← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 67

Sashe 19

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Yi hakuri..." Daga haka yawuce zai shiga bathroom,kunkunin nasa yasoma yi shi kadai,

"Haka kawai kin saka mutane sun makara sallar asubah dan kawai kin san ke bayi zakiyi ba....."

"Magana kakeyi ne?"

"A'a..." Daga haka yafada toilet yayi alwala yafito bayan yayi brush, tana sanye da hijab har kasa da towel daure ajikinta tana gyara kan gadon, dan tabe baki yayi ya dauki rug din salla ya shimfida yatada salla, ita kuwa saida tagyare kan gadon tsaf sannan tawuce toilet domin yin wanka da kallo yabita sannan yamaida kallonshi saman gadon cikin kunkuni yace,

"Gashi dai mun dawo daya dake da kika kwana wajen kwanan mutum biyar da ni da na kwana awurin kwanan mutum biyu..."

Yana kan abin sallar azaune har tafito, handbag dinta ta dauka tanufi drewar tana cemasa,

"Dan bani wuri zan shirya..."

Mikewa yayi baice komai ba yanade prayer rug din ya ajiye saman bedside drewar yafita azuciyarshi yana cewa,

"Oho dai tunda nasan me za ayi har ake wani korata..."

Kwanciyarshi yayi saman doguwar kujera bai san lokacin da wani baccin yasake daukeshi ba. Ita kuwa bayan ta shirya wani material ta saka peach tasa sarka da dan kunne golden sannan tasaka abun hannu da agogonta na gold wanda ammah ta siyo mata last year da taje umarah, turarenta na garari na fitina tabi ta bazawa jikinta sannan tafito domin yanzune zata yiwa gidan kallon tsaf kasancewar safiya tayi dan harma rana tafito, fahad tagani kwance yana bacci nan kuma ga shimfidarsa ta daren jiya, tattara komai tayi ta dauke mattress din takai daki tazo ta kwashe sauran suma takai daki sannan tasake fitowa, ta kofar kitchen ta fita baya ta dudduba gidan wanda yake dan cicif sannan tadawo ciki sai lokacin ta lura da buhun Irish potatoes dake jingine acikin kitchen din, dayake anrigada anhada mata cylinder din gas dinta tukwane kawai tafara lalubowa dama cooker gas dinta babu ruwanta da neman ashana wurin kunnashi nan ta kunna ta dora ruwan zafi.

Dankali ta fere wanda zai ishesu su biyu ta soya bayan ta juye ruwan zafin acikin tea flask, da kwai ta hada tayi masa kyakkyawar suya yabada kala mai kyau dama bata da matsalar kayan kamshi da kayan dandano komai gashi nan a ajiye sai dai kawai ta dauka, hatta dakakken yaji gashi nan cikin karamin plastic haka su kuka,daddawa, kubewa etc duk su maama saida suka harhada mata aka dako sannan aka kawo mata, fridge din dake cikin kitchen din taduba kamar tasan yayi ajiya nan taga balangu da yoghurt da kayan marmari danginsu tufa, kankana da ayaba, balangun taciro tasaka acikin oven ta dumama bayan takara masa kayan hadi, saida ta kammala hada abin karyawarta tsaf sannan ta dauko ta kawosu kan dinning mai dauke da kujeru kwaya hudu,kayan tea dinma da alama babu dan haka tafasa shan ruwan zafin taci iya balangunta da chips din data soya. Tana daf da gamawa taga andawo da wuta mikewa tayi tanufi daki domin jona wayarta a charge da alama shima fahad yatashi domin bata ganshi awurin da tabarshi yana bacciba,akan gadonta taganshi yana cigaba da baccinshi,

"Wannan ko yasha wani abune? Bacci yaki karewa? Uhmm"

