Sashe 9
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Lokacin da taga text din nashi murmushi tayi tana yabawa iya kalamansa acikin zuciyarta, babu bata lokaci tatura masa address din da time din da zaizo, koba komai tana jinta da dan dama dama yau sabanin kwanakin baya da taketa fama da kunci da bacin rai, hatta amma yau ta fuskanci walwala atattare da ita amma batace da ita komai ba.
K'arfe uku na yamma kiranshi yashigo wayarta lokacin tana shiryawa bayan tafito daga wanka, tana dauka yace mata gashi yazo nan tace tana zuwa, karasa shiryawa tayi tafita ta zira flat din takalmi,fararen kujeru guda biyu na roba ta daukar musu tafita zuwa gaban part din Abba wanda ke makotaka da gate ta ajiye ta zauna, waya tayi masa tace yashigo, har yashigo bata dago ta kalleshi ba hankalinta na kan wayarta tana turawa da khulsum text sai dai kamshinsa da ya ziyarceta.
Da sallama ya isa wurinta ta amsa batare da ta dago ba, zama yayi yana yimata kallon kurulla, ashe ita din yar babbar koface bai saniba sai yau domin mahaifinta yarike mukamai daban daban domin yanzu haka shine commissioner na ruwa ajihar sannan kuma mai baiwa governor shawara ta musamman akan harkar ciyar da makarantun kasa da secondary,
Dagowa tayi ta kalleshi idonta yashiga cikin nashi nan mamaki ya cika ta domin ganin wanda ke gabanta,
Murmushi tayi,
"Sannunka da zuwa musa..."
Murmushin shima yayi,
"Yawwa barkanki dai hajjaju amma muhammadu nake ba musa ba"
"Ayya sorry namanta ne, ya aiki?"
"Alhamdulillah"
"Allah yataimaka"
"Amin"
Shiru sukayi dukkaninsu, kafin daga bisani ta danja numfashi tace,
"Dama kaine wanda ke kirana sannan yake turo min wannan massages din?"
Babu fargaba ko tsoro ya daga mata kai,
"Eh nine..."
Murmushi tayi ta maida kanta gefe,
"Haba Muhammad to ai ni ba sa'ar aurenka bace.."
"Ko menene dalili?"
"Saboda nayi maka girma ai,inada kanne twins kamarka el'ameen da elmustapha suna Sudan suna karatu"
"A'a mutukar kin amince zaki aureni toni wallahi bakiyi min wani girma ba"
Murmushi tasake yi tana kallon Rabi mai aikin amma wadda aka kawo mata kwana biyu da suka gabata domin tayata aikace aikace, ruwan roba da lemon kwali tazo ta ajiye agaban fahad sannan tatafi hakan yabaiwa bilkisu damar cigaba da fadin abinda ke ranta,
"Muhammad wallahi ni ba mate din aurenka bace, saboda ko ahaifi na girmeka sosai, ai zakaji kunyar nuna ni agidanku da wurin abokanka amatsayin mata"
"Mutukar kin amince wallahi ni babu maganar kunya, kece dai kawai zakiji kunyar nuna ni amatsayin mijinki saboda nayi miki kankanta"
Fuskarta babu yabo babu fallasa ta kalleshi babu alamun wasa tace,
"Kasan me nake so dakai? Daga yanzun nan kar ka kuskura ka kuma zuwarmun da magana makamanciyar wannan, ada banma yi niyyar sauraronka ba amma dole tasaka na saurareka sakamakon mutuncin da kayi min abaya"
Shiru yayi yana faman aikin goge screen din wayarshi da handkerchief din dake hannunshi sai zuwa can yanisa ya kalleta kadan ta kuwa sha kunu kamar bata taba dariya ba,
"Shikenan tunda haka kikace amma ni anawa rashin hankalin idan akazo kan batu na aure wasu muhimman abubuwa ake dubawa bawai maganar ka girmi mutum ko shi ya girmeka ba dan haka nidai har gobe ina nan akan bakana dan wallahi ina sonki..."
