Sashe 51
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bilkisu tafada cikin fushi, dariya khulsum tayi taci gaba da tsokanarta, duk yadda sukaso ta gyara kanta da jikinta ki tayi ita kuwa dama ammah bata kulaba tunda tasan rashin yin kitso da lallen bashi zai hana ta tare dinba. Shima fahad bai sake nemanta ba tun lokacin da ya kirata taki dagawa, yasan fushi takeyi saboda yace tare zasu zauna da husnah shi kanshi idan son samune zaifi son ace kowa da wajenta to amma ai baida karfin rike gida biyu shiyasa lokacin da yasamu ayiyah da maganar tace a'a karma yafara saboda bazai iyaba, itama husnan yasanar da ita tare zasu zauna da Bilkisu saboda gara tasani tun yanzu domin so yake Bilkisu tana tarewa yatura asaka musu rana da ita domin shi ya Abba yake jira shima yagama shirinsa tsaf kawai sa ranane yarage. Ranar da su maama suka yi jere agidan ya kwana adakin Bilkisu kuma akan gadonta, kawai tunani yayita yi acikin ransa yana sake jinjina girman ubangiji saboda gashi cikin iyawarsa da hikimarsa yasake dawo masa da Bilkisu akaro na biyu,
"Hmmmm ko yanzu wanne irin zama kuma zamuyi oho... M" haka yaketa maimaitawa acikin ranshi. Ranar laraba da daddare aka raka Bilkisu gidanta tun amota iyallo take zuba ruwan fada tana cewa wannan amarya akwai shashasha shine ko dan sunkuben lallen nan bata kunsa ba bare tayi kitso? Ita dai Bilkisu najinta batayi ko da tariba har suka karasa gidan inda su anty kubra dasu anty asabe ke zaune suna zaman jiransu, babu Wanda yakara koda mintuna goma acikin gidan duk tafiya sukayi lokaci guda kamar ana korarsu,yaye mayafinta tayi bayan tafiyarsu tana kallon dakinta wannan karon komai blue ne amma furnitures dinta farine tass kirar royal, bata bukatar sake fita koda falo saboda bacci take son tayi tahuta amma kuma bata son wannan dan rainin wayon yazo ya isketa tana bacci saboda jikinta na bata komai na iya faruwa.
Sai dai abinda bata saniba shine fahad yashirya zamansu yanda zai kasance, sam bazasu yi zama irin nada ba yanzu yanaji aranshi lokacin shine yazo shima, awanccan zaman Bilkisu tayi yadda takeso to yanzu shima shine zaiyi yadda yakeso shiyasa lokacin da yadawo ma bai ko shiga dakinta ba yawuce daya dakin wanda kayansa naciki dama wanka yayi yashirya cikin kayan bacci masu taushi yayi kwanciyarsa babu jimawa bacci yayi gaba dashi,Bilkisu nata jiran shigowarsa shiru shiru har tagaji da saurare tayi bacci ba ita tatashi ba sai asubah, tana kan gadon tana niyyar saukowa taji yana yimata knocking,
"Kitashi lokacin salla yayi..."
Daga haka taji shiru alamar yabar wurin, sake kwanciyarta tayi bayan tayi salla ba ita tasake tashiba sai 10 saura wannan dinma karar wayarta ne yatada ta,tsaki tayi sakamakon ganin khulsum ce me kiran nata,
"Labour har yanzu ba awartsake bane? Ko dai sai nazo ne?"
"Uwar me zakizo kiyi min? Wallahi khulsum zan ramane..."
