← Book details Naga Ta Kaina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 39 OF 62

Sashe 39

Naga Ta Kaina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Jikinta ta Kara kwasar wani mugun zafin

Ni kuwa ihunta yasa na Shiga d'akin Aguje
Dan Sandan ne ya iya riketa Gam

Ni kuwa na durk'ushe a Gefen gadon na hau kuka
Ina kallonsa yana totofa Mata adduoi

Likitan kuwa cikin tausayawa yace mu Kai Zahira wajen Mallamai cutarta bana asibitin bane jikinta yanda yake d'aukar zafi ba Normal bane.

Likitan kuwa dak'yar ya samu ta bar fusge fusge ya Kira Yar Sandan Nan ta rik'e min Zahira ya fito na bisu a baya muka nufi d'akin da aka maida Naseer da aka Masa Karin ruwa da oxygen a hanci sabida Baya iya numfashi

Ganin Naseer a wanan halin da Zahira dake hannun Yar Sandan Kamar jaririya sai idanduna yasa naji jiri na d'ibana na zub'e a kasa kaina Kamar ya Fado

Sallati kawai nake zuciyata na bugawa yanda nake Jin kirjina kamar zai Faso

Kamar na zauce Haka nakeji idan na kalli Naseer na kalli Zahira

Sai da muka shafe kusan sati daya da kwana uku kafin Naseer yasan ma Inda kansa yake duk yabi ya rame ya fice a hayyacinsa

Bazan manta Dan Sandan Nan ba a rayuwata Dan ya taimaka min sosai har matarsa yasa ta ringa zuwa duba mu inta tashi zuwa Haka zata Zo Mana da abinci da kayan marmari

Sosai Dan Sandan ya ringa k'ok'arin nemo Safiyya da Umma da sai da suka koma can gidan da suke haya Suka Kara bincike Amma duk Basu San Inda su Umma suka koma ba

Matarsa da nasan na girme Mata sosai Ita ta ringa Dan kwantar min da hankali da Wanan yadiiko makociyata Zahira kuwa amadadin sauki ma abin nata Kara jagulewa yake karfe dayan dare nayi zata hau kururuwa Tana zunduma ihu tana fusge fusge wani zubin ta kankameni tana na boyeta gasu Nan zasu caka Mata wuka wani zubin Kuma tana kuka tana na roka Mata Allah ya d'auki ranta ko zata huta da wutan da ake hura Mata a jikinta

Naseer daya dawo hayyacinsa aka Sallame mu Haka ya zauna kamar mace Yana kuka wiwi Haka na tsaya akansa ya Dan samu lafiya

Muka bazama nida shi Muka hau Nemo Mai taimaka Mana da magani Dan Zahira ta samu sauki

Mutanen da suka San larurar Zahira Haka suka ringa zuwa kowane da kalar Wanda zasu ce muje wajensa ya kware a rukkiya mune Nan mune can fiye da wata hudu komai na mu ya Kare wajen. Bin Mallamai a karshe Naseer ya gaji yace mu hakura Haka mu Zo muyita gayawa Allah Yana kuka ya bud'e Baki Yana "Allah Kai ka halliceni ban nufi matar Nan da komai ba sai alheri ban taba bijire mata ba hasali sau daya nasan nayi kuskure hannu na ya Isa ga kumatunta da har gobe nake neman yafiyarka ba abinda Bata min ba karshe ta had'a da yiwa yata turen bakakken Aljannun ya Allah kayimin sakayya tsakanina da ita Allah ya Isa"

Da Sauri na rufe Masa baki na girgiza Masa Kai Ina "Ba sai ka Mata Allah ya Isa ba ka Gama magana tunda kace Allah ya saka Mana kuka ba naka bane Naseer neman kudi zamuyi mu nemowa Zahira magani kaga yanda Yara suke cika k'ofar gidanan suna ce wa da dodo a gidanan Wai yata ce dodo Naseer Zahirata ce dodo"

Kuka ne yaci karfina sabida yanda abin ke min ciwo.

