Sashe 50
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mikewa yayi daga kan bedside drewar yaje yatsaya mata aka dukkan hannahensa yasaka su cikin aljihu,
"Kifara sanar dasu Abba irin zaman da mukayi dake dafarko da irin gangancin da kika sakani nayi harna sakeki lokacin da wannan shedanin tsohon dan duniyar yake tsaka da hure miki kunne, sannan sai kisake fada musu abinda ke faruwa ayanzu idan har kikayi haka to wallahi zan yimiki yadda kike so...."
Sosai kalamansa suka bata haushi ta lura yanzu baida magana saita hamood magana daya sai ya jefo hamood aciki, takasa gane tsakanin shi da hamood waye yafi wani tsanar dan uwansa saboda shima hamood din lokacin da tana gidansa baida magana sai ta ya kira fahad da karamin yaron nan marar kunya, shi kuma fahad yanzu magana kadan zaice tsohon dan duniya,tana can duniyar tunani har fahad yawuce yabar mata dakin yayi tafiyarshi kawai sai bude ido tayi taga baya nan,
Tagumi ta rafka tana tunani, ai ko giyar wake takesha bazata taba gigin aikata wannan abun da fahad yafada ba, ai idan ta kuskura abba yaji cewar itace ta kashe aurenta karo nafarko dan ta auri hamood wallahi kashinta yabushe,
"Ai yanzu bakida mafita banda wacce tawuce kiyi hakuri ki zubawa sarautar Allah ido...." Zuciyarta tafada mata, shiru tayi kawai tana tunani, yanzu ita shikenan haka zatayi rayuwarta da yaro karami wanda baya ganin girmanta? Tunfa daga yanzu ya rainata to inaga wani abu ya hadasu ai sunanta sorry kawai, tsaki taja takoma ta kwanta tana istigfari acikin zuciyarta.
Tun daga ranar har takarasa warwarewa takoma aiki fahad bai sake zuwa gidanba ita anata bangaren hakanma yafi mata kwanciyar hankali saboda baizo inda takeba bare yafada mata bakar maganar da zata hanata bacci kamar yadda yasaba, kokari ma take tayi tasamu ta yakice matsalarshi daga zuciyarta. Shi dinma yayi hakanne domin yabarta ta sarara kuma ta huta sannan shima aiki yasakoshi gaba koda yaushe cikin aiki suke mutum baida lokacin kansa,
Ana saura kwana uku abbanta zai dawo daga tafiyar da yayi masu hayar gidan fahad suka tashi wato wadannan turawan da suka karbi gidanshi dama already sun gyara gidan sai dan gyare gyaren da baza arasa ba. Ranar laraba da daddare Abba yasauka wanda da tunima yajima da dawowa dan dai kawai yabiya ta wurinsu elmustapha ne yagansu, dawowarsa da kwana biyu fahad yarako babansu domin yiwa Abba sannu da zuwa dama awurin maama yake jin komai yanzunma itace tasanar dashi dawowar Abba,
Tunda fahad yagaida Abba yakoma gefe ya zauna yana saurarensu suna tattaunawa cikin fahimtar juna da mutuntawa, ahaka ammah tazo ta samesu suka gaisa ta fita, babu jimawa saiga Bilkisu itama tasha dogon hijabi har kasa,durkusawa tayi ta gaida baba sannan tamike zata fita, hada ido sukayi da fahad ta harareshi wannan karon bai ramaba amaimakon hakama sai yayi murmushi kawai, bayan fitarta ya maida hankalinsa kan maganar da su Abba sukeyi inda abban yake cewa tunda yadawo ai sai ayi maganar tarewar Bilkisu agidanta, dan haka idan har babu matsala nanda sati biyu sai ta tare agidanta nan baba yace babu kuma anyi abu akan gaba saboda dama mutanen da suke zaune agidan fahad din sun fita dan haka ko gobe ake son tariyar babu damuwa, anan dai aka bar zancen azuwan nanda sati biyu zata tare saboda abata dama ta gabatar da dan shirye shiryenta da take son gudanarwa.
Fahad sun bar gidansu Bilkisu cikeda karramawa ga uban kayan tsaraba da Abba yabawa baba, washe gari fahad yasoma gyara gidansa gashi a lissafinsa bazaifi sati daya da tariyar ba zai koma makaranta, haka dai yake ta kaiwa da kawowa danma yayunshi na taimaka masa.
