Sashe 15
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Murmushi yayi shi wlhi drama din da zasuyi da bilkisu kawai yake hangowa,
"Am sorry bazan sakeba amma seriously na dan rame fa"
"To ya za ayi ai situation ne"
Daga haka tawuce ciki ta dauko masa kayan da zai dinka mata takoma wurinsa,yana tsaye a inda tabarshi yana yin waya ganin tana jiranshi yakatse wayar yamaida hankalinsa gareta,
"Gashi duk riga da skirt zaka yimin..."
"Banda doguwar riga?"
"To Kaduba dai kagani idan akwai wanda zaiyi kyau da doguwar rigar sai kayi min"
"Shikenan to, kigaida su ammah"
"Zasuji"
Fita yayi yatafi ita kuma takoma ciki wurin khulsum wacce ke jiranta tayi wanka su fita gidan da za ayi mata gyaran jiki saboda yau za afara.
Cikin kwana biyu yagama dinkunan bilkisu kala takwas ne shadda guda biyu leshi guda biyu sai material da atamfa suma duk kala bibbiyu amma abinda yabashi mamaki duk cikin kayan babu na cikin lefenshi wanda yasaka amma bai kawo komai aranshi ba tunda watakila wannan din agidansu aka yimata, bai samu damar Kai mata kayan da kansa ba sai salim ne yakai saboda shi ranar yana can gidanshi ana saka masa tile da sauran abubuwan da ba akarasa ba, washe gari aka karasa komai na gidan akayi fenti gida yafito rangadau dama unguwar shiru take babu gidaje da yawa ma domin sabuwar unguwace bata fara yawaba, agajiye yakoma gida bayan sallar ishah wanka kawai yayi ya kwanta ko abinci bai nema ba babu bata lokaci baccin gajiya yace muje zuwa, koda Abba yashigo yaganshi baje yana bacci dariya yayi yace,
"Dole kayi bacci ango, irin wannan commitment Haka?"
Dasafe garau yatashi sakamakon baccin da yasha sosai adaren jiya, miss called din bilkisu yagani har guda uku hakan yabashi tabbacin akwai dalili shiyasa yayi gaggawar calling dinta back,
"Fahad dakuna nawane agidan, kofofi nawane sannan windows nawane? Muna wurin masu dinka cuttens ne"
"To hajjaju bari naturo miki gaba daya pics din gidan ki ganshi"
"Yawwa dan Allah hanzarta"
Katse wayar tayi nan yashiga whatsapp yatura mata aranshi yana cewa,
"Akwai rikici nasani"
Bai kara jin duriyarta ba sai text tamishi akan yabasu keys din gidan saboda masu zuwa jeren kaya gobe nanma aiken yayi mata aka kai musu, sai ana igobe kamu ta kirashi tana yimishi maganar itafa baza suje wata dinner ba walima kadai zatayi da friends dinta dan haka shima ya hada reception da friends dinshi kawai ya isa, tayi hakane saboda kunyar yaje dinner mutane su ganshi take,bai musa ba yace to.
Tana zaune tayi uban tagumi bayan mai kunshi tagama yarfa mata jan lalle da baki, khulsum tashigo agajiye itama daga kunshin take, zama tayi kusa da bilkisu wacce ke kallon masu shigowa da masu fita tayi tagumi,
"Wallahi fahad dinnan yayi yaro da yawa, Allah mai yadda yaso..."
Dariya khulsum tayi,
"Baiwar Allah ki rungumi kaddara kiyi hakuri, haka Allah yashirya ko jinjirine dai shine mijinki uban yayanki..."
"Tab.... Allah ya kiyaye, nifa wallahi baki ma san wani abuba, kunyar nunashi nake a matsayin mijina"
"Sai kiyi kuma malama, wai inasu maama?"