"Shikenan sai nazo din to"
Katse wayar tayi tana hamma saboda yunwa da kuma sauran bacci baccin dake kanta, wanka tashiga tayi tafito ta shirya tsaf cikin doguwar riga ta atamfa coffee colour sai dison yellow yellow ajiki, batayi kwalliya ba dan kawai powder tashafa sai kwalli ta fita falo, dama kayan abinci tasan babu matsala domin wannan karonma kamar waccan abba ya ajiye musu komai cikin store, afalo taganshi kwance daga shi sai three quarter da yar t shirt, yana kwance kan three sitter yana lallatsa waya, kanta ta dauke kamar bata ganshiba shima haka domin yasan awannan shegen son girman nata bazata yimasa magana ba saboda jira take ya gaidata tukun, harda wani dan bata rai yayi sai kace shine babba koda yake shima yanzun jin kansa yake a babba tunda shi yake aurenta ba itace take aurenshi ba dan haka yazama tilas tayi respecting dinshi a matsayinshi na mijinta, maganar hakkinshi kuwa dama shi yanzu ba ta wannan yakeyi ba saboda aduk lokacin da yatuna cewar ta auri wani yayi tarayya da ita sai yaji baya sha'awar abun, gaba daya abun yafice masa akai saboda yatsani hamood dinnan tsana mai tsanani. Kitchen tawuce domin taga kayan tea akan table,tana neman cattle tajiyo buga gida, duk haushi yabi yakamata sakamakon rashin gaishetan da fahad baiyiba,
Fitowa tayi daga kitchen din dan ganin suwaye, daidai lokacin da su mariya suka shigo dauke da kuloli akansu fahad yana biye dasu, nunata yayi yana cewa,
"Maza ku kai mata gata can"
Nufarta sukayi suna fara'a babu shiri itama tasaki fuskarta tana yimusu murmushi gamida karbar kayan dake kansu, maryam tariko kular wainar shinkafa ita kuma maryama tariko kular miyar agushi, anty Fauziyya ce tashiryo musu wannan wainar ta musamman domin ta hutar da amarya girkin safe, fahad baiko kalleta ba yawuce dayan bedroom din wanda ke gefen nata amma akwai dan tazara kadan,
Tare ta hada musu tea din dasu Maryam suka karya, ba karamin dadi taji wainar nan tayi mata ba wannan dalilinne ma yasata zagewa taci wainar sosai tana korawa da ruwan tea, daga nan falo suka tarkata suka koma ta kunna musu kallo har lokacin fahad bai fitoba ko breakfast dinma shi bai fito yayiba har 12 saura. Misalin karfe daya saura mintuna biyar ya Abba yakawo musu abincin rana, su maryama ne suka shigo da abincin amma shi ko shigowa baiyiba yadai ce agaidata, yanzunma tare suka ci abincin ranan shinkafa da miya da salad, bayan sun gama tawuce dakinta domin lokacin salla yayi, wanka tayi tai alwala tafito tashirya tana ta mitar shine babu wanda yazo mata yau wato har khulsum dinma da take cewa zatazo shine itama tayi zamanta ko leke, da abin sallarta tafita ahannu da hijabinta wurinsu maryama, tunda tashiga falon kamshi yacika kofofin hancinta wanda ko ba afada mata ba tasan na dan mulkinne saboda da alama yau da mulki yatashi da nuna isa,
"Anty ya fahad yanzu yafita yace lallai lallai muna yin salla mutafi gida saboda zamuje islamiyyar yamma..."
"Ba yau alhamis ba, har yau kunayin islamiyyar ne?" Tafada tana kokarin shimfida rug din sallar,
"Ehh munayi ranar juma'a ne kawai ba azuwa yanzu..." Maryama tabata amsa,
"Ok, fahad din yaci abincine?" Tayi tambayar da ita kanta bata san daliliba,
"A'a baiciba" suka hada baki wurin amsawa,
Sallarta ta tayar batare da ta kara magana ba, bayan ta idar tatashi tawuce daki tana ninke hijabinta tabarsu maryama afalo suma suna yin sallar, rasa abinda zata bawa yaran tayi daga karshe ta dauko wata atamfarta wadda matar abokin abba ta aiko mata da kyautarta lokacin da tana gida amma bata dinkaba,saida ta wahala kafin tanemo ledar da zata saka musu aciki, da atamfar da dari biyar tabasu sukayi mata sallama suka tafi, wayarta ta dauka tana latsawa amma kuma can kasan ranta tunani takeyi, wato wannan yaron dan rainin wayo ya karo wulakanci shine harda wani ficewa baiko fada mataba? Ohh sai yanzu tagano dalilin dayasa jiya baiko shiga dakinta ba, wato irin zaman da ya zaba musu kenan ahalin yanzu? To azuba agani zataga tsakaninsu wanda zai sauko yabi daya........