"Naji kana sona amma ni nagama fada maka ra'ayina idan kaji fine idanma bakaji ba duk daya, sai anjima"
Daga haka tamike ta wuce cikin gida cikeda takaici wannan wacce irin lalacewa ce ace yaro karami wai yazo mata da maganar aure babu ko kunya bare tsoro lallai zamani mai yayi, dakinta tashiga ta watsar da komai dake hannunta ta kwanta kan gado idonta akan tv, gaba daya ranta abace yake meyasa hamood yayi mata haka? Duk da zuciyarta na bata yakinin tayuyu akwai gagurumin abin da yafaru dashi wanda ita bata saniba....
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA...!*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*10*
*Dan Allah idan baki siyaba karki karanta....*
***Ji take kamar tafashe da kuka ko zata samu saukin damuwar dake addabarta,
"Lallai yaron nan yama raina min wayo wallahi..."
Haka tayita fada tana yin kwafa daga karshe kasa jurewa tayi har saida ta kira khulsum, khulsum na dagawa bilkisu tafara jaraba kamar khulsum din nada masaniyar abinda ke faruwa,
"Gaskiya tailor nan baida kunya wallahi saina saita masa zama"
"Wanne tailor kuma? Inji khulsum,
"Wanda yayi mana dinkunan bikinsu Hindu mana"
"Me yayi miki wai?"
"Zuwa yayi har gida wai sona yake da aure dama kuma yadade yana turo min text harda kirana awaya duk ban san shi bane dan banza,yaron da baifi su el'mustapha ba"
Khulsum najin haka me zatayi idan ba dariyaba nan tashiga kyakyatawa ita kuma bilkisu na masifa daga karshe dai kashe wayarta tayi sai lokacin taga ashe tun tuni tanada ajiyayyen sako da yashigo, cikin hanzari ta budeshi dan tana zaton ko hamood ne amma abin takaici fahad ne,
_Gimbiya kiyi hakuri na bata miki rai wanda bana farin ciki da hakan, kiyi min afuwa kuma ki gafarce ni akan abinda nayi, ni nayi zaton aure ana ginashi ne bisa yarda da amana da kuma gaskiya da kaunar juna baya ga wannan basai an hada da wani abu can waishi fin shekaru ba, ki taimaka min kiyi nazari da tunani akan maganata sannan ki sanyata a mizani na adalci kafin ki yanke hukunci, nabarki lafiya...._
Tsaki tayi ahankali marar sauti itafa yaron nan yafara takura mata kuma gaskiya, bata yi yunkurin tura masa reply ba ta shareshi taci gaba da hadiyar bacin ranta.
***
Dama fahad yasan za ayi haka yasan sai bilkisu ta raina girmansa gashi kuwa hakance tafaru amma hakan ko kadan bai karyar masa da gwiwa ba, yajima zaune a inda tatafi tabarshi yana faman zaman jiran gawon shanu daga karshe yatashi yatafi batare da yasha koda ruwan da Rabi ta ajiye masa ba. Bai sanar da kowa abinda yafaru ba domin hatta salim bai fadawa ba ubangijinsa kadai ya fadawa wanda yake da tabbacin yafishi sanin komai kuma shine zaiyi masa magani sai da yakoma gida sannan yatura mata da text daga nan yaci gaba da harkarsa shima ya shareta duk da yana son yaji daga gareta ga yar naci husna da ta sakoshi agaba kwana biyu kullum ashagon take wuni wai lallai sai ta koyi dinki awurinsa, ko ya shareta bata zuciya bare tatafi haka yake hakura suke hira.
Yau Satinta uku da komawa aiki bayan hutunta da ta cinye wanda ta dauka bayan tadawo daga aiki da yamma ammah ke yimata maganar data dan razana ta wai iyallo tace tana nan zuwa acikin satin nan gara tazo da kanta ayi maganar mudan da ita agama, kadan ta iya cin abincin da ta zubo dambun zogale da wainar shinkafa, daki ta koma ta zauna, yanzu kam yazama dole ta nemo fahad ko dan su shirya deal inyaso daga baya sai su warware, wayarta ta dauka ta tura masa text,daga nan ta wurgar da wayar saman gado tawuce bathroom.