"Suna can gidanshi karasa jere"
"Gidanki dai, kyace wani gidanshi"
"Kinga malama ni idan kina tashi kitashi mutafi kitson nan idan kuma baki zuwa ki sanar dani"
"Ahh kinga karki fada min bak'a, shirya muje amma wallahi da retouching kikayi zaifi kitson nan, kinga kanki yanzu fa kullum sai yaji ruwa"
"Kanki akeji, ni tashi mutafi dan bamuda lokaci"
Hijabinta tasaka har kasa suka tafi bayan tayiwa ammah sallama iyallo sai jaraba take wai yakamata ta daina fita hakanan amma tunda tazo gidannan bataga ta yini agida batare da ta fita ba, batace komai ba tabi khulsum suka tafi,
"Shagon ma da babu wani nisa nan bayane fa amma shine iyallo sai tayiwa mutane ihu aka, kai Allah yakyauta"
"Ai keda iyallon nan taku kuna sani nishadi wallahi, gaskiya i have been missing my grandma"
Dariya bilkisu tayi,
"Uhm ai iyallo bata haduba sam wallahi, hajjaye kakarmu ta wurin uwa tafi kirki"
"Kya hadu da Abba wallahi"
"Bawani nahadu da abba ai gaskiyace"
Har sukaje shagon hirar iyallo suke yi. Kitso hadadde aka yarfawa bilkisu dan har la'asar lis suna shagon ita kuma khulsum akayi mata retouching, tun suna hanya taga su meenah nata kiranta, koda tashigo gida suma suna gidan ana yimusu kunshi har angama musu yanzu hindu ake yiwa itama ankusa gamawa,
"Wai wai wai... Gaskiya yakamata yaya fahad yaga wannan kitson da lallen" inji Hindu bayan bilkisu tacire hijab din kanta,
"To ke gaggawar me kike ko kin mantane nanda jibi suna jone ana..." Maama tafada cikin shakiyanci, tun kafin tarufe bakinta bilkisu takai mata duka ta gudu,
"Allah adda labour idan ya fahad yaga kunshin nan da kitson nan zaucewa kawaine bazai yiba" meenah itama ta karbi zancen,
"Wai dama haka kuke bakuda kunya?" Khulsum tafada tana rike haba,
"A'a wallahi Anty khulsum ai kin san Adda labour kakarmu ce fa dole mu rinka janta" inji meenah,
"Adda mai gado ki fada masa angama komai yatura wadanda zasu jire gidan saboda anjima suma su yafendon zasu taho"
Bata tanka ba takarasa shiga cikin daki wanda yanzu kayan ciki suka zama sai saura domin duk su maama sun shirge mata kayanta sunyi mata gaba dashi sai wanda zata nema kawai aka bari, zama tayi gefen gadonta tana kallon tv domin wani Indian film ake haskawa atashar MBC Bollywood mai suna a gentleman, wayar fahad takira ringing biyu yadauka,
"Ranki yadade..."
"Am yawwa kaga angama jeren nanne shine zan fada maka katura wasu sai su kwana agidan"
"Angama ranki yadade"
Katse wayar tayi tamike tafita waje wurinsu khulsum. Kamar yadda yafada da daddare su salim da Abba ya tura domin su kwana agidan,lokacin da zasu tafi jan salim yayi yace masa,
"Allah karku kwanta mana agado kasan dai babu kyau..."
Dariya salim yayi yakai masa duka,
"Allah ko fitsararre? To ai ya Abba yadace ka fadawa tunda shine babba amma baniba"
"Shi ai nasan bazaiyi hakaba sai kai...."
"To kuwa kwana bisa gadonku daram..."
"Wallahi karka kuskura..."
"Sai kayi kuma...."
Daga haka yayi gaba abinshi, fahad kam neman wuri yayi ya zauna nan kofar gida domin cikin gidan cike yake da mata yan uwa da abokan arziki, saida yakira bilkisu yasanar da ita yatura wadanda zasu yi gadin gidan sannan hankalinta ya kwanta.
