Sashe 44
Kamarsu Ce Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zainura ta koma kusa da Irfan tace Wai kai ina budurwarka nuna min ita na kure karyar gayu,Irfan ya nuna mata pics din wata me dan kyau a wayarsa yar gayu da ita,Zainura tace tab yasin baka iya Zabe ba tana haihuwa zata tsufa,kuma da gani yanga zata ma kana Shan wahala da ita,kalleta fa a haka ko shinkafa baza ta iya dafawa ba tun kafin tafiya tayi nisa ka canja wata,haba ai kafi karfin wannan,kalli Na'im yanda ya zabo yar gaske amma kai ka dauko gwalagwaje,Irfan sai lokacin ya hango munin budurwarsa da ta nace masa har yace yana sonta,yace dama ita take so na ni,Zainura tace amma kai kwai dolo wlh me zaka ci da wacce zata dinga sonka bata da aji ita ta damu da kai to taya zaka yi soyayya irin ta Na'im da Salma me dadi?
Irfan girman turai ba wayo sai ya dauki maganar Zainura tana ta Zugashi tana kushe masa Budurwa har yaji dama Ashe ba sonta yake ba wayo tayi masa,yace zanje dake zance ki ganta kuma wlh tayi ta yanga da kyar take magana baki gani ba wahala take bani,Zainura tace ka dauko caka Allah sarki za a cinyeka a caca a banza,Irfan yace naji dadi da kika ganar dani gaskiya,Zainura tace af ka kiyayi mata marasa aji masu Mannewa maza ba don Allah suke son mutum ba,kyanka da kudinka suka gani ni yanzu kaga yar kauye ce ni ko?yace eh tace to bazan aureka ba gwara na auri Ashiru na ko Audu me kifi sabo da dan Allah nake sonsu,Irfan yace gaskiya ke na garine Zainura mijinki ya huta,Zainura tace Allah ne yasa iyayenmu sun mana tarbiya mu bama son mutum dan abinsa,kuma mu idan muka rangada girki to mutum fa sai ya manta agogonsa,Hunaif ya kyalkyale da dariya dan yana jin yanda Zainura take ta yiwa Irfan wayo baya ganewa shi sai yaji Zainura da iyayenta sun birgeshi ma wlh.
Zainura tace kuma cewa kuma tana da Addini?Irfan Ya tabe baki cikin hausarsa da shima dai ba fita take can ba yace ni nan dai Bana taba Jin tana kiran ko name of Allah sau daya ba,Zainura ta tabe baki tace to anya kuwa tana Sallah? Kaga ko ta nan baka yi dace ba domin baza tayi addua ba,yaranka ba tarbiya,Irfan yaja tsaki tare da cewa kinga tana kirana,Zainura tace daga muji,ya daga hello sai ga muryarta tace Babyna ina ta sauraronka shuru anjima zan shigo wajenka gidanku,kuma kace zaka sake min mota har yau ban jika ba,Irfan yace sai kinzo ya datse wayar.
Zainura ta jinjina kai tace abin ya wuce tunani na harda roko? Wai kuma zata biyoka har gida? Irfan yace hmmm haka take min wlh ni shi yasa ma Bana ta sonta, Zainura tace to kayi karatun ta nutsu ka rabu da ita ba tare da wulakantata ba kuyi rabuwar mutunci yanda baza taji haushi ba na San Mummy bata son Wannan Rayhanat din taka,Irfan yace kamar kin sani wlh tace bata sonta bata da tarbiya.
Zan tsara ma yanda zaku rabu da ita ba tare da kun samu matsala tsakaninku ba.Irfan ya mikawa Zainura hannu yace nice to meet u,ta kalli hannun kawai tare da cewa Bana harkar yahudu da Nasara ni,Nan Irfan Ya tuno Rayhanat dinsa da gudu take cafe masa hannu tana rungumeshi tana damunsa da Romancing a ransa yace gaskiya Zainura ta fada Rayhanat bata da tarbiya wata zan canja,hhhhh shegiya Zainura.