Ita kadai take maganarta tana kokarin saka wayarta a charge, handbag dinta ta dauko ta zazzage kudin data samu tafara shiryasu domin wasu yan dari darine sabbi fil wasu yan dari bibbiyu wasu kuma yan dari biyar biyar harda yan hamsin hamsin ma, hakura tayi da shiryawar tasake gwamutsasu ta maida cikin handbag din taje ta ajiye tafita falo, daga can tayi waje, flowers din da aka shuka sunyi masifar kyau ga kuma wasu kananan shukoki nan da suka dan fara fitowa kamar bishiya duk da dai bata gane menene ba,abakin slave din pop din kofar falon nasu ta zauna,

Gajiya tayi da zaman wajen tasake diba takoma cikin falon ta zauna, tana nan zaune yafito sanye da blue din shadda yana balle links din hannun rigar,

"Hajjaju barka da safiya?"

"Yawwa, katashi lafiya?"

"Lafiya lau, ya kwanan kadaici?"

Banza tayi dashi tamaida hankalinta kan agogon dake manne jikin bangon falon wanda yake tafkeken gaske mai dauke da hoton abbansu ajiki,

"Babu kayan tea ko? Bari naje nasiyo yanzu"

"Babu amma ai ga breakfast can na hada"

"Haba ranki yadade daga zuwa sai girki? Shikenan godiya nake"

Bai jira cewarta ba yayi dinning area din yazauna yaci abincin yayi dam dan babu abinda yarage yana gamawa yayi mata sallama yafice, wani takaicine kuma yafara ziyartarta shi yayi ficewarsa yanzu hakama gidansu yatafi amma ita gashi nan yabarta agida ita kadai gashi kuma tamanta ta tambayeshi taji ko anhada mata kayan kallonta, daki ta koma ta zare wayarta daga sucket ta kunna data ta fada yanar gizo wai ko zata rage zaman kadaici......

*Book dina na kudine dan Allah idan har baki biyaba karki karanta.*

*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO*

*KAMAR DA WASA...!*

_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*

*20*

***Fahad lokacin da yafita saida yafara zuwa gidansu yagaida su ayiyah yayi musu ban gajiyar biki sannan yawuce kasuwa duk abinda suke bukata na amfanin gida saida yasiyo daga karshe ya iyo cefanenshi na abincin rana ya hado kayan tea sannan yanufi gida, lokacin har bilkisu tagaji da chaten dinma ta kashe data tana kwance tarasa abinda yake yimata dadi, kitchen yakai kayan gaba daya ya ajiye mata sannan yanufi bedroom, akwance yaganta kamar marar lafiya tayi shiru,

"Hajjaju yadai?"

"Yawwa dan Allah wai ba ahada kayan kallon can bane?"

"Anhada mana.... Zo kigani"

Tashi tayi tabishi zuwa falo nan yajona komai saiga tashar mbc Bollywood takawo darr, ajiyar zuciya tasauke harta dan ji dadi ai kalloma ba karamin rage kadaici yakeba, yana debewa mutum kewa sosai sai yau tayarda,

"Ga kaya can a kitchen ni Zan fita.."

"Ina zaka fita? Ni kadai zan zauna agidan? Wallahi a'a kaima neman wuri zakayi mu zauna tare..."

Kujerar dake makotaka da tata yaje ya zauna, yana zama wayarshi na yin kara, cirota yayi yaduba nan yayi dariya ya daga,

"Allah yabar babban yaya, har ka tafi ne?"

Bata jin me ake cewa amma dai taji yace,

"Ehh to shikenan sai kazo"

Saida yakatse wayar sannan yajuya ya kalleta,

"Ya Abba ne wai zai koma school amma zai fara biyowa tanan kugaisa tukunna"

"To babu damuwa Allah yakawoshi lafiya"

Tashi tayi zuwa kitchen tana ware kayan da yakawo wanda zata barsu a kitchen din tabarsu anan wanda zata kai toilet ta kwasa takai sannan kayan tea din kuma takai dining area ta zuba cikin wani glass da aka tanada musammsn domin ajiya,

Saboda taji zaiyi bako shiyasa ta dora girkin da wuri sannan takoma falo ta iskeshi yana kallon spider man atashar mbc max, tana zama sukaji knocking, shine yaje yabude, khulsum ce kawarta bata hanya yayi yana cewa,

"Barka da zuwa hajiya khulsum"

"Yawwa haji fahad, ya kwanan amarya?"