Washe gari da shirye shirye aka tashi kasancewar ranar za ayi kamu, kuma anan compound din gidan za ayi kamun domin ita bata da ra'ayin zuwa hall, kowa kagani acikin hidima yake fuskarsa dauke da farin ciki ba ma kamar ya mahaifiyarta ammah wacce ke jin kamar ancire mata k'aya, yanzu kam tasan zasu huta da wadannan maganganun da habaice habaicen da ake yimusu acikin dangi, mutane sukan manta da cewa Allah shine gwani wurin iya tsara komai na rayuwar bayinsa kuma duk yanda ya tsara to hakance zata faru ko anaso ko ba aso, ko anshirya ko ba ashirya ba. Su meenah dai ana can wurin masu decoration ana nuna musu muhallin da yadace asaka kowacce kwalliya domin gudun kuskure, amarya fa? Ana can daki tareda bakinta wadanda suka zazzo daga sassa daban daban na jihar Kano musamman ma wadanda sukayi secondary school tare da wadanda sukayi Jami'a shiyasa itama yau tasamu nasarar warewa ta cika da farin ciki saboda ganin wadanda tajima bata ganiba amma da har masifa tayiwa khulsum lokacin da ta turawa class mates dinsu invitation card ta group chat dinsu dake Facebook da whatsapp tana cemusu ga labour prefect dinsu fa zatayi aure dan haka su daura damarar zuwa shan shagali, ai kuwa sunyi mata kara domin kusan duk wadanda ke zaune acikin kano sunzo,anyi bushasha babu laifi domin chicken pepe da lafiyayyar fried rice aka dafo aka kawowa friends din nasu wanda wannan yana daya daga cikin gudunmawar khulsum banda kayan sanyaya makoshi cikin manya manyan kuloli, ba karamin kyau amarya tayiba tun kafin tayi shirin zuwa wurin kamu, karfe uku tayi wanka da ruwan lalle da turare, tana yin sallar la'asar kuma mai kwalliya tafara aikinta, wanda suka dauki tsawon lokaci sunayi,
"Masha Allah...masha Allah" shine abinda kowa ke fadi lokacin da amarya tafito domin ba karamin kyau tayi ba, tayi kyau na bugawa ajarida, komai na jikinta golden colour ne kama tun daga material din jikinta wanda akayi kyakkyawar doguwar riga irinta amare zuwa head din dake nade akanta da takalminta,pose da komai da amarya ke sakawa har sarka da dan kunne, kidanta daban aka saka mata lokacin da ta karasa wurin khulsum na rike da hannunta, fuskarta abude take amma da akwai wani net me kyau akanta, kujerar da aka tanada musamman dominta taje ta zauna babu bata lokaci aka fara gudanar da abinda yadace daidai lokacin dangin ango suka karaso nan aka tarbesu aka basu wurin zama suka zazzauna. Babu karya kamun yayi kyau domin babu tarkacen shirme aciki kawai dan abinda ba arasa ba aka gudanar daga nan su iyallo suka zo suka sakawa amarya lalle lokacin magriba takusa, dangin ango basu tafiba saida aka gama komai, suka daddauki pics da amarya da danginta sannan suka tafi bayan anware musu manyan jakunkunan da aka rarraba awurin. Ango kuwa yana can gidansu salim adakinsu amma yana ganin duk abinda yake faruwa awurin kamun domin yatura mutane biyu daya zaiyi video coverage dayan kuma zai rinka turo masa ta whatsapp, hakance kuwa tafaru domin komai kamar akan idonsa akeyi....
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA....!*
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*17*
*Kamar da wasa na saidawa ne yar uwa idan kinada bukata kisiya sai ki karanta.*
***Ba karamin kyau tayi masa ba, yau sai yaga tafi koyaushe kyau kamar zaka saceta ka gudu ko kuma ko dan bai taba ganinta cikin kwalliya kamar haka bane shiyasa yau yaga kamar canjata akayi? Kunshin dake hannunta yaketa zooming yana kallo sannan yakoma kan fuskarta itama yarinka zooming dinta yana gani,dariyar shakiyanci yayi lokacin da ya kurawa kirjinta ido bayan yayi zooming,
"Aita boye abu ayita boye abu to yau dai gashi ina kallo..."