Malam da Umma har mamaki suke Na'im da Salma ko Saurararsu basa yi lallai Memory baiyi abin kirki ba ya raba su,su kuwa sun shaku dasu zaman da suke a birni ba Na'im da Salma kusa ba dadi gaba daya ma ya ishesu,suna cika kwana Uku suka fito cikin shirin tafiya kauyensu,Mummy bata so tafiyarsu ba sun saba haka Dada ma da take zuwa kullum wajensu, Mummy ta hada musu Sha tara ta kirki tare da Kudi masu yawa Malam yaki karba ko kwandalarsu,babu yanda basuyi ba yaki karba,sai kaya kawai na sutura da Mummy ta siya musu shaddoji da atamfofi masu tsada da sauran abubuwa shima dan kar Suga Malam ya musu wulakanci ne shi yasa ya karba,Salma da Na'im suka musu godiya tare da cewa suyi hakuri suna tuna memory dinsu zasu zo,Zainura harda kuka za a tafi a barta a birni ita wajen Baffanta take so da kyar Mummy ta shawo kanta tace Irfan zai dinga kaita yawo kuma za a sata a makaranta.
Umma kuka sosai tayi na rabuwa da yaranta da basa tunata Salma da Na'im Malam ma yaji ba dadi sabo da sun shaku matuka,haka suka tafi daga Umma sai Malam sunyi exchange na waya za a dinga gaisawa.
Lfy Malam suka sauka a kauye sannan Mummy ta kira taji sun sauka lfy suka yiwa Allah godiya,Malam yayiwa maigari bayani da kuma Baban Zainura,Baban Zainura yace wlh in suna so ma zan iya bar musu ita ni da gyatimarta zamu dinga zuwa muna ganinta itama tazo Hutu,indai zatayi karatun dama surutun kauye yasa zan aurar da ita amma karatun ai yafi,kuma idan gidan mutunci da tarbiya ne ai da na kowa ne,mene a auren ma na kauye kaga yarinya na wahala,Allah sa mu dace ya Zaba mafi alkhairi,Malam yaji dadi shima.
Salma yanzu Zainura ta tsoratata ta daina nesa da Na'im kullum tana manne a wajensa,wajen aiki ma sai ta fara kuka sai ya tafi da ita,kuma da yace zai tabata ta fara shagwabar Kuka,haka yake kyaleta bai San wannan halin nata ba.
Yanzu ma yayi shirin fita Hospital ya fito da saurin gaske tare da Shan gabansa taci wankan sugar shagwaba ta fara tana doka kafafu Allah..sai ka je dani,ba inda zanje dake bakya bari nayi aiki kuma wahala kike jefani kullum,sai kin jawo ina feeling sai kice ke waye waye,matsa min na wuce ki daina zuwa kusa dani tunda ke baki da Imani naga Alama.
Salma ta cuno baki tana Hawaye bata yarda ba,Zai wuce ta rike rigarshi kam tana binsa kamar jela,Mummy ta fito tare da Zainura,Zainura tace Mummy kalla kiga abinda sukeyi a can kice lallai ya tafi da ita wlh a kauye komai tare sukeyi baki gani ba,Mummy tace Salma lfy?naga kina kuka, Tace shine fa Mummy yake sawa ana kira masa Budurwa yana zance da ita,Na'im yayi dariya jin sharrin Salma,Na'im yace kin San dai Mummy ko mene a gida nakeyi Bana Jin kunyar kowa,nace bani zuwa da ita Office wai sai taje,Mummy tace to ka tafi da ita mana,Na'im yace na rantse ai ni bazanje da ita ba,tana sa mutum yana son Iskanci tana tafiyarta,Zainura ta rufe baki jin Na'im ya tafka abin kunya gaban Mummy,Mummy tace naga ranar da zaka girma Na'im har yau kana nan a haka Allah ya shiryeka,Salma sakeshi ya tafi idan ya dawo kema ki murza kambunki,Salma ta kara fashewa da kuka wai ita an tauye mata hakki,wanne kambu zan Murda masa bayan ya daina sona kuma wata zai kula,Mummy tace maganinka ke nan baka San inda rana zata fadi ba ka dinga shigo da mata gidan nan gabanta gashi nan tana zarginka bata yarda da kai ba,yanzu dadi kaji haka? Zainura tace ke Salma laifinki ne fa ya za ayi sabo da baki da Number 7 a kwakwalwarki ta kwance zakice sai kinbi miji unguwa haka kikaga matan aure sunayi,ke baza ki Kula da gidan miji ba sai kin bishi unguwa,a kauye baya kula kowa sai ke mata ma basu isheshi kallo ba,Na'im yace a nan ma fa ita take korar min yan mata Bana yin komai dasu zata koresu,sai kuma ki dinga zarginsa aurenki ya mutu a haka baki sani ba,wa yace miki ana zargi a aure,Mummy tace yawwa Zainura halina dake kwai wayo da hankali,Salma tayi shuru dai tace ita dan kawai Mummy ta hakura amma wlh da sai anje da ita dole,Mummy tace Zainura je ki taso min Hunaif da Irfan su fito sauri.