Yana shago yana hutawa bayan yagama wasu dinkunan biki husna ta kawo masa tuwon semo miyar shuwaka amma dayake ba cin girkinta yakeba ko dandanawa baiyi ba sai su hamza ne keta kwasa yana kwance gefe yana kallonsu, wayar yazaro daga aljihunsa yaduba saboda jin sako yashigo shi duk atunaninsa ma kudinsa aka turo masa na dinkunan da yayi saboda yabawa mutanen account number dinshi amma sai yaga sako daga bilkisu tana cewa,
_Salam, yakake, kazo anjima ina son ganinka._
Murmushi yayi yamike yana tattara komatsansa domin amsa kiran gimbiya.
Saida yakoma gida yayi wanka yashirya tsaf sannan yanufi gidansu bilkisu yau kam daga waje ya tsaya ya kirata, ta kwashe kimanin mintuna goma kafin ta fito ta leko bakin gate din,yana tsaye ya jingina kafarsa da bango yana danna wayarshi,
"Bismilllah..." Tafada atakaice, bin bayanta yayi suka shiga cikin gidan inda ta tanadar musu fararen kujerun roba guda biyu. Zama sukayi ta daga kai ta kalleshi, sanye yake da blue din shadda mai kyau harda hula wacce ta saku da blue din zare amma hakan bai hana sumar kanshi bayyana ba,
Shine yakatse shirun ta hanyar cewa,
"Ina yini hajjaju?"
"Lafiya lau, kasan meyasa na kiraka?
"A'a" yafada yana girgiza kai,
"Kace kana sona zaka aureni ko?"
"Uhmm" yabata amsa,
"To nima zan aureka amma bisa wasu sharruda, kaga nafarko akwai wanda mukayi alkawarin aure dashi wanda mu duka muna son junanmu amma aka samu wata yar tangarda bama jin juna nikuma kakata ta matsawa babana akan lallai sai nayi aure acikin watanni uku kacal idan ba hakaba ta aura min wani cousin dina wanda nikuma bazan iya zaman aure dashiba,that's why nake neman taimakonka..."
"Taimakona kamar yaya?" Ya bukata yana kallonta,
"Yawwa, so nake muyi aure kamar gaske daga baya idan hamood yadawo sai mu rabu naje na auri saurayina wanda nakeso"
Murmushi yayi wanda ya bayyanar da hakoransa,
"To wannan auren namu menene sunanshi?"
"Auren taimako domin taimako na zakiyi mutukar da gasken kana kaunata"
Murmushin yasake yi,
"Gashi nikuma ban shirya aure kwana kusa ba"
"Karka damu zan baka dukkan abubuwan da za ayi amfani dashi, ni dakaina zan hada lefe inbaka akawo da komai da komai"
"Sai kace acikin shirin film ko littafin hausa? Gaskiya bazan iya wannan auren ba, da dai aure zamuyi halattacce kamar na kowa shine sai indage inyi iya bakin kokarina inga nasamo abinda zan aureki cikin watannin da kika fada amma wannan auren gaskiya ba daniba..."
Daga haka yamike yana kallon agogo,
"Ni zan wuce, nabarki lafiya"
Ya fita daga gate din gidan bata iya cemasa komai ba saboda tsananin mamaki ashe haka yake da baki da iya zance bata saniba? Ganin zaman babu amfanin da zai tsinana mata yasata tashi tashiga cikin gida, wurin ammah tawuce ta zauna anan ammah ke tambayarta waye yazo nan ta sanar da ita sabon saurayi tayi kuma dagaske yake yashirya aure, fatan alkhairi ammah tayi domin ita zabin bilkisu shine nata.
Koda ta shiga daki kasa zaune tayi ta kasa tsaye bata son damarta tawuce, ya kamata tayi amfani da wannan yaron wurin cikawa hamood burinsa,
Wayarta tajawo ta shiga kiransa, tana daf da tsinkewa yadaga,
"Hello, sorry hajjaju wanka na shigane"
"Babu komai dama na kiraka ne infada maka na amince ayi yadda kakeso din, ya kakeso ayi?"
