansu da waleed ya fasawa kai da ya Sha bandeji a kansa na hau Masa sannu.
Bamu samu mahaifin yaron a gida ba da shi ya d'auki case din da zafi har aka Kai Waleed station hakane yasa muka zauna zaman jiran dawowarsa dan sai ya yafe Zan samu a sallami Waleed.
Ana kiraye Kirayen sallah Magriba ya shigo gidan da sallama babban dansa na biye dashi a baya.
Gaisuwar da muka Masa kawai ya amsa ya fara k'ok'arin Shiga falon matarsa ta dakatar dashi ta nuna mu tana wajensa muka zo ta Kara da bashi hakuri akan tunda Mai afkuwa ya riga da ya afku yayi hakuri kawai ya saki waleed.
Yanda ya hade rai yasa na fashe da kuka Ina cigaba da bashi hakuri Ina "Kayi hakuri d'a na kowane wlh Tallahi da ba haka yaron nan yake ba daga baya ya zama haka kila Kuma bazaku rasa sanin sa ba yaron nan dake yawan sharar Massallaci a kasan layi wlh shine ya dawo haka lokaci guda muna ta iya kokarinmu dan muga ya dawo hanya ayi hakuri a yafe Masa duk abinda aka kashe wajen maganin yaron Nan Zan bayar ka taimaka"
"Jikinsu sanyi yayi da suka ga yanda nake kuka a karshe mutumin yace ba komai Amma ya zama dole na dage Akan Waleed da yanzu abin yazo da tsautsayi dansa ya rasa ransa fa nasan yanda zanyi na raba Waleed dasu shagari.
Kar Waleed ya jawo min abinda ba shi kadai zaa kulle ba har damu.
Sai da yayi sallah Magriba ya huta duk.muna zaune kafin ya fito yace Mana muje.
Dubu daya na ajiye a Gefen yaron na Kara Masa Addu'a samun sauki
Na Kara yiwa mahaifiyarsa godiya na fito muka tafi station din.
Sai da nayi da gaske da kuka da magiya kafin su yarda zasu bada belin Waleed dan rashin kunya Waleed ya ringa musu.
Kudin da na basu da dan yawa yasa suka sakeshi.
A yanda na fahimci waleed idan ana Masa fada ko aka hukunta shi zuciyarsa Kara taurara yake dan da aka sakeshi wani irin hucci ya ringayi Kamar wani Zaki yabi wani dan sanda da mugun kallon daya sa dan Sandar rantsewa akan duk ranar da tsautsayi yasa aka Kara kawo shi station dinsu wlh bazasu sake shi ba
Waleed wani mugun Tsaki ya Masa ya wuce mu.
Ni kuwa nabi bayansa da Sauri Ina kwalla Masa Kira.
Da kyar ya tsaya ya zubomin Ido daya sa nake ganin kamar bani na Haife shin ba kamar ba dana Waleed dan Umma Dan lelen Abbansa yanda yayyensa kan tsokaneshi.
"Waleed so kake ka kasheni da raina ko"?
"Wai da nayi me har ni Abba zai ce a wuce dani station Kar a sakeni"?
Wani irin girgiza kai yayi ya barni a tsaya ya hau zuba Sauri
A haka muka ringa binsa a baya Ina kuka ni kadai nasan Mai nakeji a Zuciyata.
Muna isa gida yayi fatali da butan daya samu a tsakar gidan ya wuce d'akinsu zahira dan palo yayi niyyar Shiga Naseer dake zaune a palon yasa yayi tsaki kasa kasa ya nufi d'akin.
Butar da yayi kwalo dashi na dauko na zuba ruwa nayi alwala.
Na Shiga d'akin Inna Amina dan nayi Sallah Magriba
Nadeeya Kuma ta Shiga d'akinsu.
Ina cikin rakaa na karshe na ringa jiyo hayaniya daga d'akinsu zahira take hankalina ya rabu gida biyu.
Allah Allah kawai nake na iddar na tafi dakinsu Naga Mai ke faruwa
Sujjada nayi naji ihun raheema da k'arfi.
Da Sauri na Sallame sallahr na fito a lokaci guda muka isa d'akinsu zahira da Naseeru.