Idon Zahira daya fito warwaje da kasusuwanta da suka fito na jikinta da Abu da takeyi kamar Mai tab'in hankali yasa yaran unguwar wani zubin cika k'ofar gidana suna lekan Zahira

Nadeeya da Minal ne ma wani zubin suke fita su Kori yaran wani zubin har da duka

Wasu Kuma yaran haka zasu wayance da zasu Sha ruwa ko suna neman wani Abu Wai duk Dan suga Zahira

K'arfi da yaji na koma kulle ta a daki

Dan Sandan Nan ma Haka ya ringa kawo min mallamai masana addini suna iya kokarinsu akan zahiran

Sai dai duk a banza abinda kawai Zahira ta samu saukinsa shine zafin Nan da jikinta ke dauka ya ragu

Wani zubin Kuma tana iya bacci da Rana Amma fa idan dare yayi Haka zata tayi ta ihu tana fusge fusge har garin Allah ya waye Haka Naseer zai tsaya akanta dagani har Naseer ba Mai bacci a cikinmu Haka Nadeeya da kannenta sai dai idan bacci ne ya d'auketa

Nakanji ma ance mak'ota nayi damu Wai Zahira na damunsu da ihu da Kara wasu Kuma tausayi take basu.

Komai nawa ya kare a nemawa Zahira magani daidai da suturuna duk na siyar da rabi
Naseer ma har filinsa ya siyar Bai gayamin ba yaje can har garin calabar neman su Umma Wai duk Dan ya rokesu su dawo Mana da Zahira daidai Amma ya karaci nemansu Bai gansu ba har Mallam Musbahu sai daya nema bai samu ma Mai labarinsa ba sai Haka ya dawo.

Muka cigaba da neman Mai yiwa Zahira magani

Har muka shekara a cikin wanan masifa da balain

Sai maneman Nadeeya ke Dan taimaka Mana wani zubin har da na Minal din Dan duk sun kawo girma.

Kuma ba laifi manyan mutane ke zuwa neman Nadeeya dayake baa nutse muke ba bama bi takanta ba laifi ba iya Zahira keda farinjini ba ga dukan alamu yaran nawa Rabbi ya musu farinjini Zan iya cewa albarkacin masu neman Nadeeya da auren yanzu asirinmu ke rufe Dan sukan mata kyautar ban girma ko su siyo kayayakin abinci Dana gida da Sunan kayan Dubiya kila sun San Daga Ni har Naseer din muna bukatar taimakone

Ganin Nadeeya tana neman amfani da Wanan damar wajen wankar Samari yasa na taka Mata birki Akan ta tsayar da hankalinta waje daya ta ringa kula guda a cikinsu

A Haka ta tsayar da Wanda yafi kudi a cikinsu da bansani ba Dan tana sanshi take kulashi ko Dan Yana kashe Mana kudin ne Dan ta taimaka Mana.

Halin da muke ciki Bai saka na Bari sun dakata da zuwa makaranta ba da ace larurar Nan Bai samu Zahira da yanzu tayi candy Kila ma har ta samu Wanda hankalinta ya kwanta dashi ya fito na aurar da ita Amma Ina ga diyar tawa Nan rabi mutum rabi wani hallita

Naseer kuwa ganin Abu yak'i ci yak'i cinyewa yacemin mu barwa Allah komai mu dage da Addu'a muyita Gaya masa yana sane damu.

Take kuwa nayi naam da shawararsa Dan ko Ni Nagaji da yawon bin Mallamai da Kamar kudinmu kawai suke cinye Mana

Daga Ni har shi Haka Muka dukufa da Addu'a.

Kullum bakina d'auke da azumi

Yata kuwa bazan iya bada labarin yanda ta dawo ba dan ba sauki wajenta sai a wajen Allah.

( Na Dan gajarta labarin sabida da yawa)

A haka Watarana da Zahira ta samu shekara guda da wata hudu da Wanan lalurar ranar alhamis wajen biyar na yamma Naseer na zaune a tsakar gida a zaune hannunsa dauke da Qurani Yana Dan karantawa kasa kasa dayake dagani har shi azumi muke

Nadeeya tana kitchen tana Mana abinci su Minal Kuma suna Palo suna duba littattafansu

Ni Kuma Ina zaune akan tabarma na Dora Kan zahira a cinyata Ina Dan Mata fifita bama gashi yanzu a kanta kanta ma ya dawo kararrami.