K'arfe uku na yamma kiranshi yashigo wayarta lokacin tana shiryawa bayan tafito daga wanka, tana dauka yace mata gashi yazo nan tace tana zuwa, karasa shiryawa tayi tafita ta zira flat din takalmi,fararen kujeru guda biyu na roba ta daukar musu tafita zuwa gaban part din Abba wanda ke makotaka da gate ta ajiye ta zauna, waya tayi masa tace yashigo, har yashigo bata dago ta kalleshi ba hankalinta na kan wayarta tana turawa da khulsum text sai dai kamshinsa da ya ziyarceta.
Da sallama ya isa wurinta ta amsa batare da ta dago ba, zama yayi yana yimata kallon kurulla, ashe ita din yar babbar koface bai saniba sai yau domin mahaifinta yarike mukamai daban daban domin yanzu haka shine commissioner na ruwa ajihar sannan kuma mai baiwa governor shawara ta musamman akan harkar ciyar da makarantun kasa da secondary,
Dagowa tayi ta kalleshi idonta yashiga cikin nashi nan mamaki ya cika ta domin ganin wanda ke gabanta,
Murmushi tayi,
"Sannunka da zuwa musa..."
Murmushin shima yayi,
"Yawwa barkanki dai hajjaju amma muhammadu nake ba musa ba"
"Ayya sorry namanta ne, ya aiki?"
"Alhamdulillah"
"Allah yataimaka"
"Amin"
Shiru sukayi dukkaninsu, kafin daga bisani ta danja numfashi tace,
"Dama kaine wanda ke kirana sannan yake turo min wannan massages din?"
Babu fargaba ko tsoro ya daga mata kai,
"Eh nine..."
Murmushi tayi ta maida kanta gefe,
"Haba Muhammad to ai ni ba sa'ar aurenka bace.."
"Ko menene dalili?"
"Saboda nayi maka girma ai,inada kanne twins kamarka el'ameen da elmustapha suna Sudan suna karatu"
"A'a mutukar kin amince zaki aureni toni wallahi bakiyi min wani girma ba"
Murmushi tasake yi tana kallon Rabi mai aikin amma wadda aka kawo mata kwana biyu da suka gabata domin tayata aikace aikace, ruwan roba da lemon kwali tazo ta ajiye agaban fahad sannan tatafi hakan yabaiwa bilkisu damar cigaba da fadin abinda ke ranta,
"Muhammad wallahi ni ba mate din aurenka bace, saboda ko ahaifi na girmeka sosai, ai zakaji kunyar nuna ni agidanku da wurin abokanka amatsayin mata"
"Mutukar kin amince wallahi ni babu maganar kunya, kece dai kawai zakiji kunyar nuna ni amatsayin mijinki saboda nayi miki kankanta"
Fuskarta babu yabo babu fallasa ta kalleshi babu alamun wasa tace,
"Kasan me nake so dakai? Daga yanzun nan kar ka kuskura ka kuma zuwarmun da magana makamanciyar wannan, ada banma yi niyyar sauraronka ba amma dole tasaka na saurareka sakamakon mutuncin da kayi min abaya"
Shiru yayi yana faman aikin goge screen din wayarshi da handkerchief din dake hannunshi sai zuwa can yanisa ya kalleta kadan ta kuwa sha kunu kamar bata taba dariya ba,
"Shikenan tunda haka kikace amma ni anawa rashin hankalin idan akazo kan batu na aure wasu muhimman abubuwa ake dubawa bawai maganar ka girmi mutum ko shi ya girmeka ba dan haka nidai har gobe ina nan akan bakana dan wallahi ina sonki..."