Bilkisu kuwa tun lokacin da abba yasanar da ita maganar tariyar nan take cikin kunci, kullum cikin fushi take hatta khulsum saida ta fahimta har saida ta tambayeta meke faruwa nan ta sanar da ita wai tarewa zatayi nanda yan kwanaki dariya khulsum tayi tace,
"To ai ke gata ma akayi miki wannan uban sanyin dake tunkaro duk wani mai rai ai zakifi more amarcinki tunda gaki ga mijinki.... Danma kun kwafsa kin yarda yayi miki ciki tun kafin ku tare..."
Harararta Bilkisu tayi sannan atunzure tace,
"Dallah ni tashi muje news ko intafi inbarki, ke kika san wani ciki ni ban sanshi ba"
Daga haka tafigi handbag dinta tayi gaba tanata masifa aranta ita daya.
Cikin kwanaki kadan aka gama gyarawa fahad gidansa wannan karon kam komai gaban kansa yakeyi babu maganar tambayar ra'ayin Bilkisu kamar wancan, duk abinda yayi masa shi yakeyi yanzu, babu karya gida yafito yayi das dashi kowa yagani yasan gidan amarya ne, kwana biyu atsakani su maama sukazo da motar kaya aka soma shirya mata kayanta aciki komai sabone fil aledarshi, yana shirin baro cikin asibiti maama tayi masa waya tana tambayarsa wai duka bedrooms din guda biyu nasune?
Dariya ma shi abin yabashi shiyasa bayan sun gama yarawa da maama yakira Bilkisu wadda rabonshi da ita tun sati biyu da suka wuce, har wayar ta tsinke bata daga ba wannan dalilinne yasashi tura mata text massage.
Tun tana cikin bathroom tana wanka take jiyo karar wayarta amma bata fitoba saida tagama tana zuwa taga miss called da massage guda daya massage din tabude bayan ta duba miss called din,
_Ki fadawa kannenki su zaba miki daki guda daya, dayan kuma subarshi empty saboda na matata ne...._
Ganin abinda ya rubuto mata yasata zama agefen gadon tana huci azuciyarta tana tambayar kanta wai ita zai hada da matarshi agida daya? Ai kuwa sam wannan abune wanda bazai taba yuyuwa ba....
*_Ummi Shatu_*
*Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
47**** Kamar a mafarki sai taji abun na damunta, akan me zaice zai hadata da wata agida daya? Ai wallahi bazata taba sabuwa ba idan har yadamu da dole sai yayi auren to sai dai ya nemawa matar tasa wani gidan amma ba wannan ba, cikeda masifa ta jawo wayarta wadda ta cillar kan gado saboda takaici, maama takira amma har ta katse bata dagaba dan haka ta kira meenah wannan dinma saida tayiwa meenah kira biyu sannan Hindu ta daga,
"Meenah kar ku wani bar empty bedroom duka ku saka min kayana ako ina dama ai gado biyu ne ko? So kuyi min jerena ako wanne daki...."
Bata ma jira taji maganar Hindu ba ta katse wayar saboda ita duk atunaninta meenah ce, dukansu dariya abun yabasu lokacin da Hindu ke kora musu labarin fadan da taji Bilkisu nayi,
Ita kam cikin fada da masifa take yin komai tana shiryawa sai babatu takeyi ita kadai,
"Can da iyawarku kaida matar taka...., nidai abinda nasani shine bazai taba yuyuwa ka hadani da karamar yarinya ba salon tazo ta rainani...., kuje can ku karata ka kaita duk inda zaka kaita wannan damuwarku ce ba tawa ba..."
Ahaka ta gama shiryawa tasaka blue din material fitted gown tana daura dan kwali tajiyo karar wayarta, zuwa tayi ta dauka tana ganin fahad ne tayi tsaki ta sake jefa wayar saman gado tafita daga dakin ma gaba daya zuwa dakin ammah wacce ke zaune tana waya da Rabi mai aikinta tana sake karanta mata abubuwan da zata sake hado mata daga kasuwa, zama tayi tana sauraron ammah har tagama wayar ta sauketa daga kunnenta,
"Ammah kunyi waya ne dasu maama?"