Ba bacci take ba idonta biyu tana kalle kalle tsullum Naga ta mik'e Ina ganin Haka nasan Kashi takeji

Har na Saba da halin nata Bata Shiga bandaki ba Kamar iska zai d'auketa taje lungun band'akin ta tsugunna Dan ita abinda zai Zama daidai batayin shi sai dai akasin Haka.

Tana gamawa na fara k'ok'arin mik'ewa Dan na wanke Mata Naga Minal ta fito daga d'aki taje ta wanke Mata tare da gyara gurin

Ina Jin dadi da yarana basa kyankyaminta ko waleed da ya girma shima yanzu ya daina tsoronta wani zubin ma yakan wanke Mata kayayyakinta Dan ba laifi Waleed Dina akwai hankali ga hazaka da k'ok'ari tamkar mahaifinsa

Haka kawai ma zai je kusa da Zahira ya hau Mata addua Allah ya Bata lafiya wani zubin sai yacemin ya fadawa mallaminsu yayiwa yayarsa addua samun lafiya

Dawowa tayi wajena ta kwanta na gyara Mata rigarta daya Mata yawa da siyowa ma mukayi sabida duk kayan kannen ta ma sun mata yawa
.iskar danaji Yana kadani ga Ina Dan Jin azumin yasa na kwallawa humaira Kira akan ta d'auko min pillow tana kawomin na kwanta Nan da Nan bacci yayi awon gaba da Ni.

*Mafarki*

A wani katon fili na tsinci kaina amadadin gida Ina kwance dai Akan tabarmar Zahira na gefena a zaune hakane ya na mik'e da balain sauri dana ga ta dawo daidai yanda take. Ada

Ina k'ok'arin Magana na hango Yara sun kewaye wata Mata tana ta raba musu alewa suna ta murna suna tsalle.

Haka kawai sai naji inasan ganin fuskar.matar tana juyowa Naga mahaifiya tace Fuskarta d'auke da murmushi tana ta rabawa yara alewa suna Kara titilowa suna tsallen murna wani irin mik'ewa nayi na fara k'ok'arin Isa wajenta cikin tsananin murna Ina Umma

Sai dai tafiya kawai nake na kasa Isa wajenta har har ta Gama raba alewar Nan Naga ta nufi wajen wata dake kwance a kasa kamar matacciya

Tana zuwa wajenta Naga ta ajiye kwanun abinci a gabanta matar kuwa ta mik'e da sauri ta hau ci tana yiwa Mahaifiyata godiya

Tana Gama ci ta mik'e.

Tana Mahaifiyata ta ceto ta tagode

Ta fara tafiya Kamar ba itace a kwance kamar.mataciya ba

Ni kuwa sai kwalla Mata Kira nake Amma Bata kalleni ba sai k'ok'ari nake na Isa wajenta

Bubbuga pillon da nake Kai da sunana da Naseer ya Kira yasa na bud'e idona

"Tashi kinsan babu kyau bacci uwar Haka Amma kusa Shan ruwa"

Ban ma iya motsawa na dawo cikin hankalina ba sai Dana Gama karewa gidana kallo na tabbatar da mafarki nake Ashe

Rabon da Naga mahaifyata a mafarki har.na manta
Mai ma'anar mafarkin da nayi da Mahaifiyata"?

Sosai mafarkin ya tsayamin a wuya Ina tuno yanda mahaifiya ta keta sadaka Yara na murna da abinci data bawa wata dake kwance kamar matacciya daga ci ta mik'e.

Dak'yar na iya Shan kunu Dana Sha ruwa sabida tunani

A karshe Dana kasa hakuri na gayawa Naseer mafarkin danayi

Nace ko ya San fassarar mafarkin?
Chapter 39 · 0% Book details