Sashe 19
Kamarsu Ce Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dada sai murnar ganinsu takeyi gaskiya gidan Dada ma me kyau ne sosai,Salma tunda suka gaisa tayi shuru abinta ta zauna ta nutsu daga Na'im sai Dada suke hirarsu bata sa musu baki, abinci da lemuka iri iri me aiki ta kawo musu Sai da Salma taci tayi nak dama ita akwai ci,kawai ciye ciyenta takeyi bakinta Bai hutawa da tauna.har dare suna gidan saida yaje masallaci yayi sallar Isha yace tazo su tafi,da sauri ta Mike dama ta gaji Dada ta bata turare da Sabulan wanka masu kyau da kamshi,tayi godiya suka dauko hanyar gida,saida ya tsaya ya siya mata kilishi da yawa yaga tana sonsa,tun a mota kuwa ta fara bude ledar tana dan yagowa tana cinyewa,yana satar kallonta sai ji yayi tace a daina kallo na,murmushi yayi Bai ce mata komai ba Driving dinsa yake ta yi, tambayarta yayi kin kuwa canja pad?sabo naga Alama Raheel din naki Bai koya miki wannan ba,ba tare da ta kalleshi ba tace sabo da shi ba dan iska bane ai,
Maimakon Na'im yaji haushi ta zageshi shine dan iskan kenan sai ma murmushi da yayi na birgewa tare da tsuke lips yaja yaji shshiiiii ni kuwa dan iska ne sabo da ina son iskanci thts y my ina ta kula mata.harara Salma ta zuba masa tace to Allah ya shiryeka,da sauri yace Ameen tare dake,dariya tayi tace ka fara iya hausa da yawa yanzu,kansa ya nuna da yatsa yace akwai ganowa( ganewa) a class 1st nake daukowa ,amma ke da gani dakika ce (,dakikiyace) Salma tace tsabar kokarina ma yaro Living things ake ce min kaje garinmu ka tambaya,ko kace wace Salma Colaboration a kasar nan za a fada ma domin na shahara na fetsara,Dariya ta kwace masa sosai a kasar wa yasanki a kasar nan in ba a kauyenku ba?,
Salma ta rike kugu a zaune tace Doctor Me Imani Na'im Alawwal,the Consilor of UK Embassy,and Also a prince, the most Handsome Arab man,he look alike with my one and Only Raheel my Heart,my soul mate.
Dariya Na'im ya kara yi sannan yace nima tsautsayi ne ya kamani ai,sai kuma wa ya sanki ba ni ba, irin su Governors,Ministers,Business men etc wanda kina fadan su a Nigeria an Sansu?ni ki daina sani ciki wa ya sanni a kasar nan? Masu kudi wanda suka yi fice nake nufi.
Salma ta sosa kai tace idan ba tsoro ba muje fadar shugaban kasa ka gani idan bamu gaisa dashi ba,Muje gidan minister of petrol a gani,karewarta wife din dan Gote kawata ce kamar yanda nake a gidanku haka nakeyi,ka tambayi Adam a zango karewar ta yan film ma sun sanni,Idan kana ji karyane aje gidan Ali Nuhu a gani mana,kai ka daina kallo na wata shuru shuru ba karamar shegiya ce ni a kasar nan ba,Salman Khan nan in kaga yanda muke wasa da dariya dashi sai kanka ya kulle,Amita batchan,su jitandara,kai kasan Sharukhan?to saida yace yana so na kar kaso kaga wulakancin dana masa, an fada ma ni ta wasa ce,bari ma na kaika wajen turawa kasan dai dan Wrestling undertaker ko? to mun dade tare tight frnd nane,Nancy ta Larabawa har yau har gobe kawata ce,Ronaldo da Messi sanda Ina Spain tare muke cin abinci,Governor na jigawa,kano,Taraba duk sun sanni.