"Am sorry bazan sakeba amma seriously na dan rame fa"
"To ya za ayi ai situation ne"
Daga haka tawuce ciki ta dauko masa kayan da zai dinka mata takoma wurinsa,yana tsaye a inda tabarshi yana yin waya ganin tana jiranshi yakatse wayar yamaida hankalinsa gareta,
"Gashi duk riga da skirt zaka yimin..."
"Banda doguwar riga?"
"To Kaduba dai kagani idan akwai wanda zaiyi kyau da doguwar rigar sai kayi min"
"Shikenan to, kigaida su ammah"
"Zasuji"
Fita yayi yatafi ita kuma takoma ciki wurin khulsum wacce ke jiranta tayi wanka su fita gidan da za ayi mata gyaran jiki saboda yau za afara.
Cikin kwana biyu yagama dinkunan bilkisu kala takwas ne shadda guda biyu leshi guda biyu sai material da atamfa suma duk kala bibbiyu amma abinda yabashi mamaki duk cikin kayan babu na cikin lefenshi wanda yasaka amma bai kawo komai aranshi ba tunda watakila wannan din agidansu aka yimata, bai samu damar Kai mata kayan da kansa ba sai salim ne yakai saboda shi ranar yana can gidanshi ana saka masa tile da sauran abubuwan da ba akarasa ba, washe gari aka karasa komai na gidan akayi fenti gida yafito rangadau dama unguwar shiru take babu gidaje da yawa ma domin sabuwar unguwace bata fara yawaba, agajiye yakoma gida bayan sallar ishah wanka kawai yayi ya kwanta ko abinci bai nema ba babu bata lokaci baccin gajiya yace muje zuwa, koda Abba yashigo yaganshi baje yana bacci dariya yayi yace,
"Dole kayi bacci ango, irin wannan commitment Haka?"
Dasafe garau yatashi sakamakon baccin da yasha sosai adaren jiya, miss called din bilkisu yagani har guda uku hakan yabashi tabbacin akwai dalili shiyasa yayi gaggawar calling dinta back,
"Fahad dakuna nawane agidan, kofofi nawane sannan windows nawane? Muna wurin masu dinka cuttens ne"
"To hajjaju bari naturo miki gaba daya pics din gidan ki ganshi"
"Yawwa dan Allah hanzarta"
Katse wayar tayi nan yashiga whatsapp yatura mata aranshi yana cewa,
"Akwai rikici nasani"
Bai kara jin duriyarta ba sai text tamishi akan yabasu keys din gidan saboda masu zuwa jeren kaya gobe nanma aiken yayi mata aka kai musu, sai ana igobe kamu ta kirashi tana yimishi maganar itafa baza suje wata dinner ba walima kadai zatayi da friends dinta dan haka shima ya hada reception da friends dinshi kawai ya isa, tayi hakane saboda kunyar yaje dinner mutane su ganshi take,bai musa ba yace to.
Tana zaune tayi uban tagumi bayan mai kunshi tagama yarfa mata jan lalle da baki, khulsum tashigo agajiye itama daga kunshin take, zama tayi kusa da bilkisu wacce ke kallon masu shigowa da masu fita tayi tagumi,
"Wallahi fahad dinnan yayi yaro da yawa, Allah mai yadda yaso..."
Dariya khulsum tayi,
"Baiwar Allah ki rungumi kaddara kiyi hakuri, haka Allah yashirya ko jinjirine dai shine mijinki uban yayanki..."
"Tab.... Allah ya kiyaye, nifa wallahi baki ma san wani abuba, kunyar nunashi nake a matsayin mijina"
"Sai kiyi kuma malama, wai inasu maama?"