Salma tunda Na'im ya fita ta kasa zaune ta kasa tsaye,ta koma waje da hijab dinta ta zauna a garden tana ta jiransa abu kadan ta kalli agogo,Waya ta dauka da ya siya mata ta danna masa kira ya dauka,ko magana baiyi ba tace lokaci ai dai yayi haka ko,Na'im yana dariyar Jin dadi Salma na sonsa yace sai fa 6pm yanzu 1pm fa gaba daya,Salma tayi rau rau da ido,idan na dawo me zaki bani? Salma tace sai zan baka abu zaka dawo gida wajen matarka? Yace to sai 6pm wlh am serious ki daina ma tambayata yaushe zan dawo ina da aiki da yawa,nan taji muryar wata Nurse tace Sir a kawo tea? Salma tace dan Allah nazo?na San Office din fa,Yace Embassy zan tafi yanzu kiyi zamanki na fada miki Bana son Nacin magana zamu bata dake.
Salma ta kashe wayarta ta Mike ta tafi neman Shawarar Zainura.
Zainura kuwa dakin Hunaif ta kwankwasa yace ke gani nan karki balla min kofa Mummy ce ke nema na,Zainura ta jikin kofar tace na shigo muga dakin naka? Shigo mana,ta shigo taga Room hadadde yasha gyara tace gayu an sanka ba asan makwancinka ba yanzu haka dama kake Kazami ciki kake kwana,Hunaif yayi dariya tare da cewa wlh karya kike yarinya an fada miki saurayinki ne Audu me Kifi? Kayi sauri ka fito to bari na taso uban masu motsa jiki,tana shiga Dakin Irfan taga ma kamar yafi na Hunaif haduwa tafi raina Irfan knocking kawai tayi da Sallama ta shiga,Yana fesa turare ta kalleshi taga bai ma ko kalleta ba,tace Yasin da irin su Audu me kifi ne ko ubale Alquran da tuni yana kallona yana zare Ido anga mace,Irfan ya dinga dariya yace to ni ba su bane kuma kullum sai naga mata hadaddu,haka a UK wacce macece ban gani ba,idan tsirara zakiyi wlh sai naga dama zan kalleki,Zainura tace ja jiki malam shaddar kasuwa ka gani,muna matane dama can jikinsu kowa ganinsa yake,kai yanzu kaga jikina ba sai kwakwawarka ta juye ba,na kananan kwari kake gani jakan mata amma mu irinmu mun fi karfin a kallemu a wuce.
Irfan girman turai ba wayo sai ya dauki maganar Zainura tana ta Zugashi tana kushe masa Budurwa har yaji dama Ashe ba sonta yake ba wayo tayi masa,yace zanje dake zance ki ganta kuma wlh tayi ta yanga da kyar take magana baki gani ba wahala take bani,Zainura tace ka dauko caka Allah sarki za a cinyeka a caca a banza,Irfan yace naji dadi da kika ganar dani gaskiya,Zainura tace af ka kiyayi mata marasa aji masu Mannewa maza ba don Allah suke son mutum ba,kyanka da kudinka suka gani ni yanzu kaga yar kauye ce ni ko?yace eh tace to bazan aureka ba gwara na auri Ashiru na ko Audu me kifi sabo da dan Allah nake sonsu,Irfan yace gaskiya ke na garine Zainura mijinki ya huta,Zainura tace Allah ne yasa iyayenmu sun mana tarbiya mu bama son mutum dan abinsa,kuma mu idan muka rangada girki to mutum fa sai ya manta agogonsa,Hunaif ya kyalkyale da dariya dan yana jin yanda Zainura take ta yiwa Irfan wayo baya ganewa shi sai yaji Zainura da iyayenta sun birgeshi ma wlh.
Zainura tace kuma cewa kuma tana da Addini?Irfan Ya tabe baki cikin hausarsa da shima dai ba fita take can ba yace ni nan dai Bana taba Jin tana kiran ko name of Allah sau daya ba,Zainura ta tabe baki tace to anya kuwa tana Sallah? Kaga ko ta nan baka yi dace ba domin baza tayi addua ba,yaranka ba tarbiya,Irfan yaja tsaki tare da cewa kinga tana kirana,Zainura tace daga muji,ya daga hello sai ga muryarta tace Babyna ina ta sauraronka shuru anjima zan shigo wajenka gidanku,kuma kace zaka sake min mota har yau ban jika ba,Irfan yace sai kinzo ya datse wayar.