Waleed ne yake ta kwallo da raheema yayyensa na k'ok'arin rik'e shi.
Zahira na gefe kamar bata San Mai ke faruwa a d'akin ba.
Naseer cikin zafin nama ya isa garesu.
Ya damko Waleed da k'arfi.
Kafin kace me ya rufeshi da duka Yana naushi
Zagin Waleed kawai yake Yana jifansa da mugayen kalamai Waleed sai k'ok'ari Kare kansa yake ba ko tsoro a fuskarsa yanda ya tsaya ma Kamar zai iya rama dukan da babansa yake Kai Masa.
Taurin Kan Waleed ma yak'i bari yaji irin dukan da Naseer ke masa shi ake duka Amma ni.nakeji a jikina.
Tsakiyarsu na Shiga cikin ihun kuka Ina Naseer ya isa haka.kashe shi kake so kayi"?
Ina Jin Zahira a d'aki da Naseer ya kulleta tana kananan surutai
Ni nasan da ikon Allah kawai nake numfashi har yanzu zuciyata bata buga ba idan na dubi Zahira 'yata da nake jinta duk a yarana sabida hankali da tarbiyya ta na ga yanda ta dawo yanzu yarinya fitsarariya sai naji kamar na cire zuciyata na Yar sabida ciwon da yake min a haka ma Wai dan Inna Amina na iya k'ok'arinta a kaina da yarana da babu ita bana Jin Zan kawo yanzu
Waleed dana daya tilo da yayi hannu Riga da duk wani Abu Mai kyau ya koma Mara kyau ganinsa a Wanan halin kawai na iya sawa zuciya ta ta buga lokaci guda
Na gwammaci ni su Umma suka hukunta suka ma kasheni da barina da sukayi a rayye da banida bambanci da mataciya sabida halin da yarana ke ciki.
Sun watsa min rayuwar yarana da Karfin addua Yata Zahira ta tsaya a iya bin kawaye bata hada da bin Maza ba
da Karfin addua Waleed ke rashin ji da bai had'a da sata da shaye shaye ba.
Nakan hararo da yarana Basu hadu da wanan jarrabtar ba da kila Zahira ta Dade a gidan aure ko tana mataki na biyu a babban makaranta sai dai Kash gata a gabana ko secondary bata gama ba an susutar min da ita.
Shigowar Nadeeya aguje tana ihun kuka yasa ni mik'ewa tare da dafe kirjina da na ji kamar an soka min kibiya.
"Umma 'yan sanda sun tafi da Waleed station saboda ya fasawa wani yaro kai da kwalba Abba yace idan Suka tafi dashi Kar a sake shi"
Tunda ta fara magana naji gidan na juyamin har Naseeru shima ya shigo a daidai lokacin dana tafi Zan zub'e a kasa ya taroni da sauri.
Sai da na jima Ina sallati kafin naji kaina ya daina juyamin
Maganar Nadeeya na Kara maimaituwa a kaina
Ido na sauke akan Naseer Ina "Wai an tafi da Waleed station Kuma kace Kar a sake shi"?
Kamar wanda na kwarawa ruwan zafi ya mike da Sauri yana "Duk ranar da Waleed ya taka kafarsa gidanan sai na raba shi da numfashinsa tunda ya zabi ya Zama dan iska gwara ya je ya cigaba da iskancinsa Kuma ban yarda wani yaje station dan yayi belinsa ba gwara suyita rikeshi acan"
Yana gama fadar haka yayi daki a fusace
Ni kuwa Zan iya cewa tunda ya fara magana nayi suman wucin gadi na kasa yarda Naseer ke furta kalmomin nan daga bakinsa.
Na dauka zai fi kowa Shiga tashin hankali da halin da Waleed ya tsinci kansa lura da irin Kaunar da yake Masa ga mamakina Dan namu yake cewa Dan iska
Bansan yanda akayi na mik'e na isa d'akin da ya Shiga ba yana Gefen gado a zaune
Ban karasa ciki ba daga bakin kofa na Kira sunansa da Naseer dan Abban Waleed nake ce Masa tunda na haifi Waleed na bar ce Masa Abban Zahira.