Kallonta ammah tayi tana danna wayarta,
"Meya faru?, munyi waya dasu dazu nace musu subar gado daya su saka miki daya saboda wai yace daya dakin idan matarsa tazo anan zata zauna..."
Bata rai Bilkisu tayi kamar karamar yarinya tasoma magana cikin damuwa,
"Kuma shikenan ammah dan matarsa zata zauna aciki ni sai afasa saka min gado biyuna? Ni wallahi yanemi wani gidan yakaita can..."
Girgiza kai ammah tayi tana kallonta,
"Wai dan Allah sai yaushe zaki girmane mai gado? Mijin naki nawa yake da har zakice yayi gida biyu? Shida ba aiki yakeyi ba shine zakice yanemi wani gidan? Kinga.... Tam, maza dai kibari wannan maganar taje kunnen abbanku.... Zakiyi masa bayani nidai babu ruwana..... Karki bari nasake jin wannan maganar kinji dai nafada miki..."
Jin abinda ammah tace yasata sake jin bacin rai ya rufeta yanzu shikenan babu mai goyon bayanta? Haka zata zauna gida daya da karamar yarinya amatsayin kishiyarta? Tun daga lokacin take ta fushi, fushi takeyi da kowa,komai su maama sukace tayi sai tace baza tayiba, kunshi, kitso, gyaran kai duk taki yi bare asa ran zatayi gyaran jiki. Ana saura kwana uku ta tare hajiya iyallo tazo amma wannan karon ita kadai tazo ko yafindo mai gado basu taho tareba wai tana can tana kula da jikokinta wadanda aka yiwa shayi har su shida, ko kadan Bilkisu bata so zuwan iyallo ba wannan karon kamar waccan saboda yanzu abubuwan da iyallon takawo ita ba amfani zatayi dasu ba, kuma haka kawai sai inzauna inta dirkar kayan gyaran jiki saboda wannan yaron? Haka take ta tambayar kanta, tsumi ne hadadde irin na mutanen kauye sai tukudi da gumba amma fafur taki sha sai su maama ne suka rabe atsakaninsu. Lokacin da khulsum tazo kuwa saida suka yi fada da Bilkisu saboda takawo mata hadin kankana da kwakwa sannan kuma tace mata yakamata suje ayi mata kitso da kunshi amma tayi biris, tabe baki khulsum tayi tace,
"Duk dai wannan zille zillen da kikeyi bashi zai hana mu mikaki gidanshi ba jibi ehe... Kuma dole abashi hakkinsa ta dadin rai idan anki kuma ya kwata ta karfin tsiya....."
Shiru Bilkisu tayi bata kulata ba taci gaba da abinda takeyi, nan tasake jiyo maganar khulsum tana cewa,
"Badanma ina tausayawa mutum ba kar dan karamin cikin dake jikinsa ya zubeba ai wallahi da sai na zuga fahad yayiwa mutum lisss..."
"Wai ke kika yimin cikin? Ni kidaina jamin jaraba malama..."
"Kifara sanar dasu Abba irin zaman da mukayi dake dafarko da irin gangancin da kika sakani nayi harna sakeki lokacin da wannan shedanin tsohon dan duniyar yake tsaka da hure miki kunne, sannan sai kisake fada musu abinda ke faruwa ayanzu idan har kikayi haka to wallahi zan yimiki yadda kike so...."
Sosai kalamansa suka bata haushi ta lura yanzu baida magana saita hamood magana daya sai ya jefo hamood aciki, takasa gane tsakanin shi da hamood waye yafi wani tsanar dan uwansa saboda shima hamood din lokacin da tana gidansa baida magana sai ta ya kira fahad da karamin yaron nan marar kunya, shi kuma fahad yanzu magana kadan zaice tsohon dan duniya,tana can duniyar tunani har fahad yawuce yabar mata dakin yayi tafiyarshi kawai sai bude ido tayi taga baya nan,
Tagumi ta rafka tana tunani, ai ko giyar wake takesha bazata taba gigin aikata wannan abun da fahad yafada ba, ai idan ta kuskura abba yaji cewar itace ta kashe aurenta karo nafarko dan ta auri hamood wallahi kashinta yabushe,
"Ai yanzu bakida mafita banda wacce tawuce kiyi hakuri ki zubawa sarautar Allah ido...." Zuciyarta tafada mata, shiru tayi kawai tana tunani, yanzu ita shikenan haka zatayi rayuwarta da yaro karami wanda baya ganin girmanta? Tunfa daga yanzu ya rainata to inaga wani abu ya hadasu ai sunanta sorry kawai, tsaki taja takoma ta kwanta tana istigfari acikin zuciyarta.