"Naji kana sona amma ni nagama fada maka ra'ayina idan kaji fine idanma bakaji ba duk daya, sai anjima"
Daga haka tamike ta wuce cikin gida cikeda takaici wannan wacce irin lalacewa ce ace yaro karami wai yazo mata da maganar aure babu ko kunya bare tsoro lallai zamani mai yayi, dakinta tashiga ta watsar da komai dake hannunta ta kwanta kan gado idonta akan tv, gaba daya ranta abace yake meyasa hamood yayi mata haka? Duk da zuciyarta na bata yakinin tayuyu akwai gagurumin abin da yafaru dashi wanda ita bata saniba....
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA...!*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*10*
*Dan Allah idan baki siyaba karki karanta....*
***Ji take kamar tafashe da kuka ko zata samu saukin damuwar dake addabarta,
"Lallai yaron nan yama raina min wayo wallahi..."
Haka tayita fada tana yin kwafa daga karshe kasa jurewa tayi har saida ta kira khulsum, khulsum na dagawa bilkisu tafara jaraba kamar khulsum din nada masaniyar abinda ke faruwa,
"Gaskiya tailor nan baida kunya wallahi saina saita masa zama"
"Wanne tailor kuma? Inji khulsum,
"Wanda yayi mana dinkunan bikinsu Hindu mana"
"Me yayi miki wai?"
"Zuwa yayi har gida wai sona yake da aure dama kuma yadade yana turo min text harda kirana awaya duk ban san shi bane dan banza,yaron da baifi su el'mustapha ba"
Khulsum najin haka me zatayi idan ba dariyaba nan tashiga kyakyatawa ita kuma bilkisu na masifa daga karshe dai kashe wayarta tayi sai lokacin taga ashe tun tuni tanada ajiyayyen sako da yashigo, cikin hanzari ta budeshi dan tana zaton ko hamood ne amma abin takaici fahad ne,
_Gimbiya kiyi hakuri na bata miki rai wanda bana farin ciki da hakan, kiyi min afuwa kuma ki gafarce ni akan abinda nayi, ni nayi zaton aure ana ginashi ne bisa yarda da amana da kuma gaskiya da kaunar juna baya ga wannan basai an hada da wani abu can waishi fin shekaru ba, ki taimaka min kiyi nazari da tunani akan maganata sannan ki sanyata a mizani na adalci kafin ki yanke hukunci, nabarki lafiya...._
Tsaki tayi ahankali marar sauti itafa yaron nan yafara takura mata kuma gaskiya, bata yi yunkurin tura masa reply ba ta shareshi taci gaba da hadiyar bacin ranta.
***
Dama fahad yasan za ayi haka yasan sai bilkisu ta raina girmansa gashi kuwa hakance tafaru amma hakan ko kadan bai karyar masa da gwiwa ba, yajima zaune a inda tatafi tabarshi yana faman zaman jiran gawon shanu daga karshe yatashi yatafi batare da yasha koda ruwan da Rabi ta ajiye masa ba. Bai sanar da kowa abinda yafaru ba domin hatta salim bai fadawa ba ubangijinsa kadai ya fadawa wanda yake da tabbacin yafishi sanin komai kuma shine zaiyi masa magani sai da yakoma gida sannan yatura mata da text daga nan yaci gaba da harkarsa shima ya shareta duk da yana son yaji daga gareta ga yar naci husna da ta sakoshi agaba kwana biyu kullum ashagon take wuni wai lallai sai ta koyi dinki awurinsa, ko ya shareta bata zuciya bare tatafi haka yake hakura suke hira.
Yau Satinta uku da komawa aiki bayan hutunta da ta cinye wanda ta dauka bayan tadawo daga aiki da yamma ammah ke yimata maganar data dan razana ta wai iyallo tace tana nan zuwa acikin satin nan gara tazo da kanta ayi maganar mudan da ita agama, kadan ta iya cin abincin da ta zubo dambun zogale da wainar shinkafa, daki ta koma ta zauna, yanzu kam yazama dole ta nemo fahad ko dan su shirya deal inyaso daga baya sai su warware, wayarta ta dauka ta tura masa text,daga nan ta wurgar da wayar saman gado tawuce bathroom.
