Sashe 32
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shiru fahad yayi masa domin shi kadai yasan abinda yakeji, haka yayita murkususu har zuwa dare danma tare da salim din yanzu suke kwana, karfe 9 nadare a asibiti tayi musu saboda tsananin da jikin fahad yayi wani zazzafan zazzabine ya mamayeshi inbanda karkarwa babu abinda jikinsa keyi ga ciwon kirji dake barazanar tarwatsa mata hakarkari wannan dalilinne yasa su baba kaishi asibiti shida salim, babu bata lokaci aka bashi gado nan aka shiga kara masa ruwa babu ji bare gani saboda jikinsa yagama galabaita sosai.......
*Idan har kin san baki biya ba kiyiwa kanki adalci nima kiyi min karki karanta.*
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*KAMAR DA WASA...!*
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*29*
***Tunda aka kai fahad asibiti yake cikin mawuyacin hali gaba daya bai san a inda yakeba bare yasan wanda ke kansa, babban likitan da yake dubashi sai faman fada yake tayiwa su baba yana cewa ya za ayi abar karamin yaro kamar fahad yakamu da ciwon hawan jini wanda ke barazanar taba kwakwalwarsa da lafiyar jikinsa? Domin acewar likitan Allah ne kadai ya takaita abun aka kawoshi asibiti dawuri amma da ace ba akawoshi tun wuriba to irin wannan ne kesawa mutum yana tsaka da tafiya ya yanke jiki yafadi shikenan yahadu da babbar lalura dan haka yazama dole asan yanda za ayi yanisanta kansa da damuwa da yawan tunani domin jininsa yayi masifar hawa hawan da ba aso dan haka yanzu dole akan magani zasu dorashi domin lalurar ta rigada ta kamashi. Daga ayiyah har mamuh kuka suke yi jin wai dan karamin dansu yahadu da cutar zamani ta hawan jini tunda ko su da suke tsoffi basu gamu da irin wannan ciwonba lallai wannan jarraba ce daga Allah, kullum a asibitin suke wuni suna kula da fahad, salim da ya Abba wanda yazo gida saboda dan break din da suka samu na good friday Easter monday, suke kwana awurin fahad sannan suna kula dashi, husnah ma kusan kullum sai tazo asibitin ta dubashi wani lokacin ma har girki take iyo masa, shi dai fahad tunda yafara bude ido dishi dishi yake kallon kowa baya ganin mutane clearly sai ahankali sannan ganinsa yasoma washewa har yadawo daidai acewar Dr Allah ne yarufa asiri abun bai shafi ganinsa ba, tunda yafara gane mutane bai furta koda kalma daya ba har yaji dan sauki, karin ruwannan da aketa yimasa har yagaji dashi gashi duk jikinsa ciwo yake yimasa saboda alluran da aka huhhuda jikinsa dasu, satinsa biyu a asibiti aka sallameshi bayan andorashi akan magani sannan duk karshen wata zai rinka zuwa yana ganin likita, da yamma aka sallamesu suka tattara suka koma gida. Wanka yashiga yasamu yayi yafito Abba da salim na zaune saman katifa salim na karanta labaran da BBC suka saki akan Facebook,yarfe hannu fahad yayi domin har lokacin hannunsa na dama akwai cannular ajiki wadda har hannun ya dan kumbura kadan musamman ma wurin da aka saka cannular din, zama yayi gefen katifar yana duba kayan da zai saka yana ji aransa dole yabar garin kano domin yayi masa zafi bazai taba iya cigaba da zama agarinba,
"Yazama dole ma inbar garin nan wallahi....."
Dagowa Abba yayi ya kalleshi sannan yagyara kishingidar da yayi agefen katifar,
"Kamar ya?"
"Ya Abba wallahi bazan iya cigaba da zaman garin nan ba.... Gaba daya garin yafita akaina"
"To ina zaka tafi?" Salim ya bukara yana kokarin tashi zaune,
"Salim karatu zan koma...., kuma ba arewa ba, kudu zan tafi idanma son samune inbar kasar gaba daya ko Niger ne intafi"
"Fahad kenan sai hakuri fa rayuwar nan, kayi hakuri kadauki abinda yafaru dakai a matsayin jarrabawa...."