Tun daga ranar har takarasa warwarewa takoma aiki fahad bai sake zuwa gidanba ita anata bangaren hakanma yafi mata kwanciyar hankali saboda baizo inda takeba bare yafada mata bakar maganar da zata hanata bacci kamar yadda yasaba, kokari ma take tayi tasamu ta yakice matsalarshi daga zuciyarta. Shi dinma yayi hakanne domin yabarta ta sarara kuma ta huta sannan shima aiki yasakoshi gaba koda yaushe cikin aiki suke mutum baida lokacin kansa,
Ana saura kwana uku abbanta zai dawo daga tafiyar da yayi masu hayar gidan fahad suka tashi wato wadannan turawan da suka karbi gidanshi dama already sun gyara gidan sai dan gyare gyaren da baza arasa ba. Ranar laraba da daddare Abba yasauka wanda da tunima yajima da dawowa dan dai kawai yabiya ta wurinsu elmustapha ne yagansu, dawowarsa da kwana biyu fahad yarako babansu domin yiwa Abba sannu da zuwa dama awurin maama yake jin komai yanzunma itace tasanar dashi dawowar Abba,
Tunda fahad yagaida Abba yakoma gefe ya zauna yana saurarensu suna tattaunawa cikin fahimtar juna da mutuntawa, ahaka ammah tazo ta samesu suka gaisa ta fita, babu jimawa saiga Bilkisu itama tasha dogon hijabi har kasa,durkusawa tayi ta gaida baba sannan tamike zata fita, hada ido sukayi da fahad ta harareshi wannan karon bai ramaba amaimakon hakama sai yayi murmushi kawai, bayan fitarta ya maida hankalinsa kan maganar da su Abba sukeyi inda abban yake cewa tunda yadawo ai sai ayi maganar tarewar Bilkisu agidanta, dan haka idan har babu matsala nanda sati biyu sai ta tare agidanta nan baba yace babu kuma anyi abu akan gaba saboda dama mutanen da suke zaune agidan fahad din sun fita dan haka ko gobe ake son tariyar babu damuwa, anan dai aka bar zancen azuwan nanda sati biyu zata tare saboda abata dama ta gabatar da dan shirye shiryenta da take son gudanarwa.
Fahad sun bar gidansu Bilkisu cikeda karramawa ga uban kayan tsaraba da Abba yabawa baba, washe gari fahad yasoma gyara gidansa gashi a lissafinsa bazaifi sati daya da tariyar ba zai koma makaranta, haka dai yake ta kaiwa da kawowa danma yayunshi na taimaka masa.
Bilkisu kuwa tun lokacin da abba yasanar da ita maganar tariyar nan take cikin kunci, kullum cikin fushi take hatta khulsum saida ta fahimta har saida ta tambayeta meke faruwa nan ta sanar da ita wai tarewa zatayi nanda yan kwanaki dariya khulsum tayi tace,
"To ai ke gata ma akayi miki wannan uban sanyin dake tunkaro duk wani mai rai ai zakifi more amarcinki tunda gaki ga mijinki.... Danma kun kwafsa kin yarda yayi miki ciki tun kafin ku tare..."
Harararta Bilkisu tayi sannan atunzure tace,
"Dallah ni tashi muje news ko intafi inbarki, ke kika san wani ciki ni ban sanshi ba"
Daga haka tafigi handbag dinta tayi gaba tanata masifa aranta ita daya.
Cikin kwanaki kadan aka gama gyarawa fahad gidansa wannan karon kam komai gaban kansa yakeyi babu maganar tambayar ra'ayin Bilkisu kamar wancan, duk abinda yayi masa shi yakeyi yanzu, babu karya gida yafito yayi das dashi kowa yagani yasan gidan amarya ne, kwana biyu atsakani su maama sukazo da motar kaya aka soma shirya mata kayanta aciki komai sabone fil aledarshi, yana shirin baro cikin asibiti maama tayi masa waya tana tambayarsa wai duka bedrooms din guda biyu nasune?
