← Book details Kamarsu Ce Daya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 40 OF 80

Sashe 40

Kamarsu Ce Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Na'im yaga Gulf din Malam da ita za a je yace wannan zataje har Can? Malam yace kai Kaci gidanku Ku shiga muje,Salma da Na'im a baya,Zainura kusa da Salma a gefe,Umma tana gaba Malam shine yake Driving,Salma da Na'im basu San kowa ba amma haka Umma tace su daga musu Hannu,Salma tayi magana da karfi idan mun tunaku zamu dawo......mun gode,Zainura ma ta leka tace Aradu ni me sa'a ce Alquran zan biya muku kujerar Makkah kawayena hhhhh aka kwashe da dariya duk inda Na'im ya kai da son danne dariyarsa ina abin ya gagareshi, Zainura ta takura musu a motar da abin dariya iri iri har sunyi Nisa basu sani ba Sabo da iya shegen Zainura,Yanzu tace zata gwada Maganar Na'im yanda yayi a biki.

AsmaBaffa
[1/14, 5:14 PM] Sis Asma: 🏉KAMARSU CE DAYA🏉

111-115 116-120

Official

By
AsmaBaffa

ZULY BEAUTY,ADABIYA ISAH,MRS MUKHTAR,BIBA,RAMCY MAKEUP
Wannan page naku ne.

AUTA ina godiya Allah ya bar kauna.

Mummy tana nan yanzu ba laifi ta rage damuwa sai dai duk hirarta in dai ba zancen Na'im zakayi ba to baza ta wani saurareka ba,amma idan Na'im ne to fa ko kwana zakuyi bata gajiya,duk an ganota ma ko magana za kayi in dai kana so Mummy ta nutsu to ka fara kawo zancen Na'im kana karfafa mata gwiwa cewar za a ga Na'im zai fito yana nan a raye.
Yau ma Aisha tazo tana so Mummy ta bata kudi zata canja mota ta samu Mummy a daki ta zauna gefenta tare da cewa Mummy naji a jikina Na'im ya kusa bayyana kwana nan,Mummy ta washe baki tace ai insha'allah,Aisha tace Allah yasa yana hannun na gari,kinga dakinsa Mummy shi yasa kullum sai na gyarashi gashi kinyi tunani da aka kara canjawa dakin komai kamar Aljannar Duniya ai Bro yana dawowa za a ga Murna,Mummy tace wlh kuwa ai kin sanshi da son harkar wanka,Allah sarki Na'im dina Allah dawo min dakai lfy,Aisha tace Ameen dai Momma zamu shirya shagali ranar ai har anko da party zamuyi,suna ta hirar Na'im Mummy tana Jin dadi sai Aisha tace Mummy yawwa dan Allah tuna miki zanyi kudin motar da za a bani na Canja,kisa ya Irfan Ya min Transfer dan Allah Momma kar Na'im ya dawo ya ganni da tsohuwar mota,Mummy dadi ya kamata fa tace duk motocin gidan nan Aisha gashi duk su Irfan sun canja sababbi har na Na'im ma fa saida su akayi aka kawo sabon yayi ki dauki daya ciki,Aisha tace Mummy wannan ai sai irin su Na'im sun min girma ina mace, waya Mummy ta dauka tare da dannawa Irfan kira lallai yau ya yiwa Aisha transfer na Milyan biyar zata canja mota,Irfan yace to Mummyn Na'im zan bata.
Aisha da murna taci gaba da hirar Na'im a gaban Mummy.

Borno state dangin Salma,Maimuna matar Hashim ta samu ciki wata Uku kenan,kullum bata da lfy laulayi,amma Hashim sabo da rashin godiyar Allah irin na Hashim duk ya manta yanda Maimuna take bashi kulawa a baya,yanzu kullum fada sukeyi,abu kadan tayi masifa,sabo da baya samun yanda yake so lokacin tana Amarya duk ya manta,wulakanci iri iri yake mata,Yana kallo tana Amai amma ko surarta bazaiyi ba,
Yanzu ma yana Palo yana kallon Indian film tana waje jikin pampo tana ta sheka Amai amma ko kallo bata isheshi ba,haka ta gama da kyar jikin ta yana rawa ta wanke wajen tare da gyara jikinta, ta dan matso jikin inuwa ta kwanta a kasan wajen,sanyin kasan take so sai da ta yayyafa ruwa me sanyi a kasan simintin ta jikashi sannan ta kwanta a kai,nan kuma ta jika dankwalin Atamfarta sharaf ta lulluba dashi tana jin dadin sanyin.
Hashim sai da ya gama kallonsa ya fito ko tausayi babu ya kalleta shekeke tare da cewa kar ki bata min Siminti da Amai fa ki kiyaye ki karaci kazantarki,kazamar banza wlh aure zan kara idan na gaji kin isheni,Maimuna ta kalleshi kawai hawaye ya gangaro mata ta dauke kanta tace amma kasan ba dashi nazo ba kai ka haddasa min wlh ban taba ganin marar Imani irinka ba Hashim,ke karki kawo min raini zan tattakaki ba ruwana da wani cikinki aikin banza wata tsiya kike tsinana min,da dare cuta,rana Amai,ko yaushe cuta wanne hakkina kike sauke min,malalaciya da an tabaki kice zazzabi kike tsaki yaja yayi gaba tara da bugo murfin kofar.
Masu zaman tsakar gida dai ana ta yi kullum ba fashi ana tona asirin aure,ana siyan magunguna,masu kulle mazajensu da me dan mukulli ma suna ta fama,Ubale ya gano abinda suke masa duk ya koresu gida da saki daya daya tare da rangado sabuwar Amarya Iklima,Iklima akwai hankali da ilmi ga kula da miji bata zuwa wannan hirar ta tsakar gida sai daí idan masu tallan maganin mata sunzo ta siyi me inganci Ta tafi wajenta,
Nan matan suka Sa mata ido wai ita a dole ustaziyya har habaici ake mata,Maimuna kuma bata fita yanzu Sabo da ba lfy,aiki ma Iklima ke zuwa tana gyara mata ko ina na gidan,har girki tana dan yi mata watarana.
Su Shehu ko zancen Salma basa yi ko da wasa ma.