Dariya Na'im yashata kamar cikinsa zaiyi ciwo matar da take wannan kurgumin dajin badan ma Aljaninta ba ai da baza tasan ma me akeyi a duniya ba,Na'im yace karya naki ya isheni haka pls, tace yo dama kana dan kauye me ka sani kai,kaifa dan kauye ne ni ban taba ganin kauyis irinka ba wai kamata ace na fika wayewa Allah kiyaye wlh anyi asarar kaika Uk,Salma yanda ta dage tana caccake Na'im kamar gaske,yace na dai fiki kyau ai,tace Allah sittiri bukwi inji kishiyar me doro,farinka ne kawai ya ceceka,hancinka yayi tsayi da yawa ya bataka,lips naka karami da yawa ba kyau yayi red ba wacce zata so ka,gashinka santsi zaisa a tsaneshi ma,Na'im yayi dariya ke fa na fiki manyan Ido wooo,idon naka kamar na mage abin tsoro da dare miyau miyau harda gwada kukan magen, hmm gashinki kamar dutse ba laushi,Salma ta taba na gaban goshinta tayi fari da Ido tace uhmmm laushin Bala'i wlh,kai nifa am sweet komai nawa sweet muahhh tayiwa kanta kiss,Na'im ya tintsire da dariya yace to kawo na taba da kaina naji,da sauri tace ai kana tabawa za aga bingir ka Sume sabo da laushin gashin ina bazai yuwu na karasa gawar da ba tawa ba.haka sukai tayi har suka je gida cike da nishadi.
Yau gidan Malam musa me kawo musu maganin mata tazo da kwandonta guda,nan fa a kira matan gida ko wacce ta fito harda Maimuna ta ebo dan kudinta ta fito, Hafsatu me magani tace yau fa akwai sabon Harka ta dakko wani me karfe a jiki ta daga musu sama tace kun San wannan?sukace a'a tace to me mukulli kenan,idan kina so ki kulle mijinki ko kishiya yayi miki bakya so ya sadu da ita sai ki dauko shi kice Bissmillahi na kulle mijina wane sai ki saki karfen zaice das shike nan kin kulle mijinki bazai taba Jin sha'awar kishiyarki ko wata mace ba sai ranar da zai shigo dakinki ki kara dakkowa kice bismillahi na bude wane mijina to da yazo dakinki sha'awarki kadai zai ji,amma ko neman mata yake dan Ubansa kina sa masa mukulli kin gama da shege,mata sukace heeeeeee suka saya zasu gwada,can ta dakko wani tace wannan ki karanta Fatiha kafa bakwai ki jefa a tsohuwar Rijiya ba ke ba kishiya ke dai zai makalewa sai kin dinga korarsa,ga me kunama na matsi ne shima Oga ko kurnu ne dole yaji a jikinsa,ga dan kumasa a daga a hada da zuma ayi matsi ahaf ai sai ke ko kishiya ce kece a gaba,ga Sokoto timjim, daga jin sunan ma malama Basai kin mana bayani ba ai zamu Zama timjim cewar Maimuna,nan Malama ta miko hannu suka kashe ana shewa,ta kawo turaren kwanciya a shafa a cibi,kirji,da hips da ya shaki kamshin zai rude miki nan tayi ta karanta musu wasu maganin mata ne normal wasu kuma an hada da shirka a ciki,mata a kula yanzu garin neman maganin mata har abin ya koma shirka da bin malamai,ana rubutu jikin kwai,kaza,da sauran Abubuwa da gani kasan an koma bin malamai,ko ace kar ayi amfani dashi sai za a sadu za ayi tsarki da ruwan rubutu ko alwala gasu nan iri iri ana kaucewa a fada fushin Allah,har kullum a dinga tunawa da mutuwa,baka San ranar tafiya lahira ba,ko yaushe zata iya zuwa,me zakace da Allah,haka kishiya mene abin kulla mata sharri ko wacce idan ta biya allonta ta wanke ke dai ki zage kiga ya zaki kiyi zarra wajen mijinku ba ta hanyar bokaye ba ta abinda Allah yace,duniyar nawa take har za a dinga cutar da juna ana jifan juna,wannan ya jefi wannan wannan ya jefi wancan,waccen ma haka kowa wajen malamai ana shirka a juna,tsakanin musulmi da musulmi maza mata Malamai ana kashe juna,ana kullawa juna Bala'i ya kamata wlh a kiyaye a gyara halaye, malaman nan masu bada maganin kusan yanzu duk bokayene suke fakewa suna shiga rigar malamai,ya shirya karya kamar gaske yana aji tsoron Allah idan magani yaci karki cutar dashi idan kika mallakeshi etc sai ki dauka na gaske ne baki San mashirki bane yana ta tsafi yana yiwa Allah shirka,ayi addua da kanmu mana ki tashi kiyi Zikhri wanda Allah yace,time din da ake amsa adduar bayi,Karatun Qur'an,Nafeela etc kiyi sujjada kuwa Allah kirari ki zubda hawaye kikai kukanki wajen Allah wanda kullum baya Hutu baya bacci,kullum Office din Allah a bude yake kiyi kullum ki gani idan Allah Bai saurareki ba ya amsa miki,ya baki ma abinda baki zata ba a duniya kuma nasa me dorewane,amma tsafi fa karyewa yake baya tasiri,ga fushin Allah.Allah bamu ikon gyarawa,amma da ki ba malam kudi ya miki aiki gwara kici kaza gashashiya ko ki gyara kanki da kudin gyaran jiki.