Indai na Kira sunansa toh ba karamin magana zamuyi dashi ba
dagowa yayi da jajjayen idonsa Yana kallona
"A hayyacin ka kake kuwa Naseer Waleed aka tafi dashi station a gaban idonka baka yi komai ba kace Kuma a idan an tafi dashi Kar a sake shi"?
"Eee Ni nace Kar su sake shi Naeema Kuma ban yarda wani yaje belinsa ba dan bazai yiwu ya ringa jawo mana magana ba yaje can ya karaci iskancinsa"
"Waleed kake jifa da munanan kalamai Naseer waye silar zaman Waleed haka?Mahaifiyarka da kanwarka su suka Zama silar gurbacewar tarbiyyar da na yiwa yarana Naseer Waleed da haka yake?Zahira da haka take a yanzu daka dawo daya Kamata mu had'a hannu wajen ceto yarana daga halaka Amma Kaine na farko wajen cewa yarona Dan iska? Tunda na aureka nake cikin tashin hankali ban taba samun nutsuwa ba daga wanan sai wanan yanzu Kuma an bar kaina an dawo Kan yarana Naseer na gaji wlh Tallahi na gaji idan har yarana basu dawo hayyacinsu ba bazan tab'a yafewa Mahaifiyarka da kanwarka ba"
"Ke ya isa haka akan Waleed Kike jifana da maganganun banza ke yanzu ko tuntub'e kikayi sai kice mahaifiya ta ce,kin ma bar yarda da duk abinda ya Sameki yin Allah ne komai komai mahaifiyata ce da kanwata ki Shiga hankalinki Naeema Kar San Yara ya susutaki bin abokanan banza ya jefa danki a halin da yake ciki da kinsa Ido akansa da duk baa Kai ga haka ba lokacin da nake gari Mai yasa duk hakan bai faru ba sai da bana nan "?
Zuwa yanzu shi kansa Naseer din na fara ganewa ba'a hayyacinsa yake ba yanda ya hayyayako min yasa naji na zo wuya na hau jifansa da maganganu masu zafi dan a lokacin zuciyata gayamin take kamar da biyu ma Naseer yake haka dan Yana ganin ya ruko canjina a hannu.
Musayan kalmomin da muke ne ya dagawa yarana hankali suka hau k'ok'arin janye ni daga wajensa
Amma fir naki na cigaba da jifan Naseer da magangunan da suka shake min wuya har sakina nace yayi idan yasan shi dan.halak ne dan aurensa bai kareni da komai ba sai wahala da nake sha tunda mukayi aure dashi bamu tab'a irin fadan da mukayi dashi ba ban Kuma tab'a ganin ya rufe Ido Yana cimin mutunci ba sai a wanan lokacin
Kukan da inna Amina ta saka yasa na ja bakina nayi shiru zuciyata na wani irin k'unna
Wa'azi ta hau yiwa Naseer
Ni kuwa na saka hijabina nayi waje da Nadeeya dan ta rakani gidansu yaron da Waleed ya fasawa Kai tunda tacemin ta san yaron.
Ga mamakina Ina zuwa ma nagane nasan mahaifiyar yaron.
Cikin kuka na hau bata hakurin abinda ya faru na rik'e hannun dansu da waleed ya fasawa kai da ya Sha bandeji a kansa na hau Masa sannu.
Bamu samu mahaifin yaron a gida ba da shi ya d'auki case din da zafi har aka Kai Waleed station hakane yasa muka zauna zaman jiran dawowarsa dan sai ya yafe Zan samu a sallami Waleed.
Ana kiraye Kirayen sallah Magriba ya shigo gidan da sallama babban dansa na biye dashi a baya.
Gaisuwar da muka Masa kawai ya amsa ya fara k'ok'arin Shiga falon matarsa ta dakatar dashi ta nuna mu tana wajensa muka zo ta Kara da bashi hakuri akan tunda Mai afkuwa ya riga da ya afku yayi hakuri kawai ya saki waleed.