Yana shago yana hutawa bayan yagama wasu dinkunan biki husna ta kawo masa tuwon semo miyar shuwaka amma dayake ba cin girkinta yakeba ko dandanawa baiyi ba sai su hamza ne keta kwasa yana kwance gefe yana kallonsu, wayar yazaro daga aljihunsa yaduba saboda jin sako yashigo shi duk atunaninsa ma kudinsa aka turo masa na dinkunan da yayi saboda yabawa mutanen account number dinshi amma sai yaga sako daga bilkisu tana cewa,
_Salam, yakake, kazo anjima ina son ganinka._
Murmushi yayi yamike yana tattara komatsansa domin amsa kiran gimbiya.
Saida yakoma gida yayi wanka yashirya tsaf sannan yanufi gidansu bilkisu yau kam daga waje ya tsaya ya kirata, ta kwashe kimanin mintuna goma kafin ta fito ta leko bakin gate din,yana tsaye ya jingina kafarsa da bango yana danna wayarshi,
"Bismilllah..." Tafada atakaice, bin bayanta yayi suka shiga cikin gidan inda ta tanadar musu fararen kujerun roba guda biyu. Zama sukayi ta daga kai ta kalleshi, sanye yake da blue din shadda mai kyau harda hula wacce ta saku da blue din zare amma hakan bai hana sumar kanshi bayyana ba,
Shine yakatse shirun ta hanyar cewa,
"Ina yini hajjaju?"
"Lafiya lau, kasan meyasa na kiraka?
"A'a" yafada yana girgiza kai,
"Kace kana sona zaka aureni ko?"
"Uhmm" yabata amsa,
"To nima zan aureka amma bisa wasu sharruda, kaga nafarko akwai wanda mukayi alkawarin aure dashi wanda mu duka muna son junanmu amma aka samu wata yar tangarda bama jin juna nikuma kakata ta matsawa babana akan lallai sai nayi aure acikin watanni uku kacal idan ba hakaba ta aura min wani cousin dina wanda nikuma bazan iya zaman aure dashiba,that's why nake neman taimakonka..."
"Taimakona kamar yaya?" Ya bukata yana kallonta,
"Yawwa, so nake muyi aure kamar gaske daga baya idan hamood yadawo sai mu rabu naje na auri saurayina wanda nakeso"
Murmushi yayi wanda ya bayyanar da hakoransa,
"To wannan auren namu menene sunanshi?"
"Auren taimako domin taimako na zakiyi mutukar da gasken kana kaunata"
Murmushin yasake yi,
"Gashi nikuma ban shirya aure kwana kusa ba"
"Karka damu zan baka dukkan abubuwan da za ayi amfani dashi, ni dakaina zan hada lefe inbaka akawo da komai da komai"
"Sai kace acikin shirin film ko littafin hausa? Gaskiya bazan iya wannan auren ba, da dai aure zamuyi halattacce kamar na kowa shine sai indage inyi iya bakin kokarina inga nasamo abinda zan aureki cikin watannin da kika fada amma wannan auren gaskiya ba daniba..."
Daga haka yamike yana kallon agogo,
"Ni zan wuce, nabarki lafiya"
Ya fita daga gate din gidan bata iya cemasa komai ba saboda tsananin mamaki ashe haka yake da baki da iya zance bata saniba? Ganin zaman babu amfanin da zai tsinana mata yasata tashi tashiga cikin gida, wurin ammah tawuce ta zauna anan ammah ke tambayarta waye yazo nan ta sanar da ita sabon saurayi tayi kuma dagaske yake yashirya aure, fatan alkhairi ammah tayi domin ita zabin bilkisu shine nata.
Koda ta shiga daki kasa zaune tayi ta kasa tsaye bata son damarta tawuce, ya kamata tayi amfani da wannan yaron wurin cikawa hamood burinsa,
Wayarta tajawo ta shiga kiransa, tana daf da tsinkewa yadaga,
"Hello, sorry hajjaju wanka na shigane"
"Babu komai dama na kiraka ne infada maka na amince ayi yadda kakeso din, ya kakeso ayi?"