Saida suka shigo cikin falon sannan ya amsa da,

"Gata nan muna bata hakuri, bai zauna ba yawuce bedroom yabar musu falon"

Kallon khulsum bilkisu tayi,

"Kekuma sai yanzu kika gadamar zuwa?"

"Kai labour yanzun bakiyi maraba da ganina ba?"

"Oho miki, ya gajiyarki?"

"Ahh gajiya ai tana tare dake hajiya, ni ai tajima da bin lafiyar jikina"

"Nima haka..."

"Gaskiyane amarsu, me kike tafasawa ne haka?"

"Wallahi girki ma na dora gashi can wai zanyi jalop din shinkafa..."

"To muje mana mu karasa, ah tashi muje"

Tare suka shiga kitchen din khulsum ta tayata suka hada komai, kayan marmarin da yakawo jiya sukayi blending dinshi suka hada banana milk shake suka saka a fridge basu kai ga sauke abincin ba Abba yazo fahad yafita yashigo dashi, kamarsu daya da fahad kuma kusan kansu ma daya dayake shima fahad din dogo ne, a falon suma suka zauna amma bilkisu tun kafin su shigo tasako hijab dinta har kasa wanda hakan ba karamin dadi yayiwa fahad ba. A mutunce suka gaisa sai lokacin takara raina girman fahad saboda koshi abban tagirmeshi kai dakyar ma idan maama kanwarta bazata fishi ba, mikewa Abba yayi zai tafi saboda yana son ya isa Maiduguri da wuri amma suka hanashi tafiya wai sai yatsaya yaci girkin amarya, dan dole yatsaya su bilkisu sukaje suka shirya table sannan tazo tace musu,

"Bismillah..."

"To godiya nake amarya" inji ya Abba,

"Ah babu komai..." Tafada tana murmushi,

"Ni gaskiya...ni gaskiya ban ganeba, ni meyasa ba agataleni" fahad yafada yana bata fuska kamar zaiyi kuka,

"Kai ai yanzu kagirma" Abba yafada cikin sigar tsokana,

"Allah ban yarda ba"

Daga bilkisu har Abba dariya sukayi ita dai tafiya tayi tabarsu saboda taga dramar tasu ba mai karewa bace kuma da alama sun saba, cikin bedroom suka shige itada khulsum suka basu waje suma suka kai nasu can, suna cin abincin khulsum na sake yimata tsiya har suka gama daidai lokacin shima fahad ya leko yace sun gama Abba zai tafi, hijab tasaka tafita sukayi sallama takoma wurin khulsum, shima fahad ta can yawuce bayan yaraka Abba, majalissar shayinsu yatafi wacce suke zama idan sun taso daga shago amma shi bawani ma cika zama yayiba sosai domin daga shago sai filin ball. Acan gidan amarya kuwa bayan fahad sun fita tareda abba babu jimawa su yaya asabe suka zo itada Anty Fauziyya fuska asake bilkisu ta karbesu takawo musu abinci da lemon da suka hada kuma babu laifi ta saki jiki da su kamar yadda suma suka sake da ita, suna nan tare sunata kallo suna hira har maman hudah tazo wato maama takawowa bilkisu kayan tarbar baki wanda yahadar da cincin, cake, alkaki sai nakiya da dubulan an dan samu tsaiko ne matar da aka bawa tayi bata gamaba sai jiya da daddare ta aiko dashi amma da tuni anjima da kawo mata,

"Ina daughter dina naganki ke daya??"

Dariya maama tayi ta zauna kan kujera suna gaisawa da su Anty Fauzy,

"Daughter ki yau tana wurin kakarta can nabarta,ya fahad baya nanne?"
Chapter 19 · 0% Book details