*_Ummi Shatu_*
*Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
48***Kawai tana zaune ne amma bawai dan tana jin dadin zaman ba, tunani ne fal ranta wanda mafi yawa na wulakancin fahad ne atoh wulakanci mana ita aganinta ai wannan wulakancine wato ahaka yake son yakawo wata gidan ya ajiye alhali ita baya girmamata?
"Wanne girma zai baki tunda yace ke matar sadaka ce...." Zuciyarta tabata amsa a sirrance,
Tabbas ko tantama batayi wannan shine dalilin da yasa yanzu baya rawar kafa akanta tunda ita matar sadaka ce ba matar so ba, kamar zatayi kuka takeji sauki daya tasamu shine su elmustapha sun kirata awaya sun shafe dogon lokaci suna hira cikin barkwanci. Tana nan zaune har daf da magriba lokacin ne fahad yadawo yana rikeda bakar leda wadda yasiyo fruits aciki dayake yau yana azumi itama husnah tanayi kawai bayaso yasawa husnah zargi ko mummunan tunani akan Bilkisu shiyasa baije wurinta sunsha ruwa tareba kamar yadda suka saba, yasan muddin yaje yasha ruwa awurinta yau to zata raina Bilkisu ko kuma taki ganinta da kima shikuma bazai so hakanba.
D'an bata rai tayi lokacin da yashigo cikin falon ganin haka yasa shima ya dan tsare gida kadan yawuce can saman dining yana sanye da shadda kalar ruwan shanshanbale, amma babu hula akanshi, ganin bai kulata ba yasata mikewa cikeda takaici tawuce bedroom dinta nan yabi bayanta da kallo yana girgiza kai,
"Hajjaju kenan.... Kina wahalar da zuciyata fa.... Kina azabtar dani" yafada acikin zuciyarsa, saida yasha ruwan tea da fruits sannan yaje yayi salla, tsintar kansa yayi da yin addu'ar Allah yasaka sonshi azuciyar Bilkisu kamar yadda shima yake sonta. Tunda tashiga daki tsabar takaici bata sake fitowa ba kawai mamakin fahad takeyi, to meyake nufi? Wannan tambayar tayiwa kanta tafi sau goma amma bata da amsarta, fahad kam har yasha ruwansa yagama yafita sallar ishah baiga Bilkisu tasake fitowa ba, shima ana idar da salla yadawo gida, daki yawuce ya dan kishingida yana kallo a laptop dinshi gefe daya kuma yana dan taba chat da friends, shi kadai yaketa dariya sakamakon hirar da sukeyi da su mukhty, sun sakashi agaba sai tsokanarshi suke suna cewa sai yafada musu yadda al'amarin ya kasance dariya kawai yaketa tura musu da gwalo yaki yayi magana shine bash yake cewa kai ku rabu dashi ai dama mijin hajiya ne kila ta gwabeshi akan yayi shiru kar yafada mana,wannan maganarce tabashi dariya wai mijin hajiya,har lokacin bacci yayi Bilkisu ta kwanta bata kara ganin keyarshi ba yauma haka tayita raba ido ko zai shigo amma shiru. Washe gari ita da kanta ta hada breakfast mai sauki tana falo tana karyawa yafito yanata shan kamshi kamar bai iya dariya ba,
Wuceta yayi zuwa kan table yazauna shima yafara karyawa abunda yasake kona ranta kenan yasata mikewa takoma bedroom tabar masa falon gaba daya, tana zaune gefen gado da system akan cinyarta saboda nanda kwana biyu zata koma aiki dama sati daya aka bata kawai taji yana knocking abakin kofa,
"Yes..." Yafada atakaice, bude kofar yayi ya dan leko kansa ciki batare da yashigo ba yace,
"Ki duba store koda akwai abunda babu wanda kike bukata saiki rubuta fita zanyi...."