Yanda ya hade rai yasa na fashe da kuka Ina cigaba da bashi hakuri Ina "Kayi hakuri d'a na kowane wlh Tallahi da ba haka yaron nan yake ba daga baya ya zama haka kila Kuma bazaku rasa sanin sa ba yaron nan dake yawan sharar Massallaci a kasan layi wlh shine ya dawo haka lokaci guda muna ta iya kokarinmu dan muga ya dawo hanya ayi hakuri a yafe Masa duk abinda aka kashe wajen maganin yaron Nan Zan bayar ka taimaka"
"Jikinsu sanyi yayi da suka ga yanda nake kuka a karshe mutumin yace ba komai Amma ya zama dole na dage Akan Waleed da yanzu abin yazo da tsautsayi dansa ya rasa ransa fa nasan yanda zanyi na raba Waleed dasu shagari.
Kar Waleed ya jawo min abinda ba shi kadai zaa kulle ba har damu.
Sai da yayi sallah Magriba ya huta duk.muna zaune kafin ya fito yace Mana muje.
Dubu daya na ajiye a Gefen yaron na Kara Masa Addu'a samun sauki
Na Kara yiwa mahaifiyarsa godiya na fito muka tafi station din.
Sai da nayi da gaske da kuka da magiya kafin su yarda zasu bada belin Waleed dan rashin kunya Waleed ya ringa musu.
Kudin da na basu da dan yawa yasa suka sakeshi.
A yanda na fahimci waleed idan ana Masa fada ko aka hukunta shi zuciyarsa Kara taurara yake dan da aka sakeshi wani irin hucci ya ringayi Kamar wani Zaki yabi wani dan sanda da mugun kallon daya sa dan Sandar rantsewa akan duk ranar da tsautsayi yasa aka Kara kawo shi station dinsu wlh bazasu sake shi ba
Waleed wani mugun Tsaki ya Masa ya wuce mu.
Ni kuwa nabi bayansa da Sauri Ina kwalla Masa Kira.
Da kyar ya tsaya ya zubomin Ido daya sa nake ganin kamar bani na Haife shin ba kamar ba dana Waleed dan Umma Dan lelen Abbansa yanda yayyensa kan tsokaneshi.
"Waleed so kake ka kasheni da raina ko"?
"Wai da nayi me har ni Abba zai ce a wuce dani station Kar a sakeni"?
Wani irin girgiza kai yayi ya barni a tsaya ya hau zuba Sauri
A haka muka ringa binsa a baya Ina kuka ni kadai nasan Mai nakeji a Zuciyata.
Muna isa gida yayi fatali da butan daya samu a tsakar gidan ya wuce d'akinsu zahira dan palo yayi niyyar Shiga Naseer dake zaune a palon yasa yayi tsaki kasa kasa ya nufi d'akin.
Butar da yayi kwalo dashi na dauko na zuba ruwa nayi alwala.
Na Shiga d'akin Inna Amina dan nayi Sallah Magriba
Nadeeya Kuma ta Shiga d'akinsu.
Ina cikin rakaa na karshe na ringa jiyo hayaniya daga d'akinsu zahira take hankalina ya rabu gida biyu.
Allah Allah kawai nake na iddar na tafi dakinsu Naga Mai ke faruwa
Sujjada nayi naji ihun raheema da k'arfi.
Da Sauri na Sallame sallahr na fito a lokaci guda muka isa d'akinsu zahira da Naseeru.
Waleed ne yake ta kwallo da raheema yayyensa na k'ok'arin rik'e shi.
Zahira na gefe kamar bata San Mai ke faruwa a d'akin ba.
Naseer cikin zafin nama ya isa garesu.
Ya damko Waleed da k'arfi.
Kafin kace me ya rufeshi da duka Yana naushi
Zagin Waleed kawai yake Yana jifansa da mugayen kalamai Waleed sai k'ok'ari Kare kansa yake ba ko tsoro a fuskarsa yanda ya tsaya ma Kamar zai iya rama dukan da babansa yake Kai Masa.
Taurin Kan Waleed ma yak'i bari yaji irin dukan da Naseer ke masa shi ake duka Amma ni.nakeji a jikina.
Tsakiyarsu na Shiga cikin ihun kuka Ina Naseer ya isa haka.kashe shi kake so kayi"?