← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 67 OF 67

Sashe 67

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

Wata dariyar yasake yi cikeda farin ciki, hannunta yakama suka nufi cikin mota yana bata labarin dinner din da zata rakashi yau da daddare ta wani friend dinshi, sau dayawa idan yace ta rakashi party ko dinner sai tace a'a ita bataso suje tare ayi masa dariya kowa yana tafiya da yar karamar yarinya yar kasa da 25 amma shi yadebi tsohuwa duk lokacin da tafadi haka sai yayi dariya yace Shifa har yanzu yakasa ganin girman da taketa kurin tana dashi saboda kallon mitsitsiyar yarinya yake yimata her age is just a number, kuma ako ina baya kunyar nunata amatsayin matarshi duk inda zaije tare da ita yake zuwa, ko wannan umarar ma da sukaje da yara har ita yaso sutafi duk da last time iya su biyu sukaje sukasha soyayyarsu suka barwa ammah yaran,to wannan zuwan amma aiki ya hanata kasancewar tazama babbar jami'ar gwamnati mai kulada harkokin yada labarai shikuma ma'aikacine a asibitin koyarwa na mal Aminu maganar dinki kuwa tun shekarun baya yadaina domin bilkisu takafa ta tsare ita kadai yake yiwa dinki ahalin yanzu amma yanada babban shago da yabude yazuba ma'aikata sukeyi. Kowa yasan irin shakuwa da soyayyar dake tsakanin ma'auratan, lokuta da dama su maama na gulmarsu idan suka hadu suce sun rasa wannan irin kauna ta adda labour da ya fahad duk sunbi sun bata junansu da shagwaba kullum cikin yiwa juna shagwaba suke kuma duk fahad ne ya koya ma Bilkisu, ita dai Bilkisu babu abinda zata cewa fahad sai fatan alkhairi domin ya zame mata wani babban jigo acikin rayuwarta, guy din yayine tako ina yanada yakana da kunya da kawaici ga iya soyayya shiyasa baya taba gundurarta sannan yana respecting dinta takowanne bangare baya taba treating dinta kamar karamar yarinya sai ta bangaren love, itafa yanzu da zataga wacce karamin yaro da babba zasu fito neman aurenta da zata bata shawarar ta auri yaron domin sai yafi kulawa da ita, abangaren fahad shima hakane kwata kwata baya sha'awar auren karamar yarinya acewarsa wacce ta girmeka tafi kula dakai zatayi treating dinka kamar baby amma kananan yaran nan babu abinda suka ajiye sai rashin kunya, ahalin yanzu dai yaransu hudu da bilkisu hanfa da Muhammad fahad sai Mimi da Awwab, to muna addu'ar Allah yaraya su amin.

Alhamdulillah anan labarin kamar da wasa ya kammala ina addu'ar ubangiji Allah ya taramu cikin ladan nidaku yakuma yafe mana a inda nayi kuskure. Hakika ban taba sanin inada dunbin masoya har hakaba wallahi sai yanzu, tabbas kun nuna min kauna da kuma soyayya, da yawa daga cikinku wadanda suka siyi book dinnnan ban sanku ba banma taba tunanin kun san da niba, ina mutukar godiya hakika soyayyarku wallahi itace abar dubawa agareni bawai kudin da kuka siyaba domin mai sonka shi zaiso kayanka nagode Allah yabar zumunci,sai mun hadu cikin kundin haske wato gamayyar alkaluman marubutan haske gaba daya, zanzo muku da wani labari mai salo daban akan darajar malami da amfaninsa cikin alumma, sai mun hadu da yardar Allah taku ahar kullum Ummi A'isha.

*_
*_Ummi Shatu_*
Chapter 67 · 0% Book details