Batare da ta kalleshi ba tace,
"Kayan miya zaka siyo kadai...."
"Hmmmm ko yanzu wanne irin zama kuma zamuyi oho... M" haka yaketa maimaitawa acikin ranshi. Ranar laraba da daddare aka raka Bilkisu gidanta tun amota iyallo take zuba ruwan fada tana cewa wannan amarya akwai shashasha shine ko dan sunkuben lallen nan bata kunsa ba bare tayi kitso? Ita dai Bilkisu najinta batayi ko da tariba har suka karasa gidan inda su anty kubra dasu anty asabe ke zaune suna zaman jiransu, babu Wanda yakara koda mintuna goma acikin gidan duk tafiya sukayi lokaci guda kamar ana korarsu,yaye mayafinta tayi bayan tafiyarsu tana kallon dakinta wannan karon komai blue ne amma furnitures dinta farine tass kirar royal, bata bukatar sake fita koda falo saboda bacci take son tayi tahuta amma kuma bata son wannan dan rainin wayon yazo ya isketa tana bacci saboda jikinta na bata komai na iya faruwa.
Sai dai abinda bata saniba shine fahad yashirya zamansu yanda zai kasance, sam bazasu yi zama irin nada ba yanzu yanaji aranshi lokacin shine yazo shima, awanccan zaman Bilkisu tayi yadda takeso to yanzu shima shine zaiyi yadda yakeso shiyasa lokacin da yadawo ma bai ko shiga dakinta ba yawuce daya dakin wanda kayansa naciki dama wanka yayi yashirya cikin kayan bacci masu taushi yayi kwanciyarsa babu jimawa bacci yayi gaba dashi,Bilkisu nata jiran shigowarsa shiru shiru har tagaji da saurare tayi bacci ba ita tatashi ba sai asubah, tana kan gadon tana niyyar saukowa taji yana yimata knocking,
"Kitashi lokacin salla yayi..."
Daga haka taji shiru alamar yabar wurin, sake kwanciyarta tayi bayan tayi salla ba ita tasake tashiba sai 10 saura wannan dinma karar wayarta ne yatada ta,tsaki tayi sakamakon ganin khulsum ce me kiran nata,
"Labour har yanzu ba awartsake bane? Ko dai sai nazo ne?"
"Uwar me zakizo kiyi min? Wallahi khulsum zan ramane..."