"Suna can gidanshi karasa jere"
"Gidanki dai, kyace wani gidanshi"
"Kinga malama ni idan kina tashi kitashi mutafi kitson nan idan kuma baki zuwa ki sanar dani"
"Ahh kinga karki fada min bak'a, shirya muje amma wallahi da retouching kikayi zaifi kitson nan, kinga kanki yanzu fa kullum sai yaji ruwa"
"Kanki akeji, ni tashi mutafi dan bamuda lokaci"
Hijabinta tasaka har kasa suka tafi bayan tayiwa ammah sallama iyallo sai jaraba take wai yakamata ta daina fita hakanan amma tunda tazo gidannan bataga ta yini agida batare da ta fita ba, batace komai ba tabi khulsum suka tafi,
"Shagon ma da babu wani nisa nan bayane fa amma shine iyallo sai tayiwa mutane ihu aka, kai Allah yakyauta"
"Ai keda iyallon nan taku kuna sani nishadi wallahi, gaskiya i have been missing my grandma"
Dariya bilkisu tayi,
"Uhm ai iyallo bata haduba sam wallahi, hajjaye kakarmu ta wurin uwa tafi kirki"
"Kya hadu da Abba wallahi"
"Bawani nahadu da abba ai gaskiyace"
Har sukaje shagon hirar iyallo suke yi. Kitso hadadde aka yarfawa bilkisu dan har la'asar lis suna shagon ita kuma khulsum akayi mata retouching, tun suna hanya taga su meenah nata kiranta, koda tashigo gida suma suna gidan ana yimusu kunshi har angama musu yanzu hindu ake yiwa itama ankusa gamawa,
"Wai wai wai... Gaskiya yakamata yaya fahad yaga wannan kitson da lallen" inji Hindu bayan bilkisu tacire hijab din kanta,
"To ke gaggawar me kike ko kin mantane nanda jibi suna jone ana..." Maama tafada cikin shakiyanci, tun kafin tarufe bakinta bilkisu takai mata duka ta gudu,
"Allah adda labour idan ya fahad yaga kunshin nan da kitson nan zaucewa kawaine bazai yiba" meenah itama ta karbi zancen,
"Wai dama haka kuke bakuda kunya?" Khulsum tafada tana rike haba,
"A'a wallahi Anty khulsum ai kin san Adda labour kakarmu ce fa dole mu rinka janta" inji meenah,
"Adda mai gado ki fada masa angama komai yatura wadanda zasu jire gidan saboda anjima suma su yafendon zasu taho"
Bata tanka ba takarasa shiga cikin daki wanda yanzu kayan ciki suka zama sai saura domin duk su maama sun shirge mata kayanta sunyi mata gaba dashi sai wanda zata nema kawai aka bari, zama tayi gefen gadonta tana kallon tv domin wani Indian film ake haskawa atashar MBC Bollywood mai suna a gentleman, wayar fahad takira ringing biyu yadauka,
"Ranki yadade..."
"Am yawwa kaga angama jeren nanne shine zan fada maka katura wasu sai su kwana agidan"
"Angama ranki yadade"
Katse wayar tayi tamike tafita waje wurinsu khulsum. Kamar yadda yafada da daddare su salim da Abba ya tura domin su kwana agidan,lokacin da zasu tafi jan salim yayi yace masa,
"Allah karku kwanta mana agado kasan dai babu kyau..."
Dariya salim yayi yakai masa duka,
"Allah ko fitsararre? To ai ya Abba yadace ka fadawa tunda shine babba amma baniba"
"Shi ai nasan bazaiyi hakaba sai kai...."
"To kuwa kwana bisa gadonku daram..."
"Wallahi karka kuskura..."
"Sai kayi kuma...."
Daga haka yayi gaba abinshi, fahad kam neman wuri yayi ya zauna nan kofar gida domin cikin gidan cike yake da mata yan uwa da abokan arziki, saida yakira bilkisu yasanar da ita yatura wadanda zasu yi gadin gidan sannan hankalinta ya kwanta.