Zainura ta jinjina kai tace abin ya wuce tunani na harda roko? Wai kuma zata biyoka har gida? Irfan yace hmmm haka take min wlh ni shi yasa ma Bana ta sonta, Zainura tace to kayi karatun ta nutsu ka rabu da ita ba tare da wulakantata ba kuyi rabuwar mutunci yanda baza taji haushi ba na San Mummy bata son Wannan Rayhanat din taka,Irfan yace kamar kin sani wlh tace bata sonta bata da tarbiya.
Zan tsara ma yanda zaku rabu da ita ba tare da kun samu matsala tsakaninku ba.Irfan ya mikawa Zainura hannu yace nice to meet u,ta kalli hannun kawai tare da cewa Bana harkar yahudu da Nasara ni,Nan Irfan Ya tuno Rayhanat dinsa da gudu take cafe masa hannu tana rungumeshi tana damunsa da Romancing a ransa yace gaskiya Zainura ta fada Rayhanat bata da tarbiya wata zan canja,hhhhh shegiya Zainura.
Malam da Umma har mamaki suke Na'im da Salma ko Saurararsu basa yi lallai Memory baiyi abin kirki ba ya raba su,su kuwa sun shaku dasu zaman da suke a birni ba Na'im da Salma kusa ba dadi gaba daya ma ya ishesu,suna cika kwana Uku suka fito cikin shirin tafiya kauyensu,Mummy bata so tafiyarsu ba sun saba haka Dada ma da take zuwa kullum wajensu, Mummy ta hada musu Sha tara ta kirki tare da Kudi masu yawa Malam yaki karba ko kwandalarsu,babu yanda basuyi ba yaki karba,sai kaya kawai na sutura da Mummy ta siya musu shaddoji da atamfofi masu tsada da sauran abubuwa shima dan kar Suga Malam ya musu wulakanci ne shi yasa ya karba,Salma da Na'im suka musu godiya tare da cewa suyi hakuri suna tuna memory dinsu zasu zo,Zainura harda kuka za a tafi a barta a birni ita wajen Baffanta take so da kyar Mummy ta shawo kanta tace Irfan zai dinga kaita yawo kuma za a sata a makaranta.
Umma kuka sosai tayi na rabuwa da yaranta da basa tunata Salma da Na'im Malam ma yaji ba dadi sabo da sun shaku matuka,haka suka tafi daga Umma sai Malam sunyi exchange na waya za a dinga gaisawa.
Lfy Malam suka sauka a kauye sannan Mummy ta kira taji sun sauka lfy suka yiwa Allah godiya,Malam yayiwa maigari bayani da kuma Baban Zainura,Baban Zainura yace wlh in suna so ma zan iya bar musu ita ni da gyatimarta zamu dinga zuwa muna ganinta itama tazo Hutu,indai zatayi karatun dama surutun kauye yasa zan aurar da ita amma karatun ai yafi,kuma idan gidan mutunci da tarbiya ne ai da na kowa ne,mene a auren ma na kauye kaga yarinya na wahala,Allah sa mu dace ya Zaba mafi alkhairi,Malam yaji dadi shima.
Salma yanzu Zainura ta tsoratata ta daina nesa da Na'im kullum tana manne a wajensa,wajen aiki ma sai ta fara kuka sai ya tafi da ita,kuma da yace zai tabata ta fara shagwabar Kuka,haka yake kyaleta bai San wannan halin nata ba.
Yanzu ma yayi shirin fita Hospital ya fito da saurin gaske tare da Shan gabansa taci wankan sugar shagwaba ta fara tana doka kafafu Allah..sai ka je dani,ba inda zanje dake bakya bari nayi aiki kuma wahala kike jefani kullum,sai kin jawo ina feeling sai kice ke waye waye,matsa min na wuce ki daina zuwa kusa dani tunda ke baki da Imani naga Alama.