"Shikenan sai nazo din to"
Katse wayar tayi tana hamma saboda yunwa da kuma sauran bacci baccin dake kanta, wanka tashiga tayi tafito ta shirya tsaf cikin doguwar riga ta atamfa coffee colour sai dison yellow yellow ajiki, batayi kwalliya ba dan kawai powder tashafa sai kwalli ta fita falo, dama kayan abinci tasan babu matsala domin wannan karonma kamar waccan abba ya ajiye musu komai cikin store, afalo taganshi kwance daga shi sai three quarter da yar t shirt, yana kwance kan three sitter yana lallatsa waya, kanta ta dauke kamar bata ganshiba shima haka domin yasan awannan shegen son girman nata bazata yimasa magana ba saboda jira take ya gaidata tukun, harda wani dan bata rai yayi sai kace shine babba koda yake shima yanzun jin kansa yake a babba tunda shi yake aurenta ba itace take aurenshi ba dan haka yazama tilas tayi respecting dinshi a matsayinshi na mijinta, maganar hakkinshi kuwa dama shi yanzu ba ta wannan yakeyi ba saboda aduk lokacin da yatuna cewar ta auri wani yayi tarayya da ita sai yaji baya sha'awar abun, gaba daya abun yafice masa akai saboda yatsani hamood dinnan tsana mai tsanani. Kitchen tawuce domin taga kayan tea akan table,tana neman cattle tajiyo buga gida, duk haushi yabi yakamata sakamakon rashin gaishetan da fahad baiyiba,
Fitowa tayi daga kitchen din dan ganin suwaye, daidai lokacin da su mariya suka shigo dauke da kuloli akansu fahad yana biye dasu, nunata yayi yana cewa,
"Maza ku kai mata gata can"
Nufarta sukayi suna fara'a babu shiri itama tasaki fuskarta tana yimusu murmushi gamida karbar kayan dake kansu, maryam tariko kular wainar shinkafa ita kuma maryama tariko kular miyar agushi, anty Fauziyya ce tashiryo musu wannan wainar ta musamman domin ta hutar da amarya girkin safe, fahad baiko kalleta ba yawuce dayan bedroom din wanda ke gefen nata amma akwai dan tazara kadan,
Tare ta hada musu tea din dasu Maryam suka karya, ba karamin dadi taji wainar nan tayi mata ba wannan dalilinne ma yasata zagewa taci wainar sosai tana korawa da ruwan tea, daga nan falo suka tarkata suka koma ta kunna musu kallo har lokacin fahad bai fitoba ko breakfast dinma shi bai fito yayiba har 12 saura. Misalin karfe daya saura mintuna biyar ya Abba yakawo musu abincin rana, su maryama ne suka shigo da abincin amma shi ko shigowa baiyiba yadai ce agaidata, yanzunma tare suka ci abincin ranan shinkafa da miya da salad, bayan sun gama tawuce dakinta domin lokacin salla yayi, wanka tayi tai alwala tafito tashirya tana ta mitar shine babu wanda yazo mata yau wato har khulsum dinma da take cewa zatazo shine itama tayi zamanta ko leke, da abin sallarta tafita ahannu da hijabinta wurinsu maryama, tunda tashiga falon kamshi yacika kofofin hancinta wanda ko ba afada mata ba tasan na dan mulkinne saboda da alama yau da mulki yatashi da nuna isa,
"Anty ya fahad yanzu yafita yace lallai lallai muna yin salla mutafi gida saboda zamuje islamiyyar yamma..."
"Ba yau alhamis ba, har yau kunayin islamiyyar ne?" Tafada tana kokarin shimfida rug din sallar,
"Ehh munayi ranar juma'a ne kawai ba azuwa yanzu..." Maryama tabata amsa,
"Ok, fahad din yaci abincine?" Tayi tambayar da ita kanta bata san daliliba,
"A'a baiciba" suka hada baki wurin amsawa,
Sallarta ta tayar batare da ta kara magana ba, bayan ta idar tatashi tawuce daki tana ninke hijabinta tabarsu maryama afalo suma suna yin sallar, rasa abinda zata bawa yaran tayi daga karshe ta dauko wata atamfarta wadda matar abokin abba ta aiko mata da kyautarta lokacin da tana gida amma bata dinkaba,saida ta wahala kafin tanemo ledar da zata saka musu aciki, da atamfar da dari biyar tabasu sukayi mata sallama suka tafi, wayarta ta dauka tana latsawa amma kuma can kasan ranta tunani takeyi, wato wannan yaron dan rainin wayo ya karo wulakanci shine harda wani ficewa baiko fada mataba? Ohh sai yanzu tagano dalilin dayasa jiya baiko shiga dakinta ba, wato irin zaman da ya zaba musu kenan ahalin yanzu? To azuba agani zataga tsakaninsu wanda zai sauko yabi daya........