Kwana biyu Salma ta canja salon Aljanunta yawo take fita kullum ba tare da an sani ba sai dai aga bata nan,da yamma lis ta dawo ko dare,kuma idan ta fita sai ta koma mahaukaciya sosai tuburan take hauka a titi da bola,amma idan ta dawo gidan su Na'im sai a ganta fes,Na'im abin ya damesu gaba daya bashi da sukuni,tana fita yake fitowa da mota amma baya ganin inda ta shiga,Abuja kuma ba a barin mahaukata a titi,Na'im baya ganinta bare yace sai tayi Sallah ko ya mata maganin da Malam ya bashi,haka yauma ta fita ba dankwali a kanta tana ta tsince tsince a titi tana dariya ko ta bata rai,motar dake tsinto mahaukata tazo wucewa ta ganta a hanya aiko suka tsaya caraf suka kamata nan take suka buga mata Allura bacci ya tafi da ita suka jefa ta a mota sai asibitin Mahaukata na Abuja aka kai Salma suka sa mata Sarka kafafu da hannaye dasu take yawo,da ta tayar da Aljanu a maka mata Allurai,yanzu tana can cikin Uniform na mahaukata tana Shan Allurai,Na'im sati guda yaga bata dawo ba,har kauye yaje wajen su Affa ya tambaya saida Suka zageshi tas sannan suka ce bata nan,haka ma Borno yasha cin mutunci iri iri shi dai yace Jahilci ke damun su ko a jikinsa.
Cikin Abuja kullum a yawon nemanta yake lungu da sako,haka Irfan ma sai yanzu yasan ma Ashe son Salma ya kamashi da yawa Bai sani ba,
Mummy da Dada sai jimamin bacewar Salma suke sun damu kwarai,Aisha da Hunaif ma takanas suke daukan mota suyi ta zagayen nemanta layi layi amma ba alamar ta.
Maimakon Na'im yaji haushi ta zageshi shine dan iskan kenan sai ma murmushi da yayi na birgewa tare da tsuke lips yaja yaji shshiiiii ni kuwa dan iska ne sabo da ina son iskanci thts y my ina ta kula mata.harara Salma ta zuba masa tace to Allah ya shiryeka,da sauri yace Ameen tare dake,dariya tayi tace ka fara iya hausa da yawa yanzu,kansa ya nuna da yatsa yace akwai ganowa( ganewa) a class 1st nake daukowa ,amma ke da gani dakika ce (,dakikiyace) Salma tace tsabar kokarina ma yaro Living things ake ce min kaje garinmu ka tambaya,ko kace wace Salma Colaboration a kasar nan za a fada ma domin na shahara na fetsara,Dariya ta kwace masa sosai a kasar wa yasanki a kasar nan in ba a kauyenku ba?,
Salma ta rike kugu a zaune tace Doctor Me Imani Na'im Alawwal,the Consilor of UK Embassy,and Also a prince, the most Handsome Arab man,he look alike with my one and Only Raheel my Heart,my soul mate.
Dariya Na'im ya kara yi sannan yace nima tsautsayi ne ya kamani ai,sai kuma wa ya sanki ba ni ba, irin su Governors,Ministers,Business men etc wanda kina fadan su a Nigeria an Sansu?ni ki daina sani ciki wa ya sanni a kasar nan? Masu kudi wanda suka yi fice nake nufi.
