← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 43 OF 67

Sashe 43

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Mayen sonta ba, pls salim be serious... Wallahi Bilkisu bata taba yimin wani abu na cutarwa ba aduk tsawon zamanmu kawai abu daya tayi min wanda wannan ma kaddara ce da sharrin shaidan amma kai kanka shaidane munyi zaman lafiya da ita tunda kaima kana zuwa gidan kuma idanuwanka suna gane maka..... Wallahi salim ina sonta narasa ya zanyi...."

Ajiyar zuciya salim ya sauke sannan ya kalleshi,

"Nifa har yanzu banji kafadi abinda yarabaku ba nikuma shi nake son sani...."

"Salim wannan kuma ai sirrine, amma karka dora laifin akanta ka dorashi akaina... Sannan mubarshi azuwan kaddara"

"Shikenan Allah ya zabi abinda yafi alkhairi"

"Yawwa abokina, amin, dan Allah kazama cikin shiri domin wannan karon dakai za ayi yakin sannan katayani da addu'a.... Bari nahaura sama"

"Ashirye nake ai" salim yafada yana dariya, fita fahad yayi yahaura sama yana murmushi,

"Salim kenan...." Yafada acikin zuciyarshi lokacin da yake kokarin shiga cikin shagonsu. Tsawon sati biyu yadauka yana ririta maganar aranshi amma yarasa ta yadda zai iya fadawa su ayiyah ko baba, shidai yasan yayi addu'a a tsawon sati biyun nan sosai kuma har yau baiji canjiba gameda soyayyar Bilkisu sai dai abinda ke yawan fadar masa da gaba shine watanni biyu kenan da su baba suka kai musu kudin aure shida ya Abba, shi fahad gidan kanin Baban husnah dake Kaduna aka kai masa shikuma ya Abba Nusaiba kanwar salim, duk da haka baya jin zai iya hakura da auren Bilkisu koda kuwa mata uku yakaiwa kudin aure mutukar yanada gurbin da zai sakata, kullum da maganar yake kwana yana tashi amma idan yaje cikin gida sai yakasa sanar dasu amma yau ya kuduri aniyar fada ko yasamu yaji sauki acikin ranshi, mamuh yasamu tsakar gida tana daka fura ita kuma ayiya na dafa kindirmo, zama yayi kan kujerar mamuh yar tsugunno,

"Ayiyah dan Allah wani taimako nake son kuyi min.."

Dukkaninsu dakatawa sukayi daga abinda sukeyi suna sauraronsa, dakyar yasamu karfin yin magana,

"So nake ku sanarwa da baba yaje gidansu Bilkisu tsohuwar matata ta ya tambayar min izinin aurenta... Wai tunda jimawa suka rabu da tsohon mijinta nikuma wallahi har yanzu.... Ina.... Sonta..." Kai idan kaji yadda yakarasa maganar sai yabaka dariya amma su ayiyah basuyiba domin sun dake, nan kowa taci gaba da abinda takeyi babu wacce ta tanka masa har yakaraci zamansa yatashi yafita bai kara yimusu maganar ba suma basuce masa komai ba haka shima baba baice masa uffan ba shiyasa yafara tunanin kila su ayiyah basu sanar masa ba, tun yana daurewa har yasamu baba dakansa yayi kokarin yimasa maganar amma sai baba ya katseshi ta hanyar cemasa iyayensa mata sun yimasa maganar, nan mamaki ya ishi fahad, jin wai ashe baba yasani amma yayi shiru, shi dinma shirun yaci gaba dayi yana addu'a.

Bayan sati daya da faruwar lamarin ranar asabar yana kwance dasafe yana bacci kasancewar babu aiki Abba yashigo yana tashinsa, yana bude ido abba yace masa,

"Baba yace katashi kashirya zamu rakashi anguwa anjima..."