Jin abinda yaya Abba yafada yasashi yin murmushin dole shi kansa ajikinsa yana jin irin ramar da yayi duk yadawo wani shafal shafal dan har yakasa da akiba, bai sake magana ba yadauki bakar round neck t shirt mai gajeren hannu yasaka sannan yasa blue din wando yamike yana laluben turarensa yana jin zuciyarsa na suya,
"Bilkisu wallahi kin yiwa zuciyata tabon da bazai taba gogewa ba har abada......" Yafada acikin zuciyarsa yana kokarin feshe jikinsa da turare, yana gamawa yanufi kofa zai fita domin so yake ya dan fita ya zagaya ko zai ji karfin jikinsa saboda yanzu kam baida wani karfi na azo agani,maganar salim ta dakatar dashi daga yunkurin fitar da yayi niyya,
"Lover boy ga husnah fa na magana a whatsapp....."
Komawa yayi da baya yakarbi wayar yana duba sakon nata kamar haka,
_My prince ya jikin? Kasamu kayi wankan kaci abinci....? Dan Allah karka zauna da yunwa_
Murmushin karfin hali yayi yana kallon salim da ido salim yayi masa alamar tambaya, daga girarsa guda daya yayi ya tsuke baki har lokacin fuskarsa dauke da murmushi, dariya salim yayi,
"Abokina kenan.....,husnah fa kullum idan taje dubaka sai tayi kuka"
Kafin fahad yayi magana Abba yatashi yafita yabar musu dakin gaba daya dan suji dadin tattaunawa dakyau, su dinma basu wani jima acikin dakinba suka fita, da kafa suka dan bi lungunsu fahad har zuwa bakin titi domin fahad ya ware kafarsa sai magrib sannan suka koma gida. Cikin kwana biyu jikinsa ya dan warware yaji dama dama amma kuma har lokacin raunin dake cikin zuciyarsa bai warkeba kawai yana daurewa ne sannan yaji dadin cewa baba saki uku yayiwa bilkisu domin da yace saki dayane yasan dole atursasasu sake zama da juna koda kuwa bata so shikuma bazai so hakanba.
***
A bangaren bilkisu kuwa tana kammala idda abba yace hamood dinta yafito saboda kowa agidan yasan hamood hatta iyallo mutanen garko tasan da zaman hamood domin har gida yaje ya gaisheta yakai mata sha tara ta arziki, khulsum itama ba abarta abayaba wurin yiwa hamood campaign saboda tasan asalin soyayyarsu tun farko duk da bataso rabuwar bilkisu da fahad ba kuma hakan bawai yayi mata dadi bane to amma babu yadda za ayi tunda bilkisu tace saki ukune shima kuma fahad din kamar hadin baki saki uku yace yayi mata. Cikin kankanin lokaci hamood yatura uncle dinsa yaje wurin Abba nan zancen aure ya kullu domin shi Abba baya son zaman zawarcin nan shiyasa yakeso shima ayi bikin da gaggawa, shima senator barewa baija lokacin da tsawo ba yace nanda wata daya sai asha biki sannan kar akai bilkisu da ko cokali yadauki nauyin komai saboda gaba daya 'yayansa ne, aifa nan bilkisu aka shiga shirye shirye da gyare gyaren jiki kowa na gidan cikin farin ciki yake saboda bilkisu baza tayi dogon zawarci ba su elmustapha ne kadai da suka zo hutu basu ji dadin aurannan da zatayi ba domin haka kawai sukaji jininsu bai hadu da na hamood dinnan ba, biki saura sati biyu aka kawo lefe akwatuna goma masu tsada da kyau komai naciki na dunbin kudine nan shirye shirye suka sake zafi babu kama hannun yaro domin hamood yace har dinner zasuyi domin wajibine suyi kara'i. Cikin kankanin lokaci aka kammala komai bilkisu ansha gyara iya gyara duk wani gyara na amare tasha shi sannan tasha tukudi kamar babu gobe domin iyallo ce tazo dashi galan galan tun ana saura sati daya biki dama burinta taga bilkisu tayi sure bawai tasake zama agida ba shiyasa farkon mutuwar auren tazo tayita zuba masifar da kowa na gidan saida yayi la'asar kuma tace lallai lallai bilkisu tafitar da miji tana gama idda aure zatayi wannan dalilinne yasa lokacin da aka gabatar mata da hamood tarinka taka rawar murna. Ranar juma'a aka daura aure ranar asabar akayi yinin biki kuma aranar za akai amarya dakinta sannan za aje dinner, daga amarya har ango farin cikinsu bazai misaltu ba da misalin karfe 8 aka tafi wurin dinner sannan daga can za awuce akai amarya, amarya da ango sunsha dark purple din kaya sunyi kyau mutuka kuma sun burge, har karfe 10 ana wurin dinner din daga can aka raka amarya sannan kowa yasan inda dare yayi masa, gidan amarya yasha kyau a unguwar sabuwar G R A, babban gidane mai dauke da upstairs kasa falo da kitchen da dining area da bedroom guda daya sai sama mai dauke da corridor da kuma bedrooms guda biyu, gaba daya yanda aka tsara gidan yaburge bilkisu, bata wani jima ita dayaba hamood yashigo dauke da kaji da kayan motsa baki, zama yayi kusa da ita yana murmushi,
"Sweetheart yau dai burinmu ya cika, muna yiwa Allah godiya..."