Salma ta sosa kai tace idan ba tsoro ba muje fadar shugaban kasa ka gani idan bamu gaisa dashi ba,Muje gidan minister of petrol a gani,karewarta wife din dan Gote kawata ce kamar yanda nake a gidanku haka nakeyi,ka tambayi Adam a zango karewar ta yan film ma sun sanni,Idan kana ji karyane aje gidan Ali Nuhu a gani mana,kai ka daina kallo na wata shuru shuru ba karamar shegiya ce ni a kasar nan ba,Salman Khan nan in kaga yanda muke wasa da dariya dashi sai kanka ya kulle,Amita batchan,su jitandara,kai kasan Sharukhan?to saida yace yana so na kar kaso kaga wulakancin dana masa, an fada ma ni ta wasa ce,bari ma na kaika wajen turawa kasan dai dan Wrestling undertaker ko? to mun dade tare tight frnd nane,Nancy ta Larabawa har yau har gobe kawata ce,Ronaldo da Messi sanda Ina Spain tare muke cin abinci,Governor na jigawa,kano,Taraba duk sun sanni.
Dariya Na'im yashata kamar cikinsa zaiyi ciwo matar da take wannan kurgumin dajin badan ma Aljaninta ba ai da baza tasan ma me akeyi a duniya ba,Na'im yace karya naki ya isheni haka pls, tace yo dama kana dan kauye me ka sani kai,kaifa dan kauye ne ni ban taba ganin kauyis irinka ba wai kamata ace na fika wayewa Allah kiyaye wlh anyi asarar kaika Uk,Salma yanda ta dage tana caccake Na'im kamar gaske,yace na dai fiki kyau ai,tace Allah sittiri bukwi inji kishiyar me doro,farinka ne kawai ya ceceka,hancinka yayi tsayi da yawa ya bataka,lips naka karami da yawa ba kyau yayi red ba wacce zata so ka,gashinka santsi zaisa a tsaneshi ma,Na'im yayi dariya ke fa na fiki manyan Ido wooo,idon naka kamar na mage abin tsoro da dare miyau miyau harda gwada kukan magen, hmm gashinki kamar dutse ba laushi,Salma ta taba na gaban goshinta tayi fari da Ido tace uhmmm laushin Bala'i wlh,kai nifa am sweet komai nawa sweet muahhh tayiwa kanta kiss,Na'im ya tintsire da dariya yace to kawo na taba da kaina naji,da sauri tace ai kana tabawa za aga bingir ka Sume sabo da laushin gashin ina bazai yuwu na karasa gawar da ba tawa ba.haka sukai tayi har suka je gida cike da nishadi.
Yau gidan Malam musa me kawo musu maganin mata tazo da kwandonta guda,nan fa a kira matan gida ko wacce ta fito harda Maimuna ta ebo dan kudinta ta fito, Hafsatu me magani tace yau fa akwai sabon Harka ta dakko wani me karfe a jiki ta daga musu sama tace kun San wannan?sukace a'a tace to me mukulli kenan,idan kina so ki kulle mijinki ko kishiya yayi miki bakya so ya sadu da ita sai ki dauko shi kice Bissmillahi na kulle mijina wane sai ki saki karfen zaice das shike nan kin kulle mijinki bazai taba Jin sha'awar kishiyarki ko wata mace ba sai ranar da zai shigo dakinki ki kara dakkowa kice bismillahi na bude wane mijina to da yazo dakinki sha'awarki kadai zai ji,amma ko neman mata yake dan Ubansa kina sa masa mukulli kin gama da shege,mata sukace heeeeeee suka saya zasu gwada,can ta dakko wani tace wannan ki karanta Fatiha kafa bakwai ki jefa a tsohuwar Rijiya ba ke ba kishiya ke dai zai makalewa sai kin dinga korarsa,ga me kunama na matsi ne shima Oga ko kurnu ne dole yaji a jikinsa,ga dan kumasa a daga a hada da zuma ayi matsi ahaf ai sai ke ko kishiya ce kece a gaba,ga Sokoto timjim, daga jin sunan ma malama Basai kin mana bayani ba ai zamu Zama timjim cewar Maimuna,nan Malama ta miko hannu suka kashe ana shewa,ta kawo turaren kwanciya a shafa a cibi,kirji,da