Duk haushi yaji ya kamashi haka kawai yana baccinsa mai dadi Abba yakatse masa saida yagama nuku nuku da kunbiya kunbiyarshi sannan yatashi yayi wanka ganin irin shigar da Abba yayi harda babbar riga yasashi shima kwaikwayon shigar abban ko ba komai babbar rigar zatayi masa maganin sanyi, kasancewar sanyine basubar gidaba sai bayan azahar su shidane acikin motar da baban salim da baba sai salim din da fahad gaban motar kuma ya baffane ke driving ya abba na zaune gefenshi,shi dai fahad nata son ya tambayi inda zasuje amma babu dama domin da ya tambayi salim cikin rada ma cewa yayi shima wallahi bai saniba, tafiya sukayi mai nisa shidai sai yaga kamar yasan garin amma kuma gaskiya yakasa tunowa sosai yadda yakamata. Karfe uku da wani abu suka karasa babbar fada wacce ke girke tsakiyar garin sai lokacin fahad yatuna garin ashe garko ne garinsu Bilkisu domin aurensu nafarko anan aka daurashi,

"To amma me mukazo yi nan kuma? Ko rasuwa akayi musu?"

Wannan tambayar ita yake ta yiwa kansa har suka shiga ciki inda jama'a ta dan taru amma kuma mutanen basuda wani yawa sosai, daga can baya suka zauna shida salim sukuma su baba suka wuce can gaba, tsawon mintuna goma aka dauka ana gaishe gaishe kafin daga bisani aka fara daurin aure, sudai su fahad basa jiyo abinda ake fada bayan kamar mintuna biyar aka gama daura aurenshi da Bilkisu batareda yasaniba akan sadaki naira dubu talatin aka daura auren wanda baba shine yabada sadakin, kiransu ya Abba yazo yayi nan suka karasa gaban manya shidai yaga anata nunashi amma bai san daliliba saida suka fito bayan sun gama gaishe da manyan sannan yake tambayar Abba dalilin nunashin da aka yitayi aciki,

"Ango ake tambaya shine aka nunaka saboda wasu sun zaci wai nine..."

"Ango kuma? Wai auren wa mukazo ne?"

"Aurenka da Bilkisu mana...,congratulations lil bro...."

Jin abinda yace yana dafa kafadarsa yadaure masa kai shida salim, saida sukayi sallar la'asar aka fito musu da abinci sannan sukayi haramar tafiya, goro da alawa da dabino aka kawo musu fal aka saka abayan mota,suna kokarin shiga cikin mota su baba suka karaso fuskarsu dauke da fara'a hannunsa cikin na abbansu Bilkisu suna sake yin doguwar musabaha......

*_Ummi Shatu_*

*FARIN GANI*

*Wannan littafin na siyarwane me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*

41***Shi dai fahad har suka bar cikin garin garko sukayi tafiya mai nisa bai bar mamakin abinda ke faruwa ba jinsa yake kamar acikin mafarki gaba daya lamarin yadaure masa kai, yana so yayi tambaya amma yana jin kunyar kar su baba suga rashin kunyarsa, shiru yayi kawai ya lumshe idanuwansa yana sauraron hirar su baba wadda mafi yawanta akan irin halin dattako da karamcin abbansu Bilkisu ne, godewa Allah yake tayi acikin zuciyarsa domin yasan shine yayi masa wannan gatan yasake aura masa Bilkisu akaro na biyu. Daf da lokacin sallar magriba suka shiga cikin garin kano, murnarsa bazata taba kwatantuwa ba a wannan lokaci, ko cikin gida bai shiga ba yawuce dakinsu yabar ya Abba da salim da aikin shigar da kayan daurin aure cikin gida, wanka yafara yi da ruwan sanyi domin yanzu ko sanyinma sai yaji yadaina ji shifa yanzu jinsa yakeyi tamkar anzare masa wata doguwar kaya daga cikin jininsa, yana fitowa yatarar har Abba yafita masallaci haka shima salim baya nan may be ko yatafi gida kokuma yaje salla, agurguje shima yashirya dan gudun kada yarasa jam'i.

Bayan an idar da salla tareda salim suka koma dakinsu domin yana son dauko wayarshi wadda yabari acan bayan yayi wanka,

"Abokina wai tayaya duk wadannan abubuwan suka faru cikin sauki haka....?" Salim yafada yana dafe da kafadar fahad wanda yasha kananun kaya,

"Wallahi salim nima ban saniba... Gaskiya su baba sun shammaceni saboda ban taba zaton zasu aminceba duba da yadda sukayi biris da maganar bayan na sanar dasu..."

Dariya salim yayi,

"Ashe babban shiri suke yimaka..."