*_Ummi Shatu_*
*Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
48***Kawai tana zaune ne amma bawai dan tana jin dadin zaman ba, tunani ne fal ranta wanda mafi yawa na wulakancin fahad ne atoh wulakanci mana ita aganinta ai wannan wulakancine wato ahaka yake son yakawo wata gidan ya ajiye alhali ita baya girmamata?
"Wanne girma zai baki tunda yace ke matar sadaka ce...." Zuciyarta tabata amsa a sirrance,
Tabbas ko tantama batayi wannan shine dalilin da yasa yanzu baya rawar kafa akanta tunda ita matar sadaka ce ba matar so ba, kamar zatayi kuka takeji sauki daya tasamu shine su elmustapha sun kirata awaya sun shafe dogon lokaci suna hira cikin barkwanci. Tana nan zaune har daf da magriba lokacin ne fahad yadawo yana rikeda bakar leda wadda yasiyo fruits aciki dayake yau yana azumi itama husnah tanayi kawai bayaso yasawa husnah zargi ko mummunan tunani akan Bilkisu shiyasa baije wurinta sunsha ruwa tareba kamar yadda suka saba, yasan muddin yaje yasha ruwa awurinta yau to zata raina Bilkisu ko kuma taki ganinta da kima shikuma bazai so hakanba.
D'an bata rai tayi lokacin da yashigo cikin falon ganin haka yasa shima ya dan tsare gida kadan yawuce can saman dining yana sanye da shadda kalar ruwan shanshanbale, amma babu hula akanshi, ganin bai kulata ba yasata mikewa cikeda takaici tawuce bedroom dinta nan yabi bayanta da kallo yana girgiza kai,
"Hajjaju kenan.... Kina wahalar da zuciyata fa.... Kina azabtar dani" yafada acikin zuciyarsa, saida yasha ruwan tea da fruits sannan yaje yayi salla, tsintar kansa yayi da yin addu'ar Allah yasaka sonshi azuciyar Bilkisu kamar yadda shima yake sonta. Tunda tashiga daki tsabar takaici bata sake fitowa ba kawai mamakin fahad takeyi, to meyake nufi? Wannan tambayar tayiwa kanta tafi sau goma amma bata da amsarta, fahad kam har yasha ruwansa yagama yafita sallar ishah baiga Bilkisu tasake fitowa ba, shima ana idar da salla yadawo gida, daki yawuce ya dan kishingida yana kallo a laptop dinshi gefe daya kuma yana dan taba chat da friends, shi kadai yaketa dariya sakamakon hirar da sukeyi da su mukhty, sun sakashi agaba sai tsokanarshi suke suna cewa sai yafada musu yadda al'amarin ya kasance dariya kawai yaketa tura musu da gwalo yaki yayi magana shine bash yake cewa kai ku rabu dashi ai dama mijin hajiya ne kila ta gwabeshi akan yayi shiru kar yafada mana,wannan maganarce tabashi dariya wai mijin hajiya,har lokacin bacci yayi Bilkisu ta kwanta bata kara ganin keyarshi ba yauma haka tayita raba ido ko zai shigo amma shiru. Washe gari ita da kanta ta hada breakfast mai sauki tana falo tana karyawa yafito yanata shan kamshi kamar bai iya dariya ba,
Wuceta yayi zuwa kan table yazauna shima yafara karyawa abunda yasake kona ranta kenan yasata mikewa takoma bedroom tabar masa falon gaba daya, tana zaune gefen gado da system akan cinyarta saboda nanda kwana biyu zata koma aiki dama sati daya aka bata kawai taji yana knocking abakin kofa,
"Yes..." Yafada atakaice, bude kofar yayi ya dan leko kansa ciki batare da yashigo ba yace,
"Ki duba store koda akwai abunda babu wanda kike bukata saiki rubuta fita zanyi...."
Batare da ta kalleshi ba tace,
"Kayan miya zaka siyo kadai...."