Washe gari da shirye shirye aka tashi kasancewar ranar za ayi kamu, kuma anan compound din gidan za ayi kamun domin ita bata da ra'ayin zuwa hall, kowa kagani acikin hidima yake fuskarsa dauke da farin ciki ba ma kamar ya mahaifiyarta ammah wacce ke jin kamar ancire mata k'aya, yanzu kam tasan zasu huta da wadannan maganganun da habaice habaicen da ake yimusu acikin dangi, mutane sukan manta da cewa Allah shine gwani wurin iya tsara komai na rayuwar bayinsa kuma duk yanda ya tsara to hakance zata faru ko anaso ko ba aso, ko anshirya ko ba ashirya ba. Su meenah dai ana can wurin masu decoration ana nuna musu muhallin da yadace asaka kowacce kwalliya domin gudun kuskure, amarya fa? Ana can daki tareda bakinta wadanda suka zazzo daga sassa daban daban na jihar Kano musamman ma wadanda sukayi secondary school tare da wadanda sukayi Jami'a shiyasa itama yau tasamu nasarar warewa ta cika da farin ciki saboda ganin wadanda tajima bata ganiba amma da har masifa tayiwa khulsum lokacin da ta turawa class mates dinsu invitation card ta group chat dinsu dake Facebook da whatsapp tana cemusu ga labour prefect dinsu fa zatayi aure dan haka su daura damarar zuwa shan shagali, ai kuwa sunyi mata kara domin kusan duk wadanda ke zaune acikin kano sunzo,anyi bushasha babu laifi domin chicken pepe da lafiyayyar fried rice aka dafo aka kawowa friends din nasu wanda wannan yana daya daga cikin gudunmawar khulsum banda kayan sanyaya makoshi cikin manya manyan kuloli, ba karamin kyau amarya tayiba tun kafin tayi shirin zuwa wurin kamu, karfe uku tayi wanka da ruwan lalle da turare, tana yin sallar la'asar kuma mai kwalliya tafara aikinta, wanda suka dauki tsawon lokaci sunayi,
"Masha Allah...masha Allah" shine abinda kowa ke fadi lokacin da amarya tafito domin ba karamin kyau tayi ba, tayi kyau na bugawa ajarida, komai na jikinta golden colour ne kama tun daga material din jikinta wanda akayi kyakkyawar doguwar riga irinta amare zuwa head din dake nade akanta da takalminta,pose da komai da amarya ke sakawa har sarka da dan kunne, kidanta daban aka saka mata lokacin da ta karasa wurin khulsum na rike da hannunta, fuskarta abude take amma da akwai wani net me kyau akanta, kujerar da aka tanada musamman dominta taje ta zauna babu bata lokaci aka fara gudanar da abinda yadace daidai lokacin dangin ango suka karaso nan aka tarbesu aka basu wurin zama suka zazzauna. Babu karya kamun yayi kyau domin babu tarkacen shirme aciki kawai dan abinda ba arasa ba aka gudanar daga nan su iyallo suka zo suka sakawa amarya lalle lokacin magriba takusa, dangin ango basu tafiba saida aka gama komai, suka daddauki pics da amarya da danginta sannan suka tafi bayan anware musu manyan jakunkunan da aka rarraba awurin. Ango kuwa yana can gidansu salim adakinsu amma yana ganin duk abinda yake faruwa awurin kamun domin yatura mutane biyu daya zaiyi video coverage dayan kuma zai rinka turo masa ta whatsapp, hakance kuwa tafaru domin komai kamar akan idonsa akeyi....
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA....!*
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*17*
*Kamar da wasa na saidawa ne yar uwa idan kinada bukata kisiya sai ki karanta.*
***Ba karamin kyau tayi masa ba, yau sai yaga tafi koyaushe kyau kamar zaka saceta ka gudu ko kuma ko dan bai taba ganinta cikin kwalliya kamar haka bane shiyasa yau yaga kamar canjata akayi? Kunshin dake hannunta yaketa zooming yana kallo sannan yakoma kan fuskarta itama yarinka zooming dinta yana gani,dariyar shakiyanci yayi lokacin da ya kurawa kirjinta ido bayan yayi zooming,
"Aita boye abu ayita boye abu to yau dai gashi ina kallo..."