hips da ya shaki kamshin zai rude miki nan tayi ta karanta musu wasu maganin mata ne normal wasu kuma an hada da shirka a ciki,mata a kula yanzu garin neman maganin mata har abin ya koma shirka da bin malamai,ana rubutu jikin kwai,kaza,da sauran Abubuwa da gani kasan an koma bin malamai,ko ace kar ayi amfani dashi sai za a sadu za ayi tsarki da ruwan rubutu ko alwala gasu nan iri iri ana kaucewa a fada fushin Allah,har kullum a dinga tunawa da mutuwa,baka San ranar tafiya lahira ba,ko yaushe zata iya zuwa,me zakace da Allah,haka kishiya mene abin kulla mata sharri ko wacce idan ta biya allonta ta wanke ke dai ki zage kiga ya zaki kiyi zarra wajen mijinku ba ta hanyar bokaye ba ta abinda Allah yace,duniyar nawa take har za a dinga cutar da juna ana jifan juna,wannan ya jefi wannan wannan ya jefi wancan,waccen ma haka kowa wajen malamai ana shirka a juna,tsakanin musulmi da musulmi maza mata Malamai ana kashe juna,ana kullawa juna Bala'i ya kamata wlh a kiyaye a gyara halaye, malaman nan masu bada maganin kusan yanzu duk bokayene suke fakewa suna shiga rigar malamai,ya shirya karya kamar gaske yana aji tsoron Allah idan magani yaci karki cutar dashi idan kika mallakeshi etc sai ki dauka na gaske ne baki San mashirki bane yana ta tsafi yana yiwa Allah shirka,ayi addua da kanmu mana ki tashi kiyi Zikhri wanda Allah yace,time din da ake amsa adduar bayi,Karatun Qur'an,Nafeela etc kiyi sujjada kuwa Allah kirari ki zubda hawaye kikai kukanki wajen Allah wanda kullum baya Hutu baya bacci,kullum Office din Allah a bude yake kiyi kullum ki gani idan Allah Bai saurareki ba ya amsa miki,ya baki ma abinda baki zata ba a duniya kuma nasa me dorewane,amma tsafi fa karyewa yake baya tasiri,ga fushin Allah.Allah bamu ikon gyarawa,amma da ki ba malam kudi ya miki aiki gwara kici kaza gashashiya ko ki gyara kanki da kudin gyaran jiki.
Kwana biyu Salma ta canja salon Aljanunta yawo take fita kullum ba tare da an sani ba sai dai aga bata nan,da yamma lis ta dawo ko dare,kuma idan ta fita sai ta koma mahaukaciya sosai tuburan take hauka a titi da bola,amma idan ta dawo gidan su Na'im sai a ganta fes,Na'im abin ya damesu gaba daya bashi da sukuni,tana fita yake fitowa da mota amma baya ganin inda ta shiga,Abuja kuma ba a barin mahaukata a titi,Na'im baya ganinta bare yace sai tayi Sallah ko ya mata maganin da Malam ya bashi,haka yauma ta fita ba dankwali a kanta tana ta tsince tsince a titi tana dariya ko ta bata rai,motar dake tsinto mahaukata tazo wucewa ta ganta a hanya aiko suka tsaya caraf suka kamata nan take suka buga mata Allura bacci ya tafi da ita suka jefa ta a mota sai asibitin Mahaukata na Abuja aka kai Salma suka sa mata Sarka kafafu da hannaye dasu take yawo,da ta tayar da Aljanu a maka mata Allurai,yanzu tana can cikin Uniform na mahaukata tana Shan Allurai,Na'im sati guda yaga bata dawo ba,har kauye yaje wajen su Affa ya tambaya saida Suka zageshi tas sannan suka ce bata nan,haka ma Borno yasha cin mutunci iri iri shi dai yace Jahilci ke damun su ko a jikinsa.
Cikin Abuja kullum a yawon nemanta yake lungu da sako,haka Irfan ma sai yanzu yasan ma Ashe son Salma ya kamashi da yawa Bai sani ba,
Mummy da Dada sai jimamin bacewar Salma suke sun damu kwarai,Aisha da Hunaif ma takanas suke daukan mota suyi ta zagayen nemanta layi layi amma ba alamar ta.