Murmushin itama tayi batare da tace komai ba, kamar yadda addini ya tanadar saida sukayi salla raka,a biyu sannan suka zauna zaman ciyar da juna abinda yashigo musu dashi sunayi suna yan wasanni irin na masoyan da zuka jima acikin tafkin kauna suna linkaya, dakinsa yakoma domin yin shirin bacci kafin yadawo tuni itama tashirya cikin nata kayan baccin masu daukar hankali, tana kwance lamo yashigo sanye da riga da wando dark blue yazo ya kwanta abayanta tareda dora kansa bisa nata, ahankali yake yimata tafiyar tsutsa agashin kanta wanda yasha gyara dan gaske, sun dan fara nisa kadan cikin kogin so suka fara jiyo bugun kofa mai sa firgici wanda ke nuni da ba lafiyaba domin Wanda ke yin bugun tamkar zai balle kofar haka yake yi, cikin bacin rai tare da jan tsaki hamood yatashi yamaida rigarsa yafita dan ganin ko waye itama batayi kasa agwiwa ba tabi bayanshi bayan ta mayar da kayanta, tana zuwa falon kasa yana bude kofa, wata farar matashiyace tashigo taci daurin dankwali irin na yan duniya gaba daya zubinta ma irin na yan bariki ne, wani kallon baki isaba tasoma watsawa bilkisu daga sama zuwa kasa sannan tamaida dubanta ga hamood,
"Meye haka? Me zan gani ni wasila? Dama munyi haka dakaine?..."
"Yi hakuri wise bakya ganin yanzu dare ne?"
"Ina ruwana da wani dare? Malam bafa haka mukayi dakai ba.... Wato kai ga ango ko jikinka sai rawa yake zakasha angonci, to ayi angoncin nagani..... Wuce mutafi...."
Matsawa sosai bilkisu tayi tana karewa matar da hamood yakira da wasila kallo wacce ahaife bazata girmeta ba,juyawa yayi ga bilkisu cikin sanyin murya yace,
"Bilkisu yi hakuri bari naje nadawo, karki damu zuwa safe zan dawo...."
Wani kallo bilkisu tayi masa sannan tamaida kallonta ga wise wacce ke tsaye tana karkada kafa ta taro dan kwalinta gaban goshi alamun no respect,
*Idan har kin san baki biya ba kiyiwa kanki adalci nima kiyi min karki karanta.*
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*KAMAR DA WASA...!*
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*29*
***Tunda aka kai fahad asibiti yake cikin mawuyacin hali gaba daya bai san a inda yakeba bare yasan wanda ke kansa, babban likitan da yake dubashi sai faman fada yake tayiwa su baba yana cewa ya za ayi abar karamin yaro kamar fahad yakamu da ciwon hawan jini wanda ke barazanar taba kwakwalwarsa da lafiyar jikinsa? Domin acewar likitan Allah ne kadai ya takaita abun aka kawoshi asibiti dawuri amma da ace ba akawoshi tun wuriba to irin wannan ne kesawa mutum yana tsaka da tafiya ya yanke jiki yafadi shikenan yahadu da babbar lalura dan haka yazama dole asan yanda za ayi yanisanta kansa da damuwa da yawan tunani domin jininsa yayi masifar hawa hawan da ba aso dan haka yanzu dole akan magani zasu dorashi domin lalurar ta rigada ta kamashi. Daga ayiyah har mamuh kuka suke yi jin wai dan karamin dansu yahadu da cutar zamani ta hawan jini tunda ko su da suke tsoffi basu gamu da irin wannan ciwonba lallai wannan jarraba ce daga Allah, kullum a asibitin suke wuni suna kula da fahad, salim da ya Abba wanda yazo gida saboda dan break din da suka samu na good friday Easter monday, suke kwana awurin fahad sannan suna kula dashi, husnah ma kusan kullum sai tazo asibitin ta dubashi wani lokacin ma har girki take iyo masa, shi dai fahad tunda yafara bude ido dishi dishi yake kallon kowa baya ganin mutane clearly sai ahankali sannan ganinsa yasoma washewa har yadawo daidai acewar Dr Allah ne yarufa asiri abun bai shafi ganinsa ba, tunda yafara gane mutane bai furta koda kalma daya ba har yaji dan sauki, karin ruwannan da aketa yimasa har yagaji dashi gashi duk jikinsa ciwo yake yimasa saboda alluran da aka huhhuda jikinsa dasu, satinsa biyu a asibiti aka sallameshi bayan andorashi akan magani sannan duk karshen wata zai rinka zuwa yana ganin likita, da yamma aka sallamesu suka tattara suka koma gida. Wanka yashiga yasamu yayi yafito Abba da salim na zaune saman katifa salim na karanta labaran da BBC suka saki akan Facebook,yarfe hannu fahad yayi domin har lokacin hannunsa na dama akwai cannular ajiki wadda har hannun ya dan kumbura kadan musamman ma wurin da aka saka cannular din, zama yayi gefen katifar yana duba kayan da zai saka yana ji aransa dole yabar garin kano domin yayi masa zafi bazai taba iya cigaba da zama agarinba,
"Yazama dole ma inbar garin nan wallahi....."