Salma ta cuno baki tana Hawaye bata yarda ba,Zai wuce ta rike rigarshi kam tana binsa kamar jela,Mummy ta fito tare da Zainura,Zainura tace Mummy kalla kiga abinda sukeyi a can kice lallai ya tafi da ita wlh a kauye komai tare sukeyi baki gani ba,Mummy tace Salma lfy?naga kina kuka, Tace shine fa Mummy yake sawa ana kira masa Budurwa yana zance da ita,Na'im yayi dariya jin sharrin Salma,Na'im yace kin San dai Mummy ko mene a gida nakeyi Bana Jin kunyar kowa,nace bani zuwa da ita Office wai sai taje,Mummy tace to ka tafi da ita mana,Na'im yace na rantse ai ni bazanje da ita ba,tana sa mutum yana son Iskanci tana tafiyarta,Zainura ta rufe baki jin Na'im ya tafka abin kunya gaban Mummy,Mummy tace naga ranar da zaka girma Na'im har yau kana nan a haka Allah ya shiryeka,Salma sakeshi ya tafi idan ya dawo kema ki murza kambunki,Salma ta kara fashewa da kuka wai ita an tauye mata hakki,wanne kambu zan Murda masa bayan ya daina sona kuma wata zai kula,Mummy tace maganinka ke nan baka San inda rana zata fadi ba ka dinga shigo da mata gidan nan gabanta gashi nan tana zarginka bata yarda da kai ba,yanzu dadi kaji haka? Zainura tace ke Salma laifinki ne fa ya za ayi sabo da baki da Number 7 a kwakwalwarki ta kwance zakice sai kinbi miji unguwa haka kikaga matan aure sunayi,ke baza ki Kula da gidan miji ba sai kin bishi unguwa,a kauye baya kula kowa sai ke mata ma basu isheshi kallo ba,Na'im yace a nan ma fa ita take korar min yan mata Bana yin komai dasu zata koresu,sai kuma ki dinga zarginsa aurenki ya mutu a haka baki sani ba,wa yace miki ana zargi a aure,Mummy tace yawwa Zainura halina dake kwai wayo da hankali,Salma tayi shuru dai tace ita dan kawai Mummy ta hakura amma wlh da sai anje da ita dole,Mummy tace Zainura je ki taso min Hunaif da Irfan su fito sauri.
Salma tunda Na'im ya fita ta kasa zaune ta kasa tsaye,ta koma waje da hijab dinta ta zauna a garden tana ta jiransa abu kadan ta kalli agogo,Waya ta dauka da ya siya mata ta danna masa kira ya dauka,ko magana baiyi ba tace lokaci ai dai yayi haka ko,Na'im yana dariyar Jin dadi Salma na sonsa yace sai fa 6pm yanzu 1pm fa gaba daya,Salma tayi rau rau da ido,idan na dawo me zaki bani? Salma tace sai zan baka abu zaka dawo gida wajen matarka? Yace to sai 6pm wlh am serious ki daina ma tambayata yaushe zan dawo ina da aiki da yawa,nan taji muryar wata Nurse tace Sir a kawo tea? Salma tace dan Allah nazo?na San Office din fa,Yace Embassy zan tafi yanzu kiyi zamanki na fada miki Bana son Nacin magana zamu bata dake.
Salma ta kashe wayarta ta Mike ta tafi neman Shawarar Zainura.
Zainura kuwa dakin Hunaif ta kwankwasa yace ke gani nan karki balla min kofa Mummy ce ke nema na,Zainura ta jikin kofar tace na shigo muga dakin naka? Shigo mana,ta shigo taga Room hadadde yasha gyara tace gayu an sanka ba asan makwancinka ba yanzu haka dama kake Kazami ciki kake kwana,Hunaif yayi dariya tare da cewa wlh karya kike yarinya an fada miki saurayinki ne Audu me Kifi? Kayi sauri ka fito to bari na taso uban masu motsa jiki,tana shiga Dakin Irfan taga ma kamar yafi na Hunaif haduwa tafi raina Irfan knocking kawai tayi da Sallama ta shiga,Yana fesa turare ta kalleshi taga bai ma ko kalleta ba,tace Yasin da irin su Audu me kifi ne ko ubale Alquran da tuni yana kallona yana zare Ido anga mace,Irfan ya dinga dariya yace to ni ba su bane kuma kullum sai naga mata hadaddu,haka a UK wacce macece ban gani ba,idan tsirara zakiyi wlh sai naga dama zan kalleki,Zainura tace ja jiki malam shaddar kasuwa ka gani,muna matane dama can jikinsu kowa ganinsa yake,kai yanzu kaga jikina ba sai kwakwawarka ta juye ba,na kananan kwari kake gani jakan mata amma mu irinmu mun fi karfin a kallemu a wuce.