Affa kuwa dabbobinsa sai karewa sukeyi daya bayan daya abin yana damunsa,Ummitu har da kuka cikin shanu 60 saura 45 maimakon su godewa Allah sai su suka kara shiga bokaye cewar Salma ce ta jawo musu ayiwa dukiyarsu katanga da Salma da sauran makiya,Ummitu tace mun riki bala'i da hannunmu har yanzu sharrin yarinyar nan binmu yake yi Allah ya Isa wlh babu wanda zai jawo mana sai Salma ita ce me kashin tsiya,Affa yace bama tare ma Baza ta barmu mu huta ba ko mayyace ne? Wa ya sani ai gwara mayu da wannan yarinyar,haka dai su Affa ko me ya samesu kullum zargin Salma sukeyi su basa ganewa.

Malam yana ta tuki tuni har sunzo Tafa hanyar Abuja,nan suka tsaya za a ci abinci,Na'im yace shi bazai ci ba,Malam yace ka kiyayeni fa na fada ma ka bar ganin ka warke ba ruwana da kudinka ubanka zanci wlh gwara ma kaci,Salma ta sheke da dariya,Zainura tace yo kai me kyau tare da mu ma kaci abinci duk baka sani ba sai yanzu,to har tuwon Dawa ka lashe a cikinka bare nan wajen yan gayu,Na'im ya gallawa Zainura harara harda cewa Salma ki fadawa kawarki ba ruwanta dani, Salma tace Allah yaci abinci da Ku? Ganin basu gane ba Zainura ta dinga raina musu hankali tace to har hannun Barira ya kwace nama ya cinye,Salma ke kuma kinga wannan Ubaliye me makeken baki da zamu taho? Salma tace ae me hakora yellow Zainura tace to kinsha cin tuwo tare dashi kika nace masa sai ya baki sidinsa,Na'im ya dinga dariya yana toshe hanci,Salma harda kwalla,Zainura tace kai me Kyau Allah ne fa ya ceceka Amma ka dade kana son Hadizalo wannan wacce zamu taho tazo tana min rada,Akwo tuni suka tuno suffar Hadizalon da Zainura take Nufi,Na'im yace Oh God have mercy on me.

Malam yace kai kuzo mu tafi mana suka shiga wani dan Restaurant na tashar aka basu Sakwara da miyar Egusi,Zainura ta gyara Zama tare da cewa Malam Allah dai ya dai ya biyaka tana zuba lauma,Haka Salma ma,su Umma,Na'im sai cakala yake cike da kyankyami,haka suka gama ci aka ci gaba da tafiya,Zainura tayi bacci motar shuru kake ji,Salma ma ta kwanta a kafadar Na'im har suka karasa Abuja Lfy Na'im ya karbi tukin motar kawai ya kaisu har bakin gate din gidansu,Nan kowa ya saki baki banda Salma da Na'im duk da cewa an canja komai na gidan new design.

Na'im ne ya fita ya buga gate din tunda ba remote a hannunsa,Securities da gudu suka yanyame gate din tare da dana bindigu,Zainura har yau bacci take abinta Salma ta tasheta,tana mika da Salati tace nan ne gidan ko kuwa wajen shakatawa mukazo,Umma tace ke karfa ki damemu ki nutsu,Zainura tace Umma daga tambaya.

Securities suna ganin Na'im suka gigice da ihu da murna,wasu da gudu suka fada cikin gida wajen Su Mummy gashi anyi sa'a yau Saturday duk suna gida,Mummy suka ji ihu ana Oga Na'im a gigice suka Mike gaba daya,Securities suna Haki suka bada labari gasu can da Salma da wasu dattijai tare da yarinya sa'ar Salma wai Zainura,Mummy bata San Sanda tayi sujjada ba ta nuna farin ciki,haka su Irfan ma,sai kuwa ga Na'im ya shigo da sallama,sai Salma,sai Malam da Umma,Zainura tana baya sai kalle kalle takeyi ta rasa inda zata kalla ma,
Tana shigowa ciki ta fara taka kafar a hankali tana sanda kamar barauniya harda dukawa,tana lallabawa,Hunaif dariyar Zainura ta kamashi kamar tana taka wata Kwalaba tana gudu karta yanketa,Mummy baki har kunne tana ku shigo dan Allah,nan ta rungume Na'im da karfi tana Hawaye sosai shima Na'im haka sun dade a haka,sai Su Irfanma suka rungumeshi ana ta murna da Hawaye,Aisha ce ta karshe tace Bro mun shiga wani Hali na rashinka we missed u so Much,Mummy kullum sai tayi kuka,Malam yace to Alhmdllh komai ya zo karshe,Mummy sai lokacin tace kuyi hakuri dan Allah ku zauna,Zainura tana tsaye taki zama sai kalle kalle takeyi bata gajiya,Na'im ya kalli Zainura yace to Zauna mana,
Chapter 40 · 0% Book details