Dagowa Abba yayi ya kalleshi sannan yagyara kishingidar da yayi agefen katifar,
"Kamar ya?"
"Ya Abba wallahi bazan iya cigaba da zaman garin nan ba.... Gaba daya garin yafita akaina"
"To ina zaka tafi?" Salim ya bukara yana kokarin tashi zaune,
"Salim karatu zan koma...., kuma ba arewa ba, kudu zan tafi idanma son samune inbar kasar gaba daya ko Niger ne intafi"
"Fahad kenan sai hakuri fa rayuwar nan, kayi hakuri kadauki abinda yafaru dakai a matsayin jarrabawa...."
Jin abinda yaya Abba yafada yasashi yin murmushin dole shi kansa ajikinsa yana jin irin ramar da yayi duk yadawo wani shafal shafal dan har yakasa da akiba, bai sake magana ba yadauki bakar round neck t shirt mai gajeren hannu yasaka sannan yasa blue din wando yamike yana laluben turarensa yana jin zuciyarsa na suya,
"Bilkisu wallahi kin yiwa zuciyata tabon da bazai taba gogewa ba har abada......" Yafada acikin zuciyarsa yana kokarin feshe jikinsa da turare, yana gamawa yanufi kofa zai fita domin so yake ya dan fita ya zagaya ko zai ji karfin jikinsa saboda yanzu kam baida wani karfi na azo agani,maganar salim ta dakatar dashi daga yunkurin fitar da yayi niyya,
"Lover boy ga husnah fa na magana a whatsapp....."
Komawa yayi da baya yakarbi wayar yana duba sakon nata kamar haka,
_My prince ya jikin? Kasamu kayi wankan kaci abinci....? Dan Allah karka zauna da yunwa_
Murmushin karfin hali yayi yana kallon salim da ido salim yayi masa alamar tambaya, daga girarsa guda daya yayi ya tsuke baki har lokacin fuskarsa dauke da murmushi, dariya salim yayi,
"Abokina kenan.....,husnah fa kullum idan taje dubaka sai tayi kuka"
Kafin fahad yayi magana Abba yatashi yafita yabar musu dakin gaba daya dan suji dadin tattaunawa dakyau, su dinma basu wani jima acikin dakinba suka fita, da kafa suka dan bi lungunsu fahad har zuwa bakin titi domin fahad ya ware kafarsa sai magrib sannan suka koma gida. Cikin kwana biyu jikinsa ya dan warware yaji dama dama amma kuma har lokacin raunin dake cikin zuciyarsa bai warkeba kawai yana daurewa ne sannan yaji dadin cewa baba saki uku yayiwa bilkisu domin da yace saki dayane yasan dole atursasasu sake zama da juna koda kuwa bata so shikuma bazai so hakanba.