"Kabari kawai abokina... Babu abinda zamuce da iyayenmu sai dai muce Allah yakara musu nisan kwana sannan yayi musu sakayya da gidan aljannah... Aljannar ma jannatul firdaus..."

"Amin amin... Tofa yanzu kai kakusa zama mai mata biyu tunda ga husnanka agefe tana jira"

"Ai yanzu ma wurinta nakeso ka rakani...."

"Wa? Ni? Tab ai wallahi babu ni awannan tafiyar... So kake tayi fushi dani saboda narakaka ka fada mata kayi mata kishiya, last time ma dani mukaje, gaskiya bazanje ba, saboda wallahi sai tayi tsammanin ko ni ke zugaka..."

"Zuga kuma? Kajika da wani zance kuma, shikenan tunda bazaka jeba, ni bari naje"

"Allah yakiyaye hanya... Bani aron laptop dinka, wanna surprise u....."

"Kasan inda take ai kaje ka dauka..."

Turare yakara feshe jikinsa dashi sannan yadauki rigar sanyi yadauki wayarshi yafita yana duba wayar tashi cikeda mamaki ganin miss calls har guda biyar yana dubawa yaga maama ce cikeda fara'a yayi calling dinta back bugu uku yaji ta daga tana dariya,

"Ango ko duk kacaniyar fama da jama'arce haka?"

"A'a Maman hudah, naje salla ne wallahi, sai kuma kikaji abu ko?"

Dariya tayi cikin farin ciki tace,

"Wallahi fa, Allah yasanya alkhairi yabada zaman lafiya..."

"Amin maama, nagode sosai"

Sai da ta dan kara tsokanarshi sannan sukayi sallama ya ajiye wayar kawai tunanin da yake tayi shine ko har yanzu Bilkisu tana nan ayanda take kokuma ta canja?

"Hmmm may be tayi kiba ko kuma ta rame... Kila tayi haske ko kuma fatarta na nan kamar da..." Yafada yana tuki murmushi kwance kan fuskarshi, yau jinsa yake kamar yana yawo akan iska saboda farin ciki, saida yakusa isa gidansu husnah sannan yakirata awaya yace mata gashi nan zuwa shiyasa kafin yaje har tagama shiryawa taci kwalliya tana ta zuba kamshi cikin doguwar riga ta material, inda suka saba zama suyi hira idan yazo yauma acan suka zauna kan daddumar data shimfida musu, yanata janta da wasa yana fara'a irin wacce tajima bata ga yayiba sai abun yabata mamaki har tagagara yin shiru,

"Ya fahad wannan fara'ar fa? Gist me pls..."

Murmushi yayi ya gyara zamanshi yana wasa da agogon dake daure a hannunshi, gaba daya bai san ta yaya zai sanar da itaba amma yazama dole yafada mata saboda baya son yafara munafurtatta tun daga yanzu,

"Yanmata na kin san me? Ur aunt is back...."

Daga idanuwanta tayi ta kalleshi fara'ar dake kwance kan fuskarta tana gushewa,

"Which aunt? Banfa ganeba..."

"I mean matata...."

Shiru yaji tayi batace komai ba zuwa can kawai tamike tana karkade jikinta,

"Allah yasanya alkhairi yakuma baku zaman lafiya...."

Da sauri shima yamike ya rikota,

"Haba husnah... Dan Allah kar kiyi fushi... Kiyi hakuri kinji, ki tsaya ki saurareni..."

Idanuwanta dake kokarin kadawa izuwa launin ja ta zuba masa,

"Ni kaji nace kayi min laifine? Dama nasan itace aranka, ita kakeso kake kauna to kuma menene sabo aciki wanda ban saniba? Ni dama ba sona kakeyi ba ita kakeso nikuma nake yin son maso wani..."

Hannuwanta dake cikin duka nashi yarike gam yasake matsewa,

"Husnah wallahi Allah kema ina sonki... Meyasa zakice ita nakeso? Wannan auren fa nikaina wallahi ban san dashiba sai dazun nan... Haba yanmata na"

Wata harara ta watsa masa acikin duhun da suke sannan cikin fada tace,

"Sakar min hannu, kaje kayita zama da matar taka.... Nidai kasani nafasa aurenka saboda bazan taba zama tareda itaba....."
Chapter 43 · 0% Book details