***
A bangaren bilkisu kuwa tana kammala idda abba yace hamood dinta yafito saboda kowa agidan yasan hamood hatta iyallo mutanen garko tasan da zaman hamood domin har gida yaje ya gaisheta yakai mata sha tara ta arziki, khulsum itama ba abarta abayaba wurin yiwa hamood campaign saboda tasan asalin soyayyarsu tun farko duk da bataso rabuwar bilkisu da fahad ba kuma hakan bawai yayi mata dadi bane to amma babu yadda za ayi tunda bilkisu tace saki ukune shima kuma fahad din kamar hadin baki saki uku yace yayi mata. Cikin kankanin lokaci hamood yatura uncle dinsa yaje wurin Abba nan zancen aure ya kullu domin shi Abba baya son zaman zawarcin nan shiyasa yakeso shima ayi bikin da gaggawa, shima senator barewa baija lokacin da tsawo ba yace nanda wata daya sai asha biki sannan kar akai bilkisu da ko cokali yadauki nauyin komai saboda gaba daya 'yayansa ne, aifa nan bilkisu aka shiga shirye shirye da gyare gyaren jiki kowa na gidan cikin farin ciki yake saboda bilkisu baza tayi dogon zawarci ba su elmustapha ne kadai da suka zo hutu basu ji dadin aurannan da zatayi ba domin haka kawai sukaji jininsu bai hadu da na hamood dinnan ba, biki saura sati biyu aka kawo lefe akwatuna goma masu tsada da kyau komai naciki na dunbin kudine nan shirye shirye suka sake zafi babu kama hannun yaro domin hamood yace har dinner zasuyi domin wajibine suyi kara'i. Cikin kankanin lokaci aka kammala komai bilkisu ansha gyara iya gyara duk wani gyara na amare tasha shi sannan tasha tukudi kamar babu gobe domin iyallo ce tazo dashi galan galan tun ana saura sati daya biki dama burinta taga bilkisu tayi sure bawai tasake zama agida ba shiyasa farkon mutuwar auren tazo tayita zuba masifar da kowa na gidan saida yayi la'asar kuma tace lallai lallai bilkisu tafitar da miji tana gama idda aure zatayi wannan dalilinne yasa lokacin da aka gabatar mata da hamood tarinka taka rawar murna. Ranar juma'a aka daura aure ranar asabar akayi yinin biki kuma aranar za akai amarya dakinta sannan za aje dinner, daga amarya har ango farin cikinsu bazai misaltu ba da misalin karfe 8 aka tafi wurin dinner sannan daga can za awuce akai amarya, amarya da ango sunsha dark purple din kaya sunyi kyau mutuka kuma sun burge, har karfe 10 ana wurin dinner din daga can aka raka amarya sannan kowa yasan inda dare yayi masa, gidan amarya yasha kyau a unguwar sabuwar G R A, babban gidane mai dauke da upstairs kasa falo da kitchen da dining area da bedroom guda daya sai sama mai dauke da corridor da kuma bedrooms guda biyu, gaba daya yanda aka tsara gidan yaburge bilkisu, bata wani jima ita dayaba hamood yashigo dauke da kaji da kayan motsa baki, zama yayi kusa da ita yana murmushi,
"Sweetheart yau dai burinmu ya cika, muna yiwa Allah godiya..."
Murmushin itama tayi batare da tace komai ba, kamar yadda addini ya tanadar saida sukayi salla raka,a biyu sannan suka zauna zaman ciyar da juna abinda yashigo musu dashi sunayi suna yan wasanni irin na masoyan da zuka jima acikin tafkin kauna suna linkaya, dakinsa yakoma domin yin shirin bacci kafin yadawo tuni itama tashirya cikin nata kayan baccin masu daukar hankali, tana kwance lamo yashigo sanye da riga da wando dark blue yazo ya kwanta abayanta tareda dora kansa bisa nata, ahankali yake yimata tafiyar tsutsa agashin kanta wanda yasha gyara dan gaske, sun dan fara nisa kadan cikin kogin so suka fara jiyo bugun kofa mai sa firgici wanda ke nuni da ba lafiyaba domin Wanda ke yin bugun tamkar zai balle kofar haka yake yi, cikin bacin rai tare da jan tsaki hamood yatashi yamaida rigarsa yafita dan ganin ko waye itama batayi kasa agwiwa ba tabi bayanshi bayan ta mayar da kayanta, tana zuwa falon kasa yana bude kofa, wata farar matashiyace tashigo taci daurin dankwali irin na yan duniya gaba daya zubinta ma irin na yan bariki ne, wani kallon baki isaba tasoma watsawa bilkisu daga sama zuwa kasa sannan tamaida dubanta ga hamood,
"Meye haka? Me zan gani ni wasila? Dama munyi haka dakaine?..."
"Yi hakuri wise bakya ganin yanzu dare ne?"
"Ina ruwana da wani dare? Malam bafa haka mukayi dakai ba.... Wato kai ga ango ko jikinka sai rawa yake zakasha angonci, to ayi angoncin nagani..... Wuce mutafi...."
Matsawa sosai bilkisu tayi tana karewa matar da hamood yakira da wasila kallo wacce ahaife bazata girmeta ba,juyawa yayi ga bilkisu cikin sanyin murya yace,
"Bilkisu yi hakuri bari naje nadawo, karki damu zuwa safe zan dawo...."
Wani kallo bilkisu tayi masa sannan tamaida kallonta ga wise wacce ke tsaye tana karkada kafa ta taro dan kwalinta gaban goshi alamun no respect,