Dariya ma shi abin yabashi shiyasa bayan sun gama yarawa da maama yakira Bilkisu wadda rabonshi da ita tun sati biyu da suka wuce, har wayar ta tsinke bata daga ba wannan dalilinne yasashi tura mata text massage.
Tun tana cikin bathroom tana wanka take jiyo karar wayarta amma bata fitoba saida tagama tana zuwa taga miss called da massage guda daya massage din tabude bayan ta duba miss called din,
_Ki fadawa kannenki su zaba miki daki guda daya, dayan kuma subarshi empty saboda na matata ne...._
Ganin abinda ya rubuto mata yasata zama agefen gadon tana huci azuciyarta tana tambayar kanta wai ita zai hada da matarshi agida daya? Ai kuwa sam wannan abune wanda bazai taba yuyuwa ba....
*_Ummi Shatu_*
*Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
47**** Kamar a mafarki sai taji abun na damunta, akan me zaice zai hadata da wata agida daya? Ai wallahi bazata taba sabuwa ba idan har yadamu da dole sai yayi auren to sai dai ya nemawa matar tasa wani gidan amma ba wannan ba, cikeda masifa ta jawo wayarta wadda ta cillar kan gado saboda takaici, maama takira amma har ta katse bata dagaba dan haka ta kira meenah wannan dinma saida tayiwa meenah kira biyu sannan Hindu ta daga,
"Meenah kar ku wani bar empty bedroom duka ku saka min kayana ako ina dama ai gado biyu ne ko? So kuyi min jerena ako wanne daki...."
Bata ma jira taji maganar Hindu ba ta katse wayar saboda ita duk atunaninta meenah ce, dukansu dariya abun yabasu lokacin da Hindu ke kora musu labarin fadan da taji Bilkisu nayi,
Ita kam cikin fada da masifa take yin komai tana shiryawa sai babatu takeyi ita kadai,
"Can da iyawarku kaida matar taka...., nidai abinda nasani shine bazai taba yuyuwa ka hadani da karamar yarinya ba salon tazo ta rainani...., kuje can ku karata ka kaita duk inda zaka kaita wannan damuwarku ce ba tawa ba..."
Ahaka ta gama shiryawa tasaka blue din material fitted gown tana daura dan kwali tajiyo karar wayarta, zuwa tayi ta dauka tana ganin fahad ne tayi tsaki ta sake jefa wayar saman gado tafita daga dakin ma gaba daya zuwa dakin ammah wacce ke zaune tana waya da Rabi mai aikinta tana sake karanta mata abubuwan da zata sake hado mata daga kasuwa, zama tayi tana sauraron ammah har tagama wayar ta sauketa daga kunnenta,
"Ammah kunyi waya ne dasu maama?"
Kallonta ammah tayi tana danna wayarta,
"Meya faru?, munyi waya dasu dazu nace musu subar gado daya su saka miki daya saboda wai yace daya dakin idan matarsa tazo anan zata zauna..."
Bata rai Bilkisu tayi kamar karamar yarinya tasoma magana cikin damuwa,
"Kuma shikenan ammah dan matarsa zata zauna aciki ni sai afasa saka min gado biyuna? Ni wallahi yanemi wani gidan yakaita can..."
Girgiza kai ammah tayi tana kallonta,
"Wai dan Allah sai yaushe zaki girmane mai gado? Mijin naki nawa yake da har zakice yayi gida biyu? Shida ba aiki yakeyi ba shine zakice yanemi wani gidan? Kinga.... Tam, maza dai kibari wannan maganar taje kunnen abbanku.... Zakiyi masa bayani nidai babu ruwana..... Karki bari nasake jin wannan maganar kinji dai nafada miki..."
Jin abinda ammah tace yasata sake jin bacin rai ya rufeta yanzu shikenan babu mai goyon bayanta? Haka zata zauna gida daya da karamar yarinya amatsayin kishiyarta? Tun daga lokacin take ta fushi, fushi takeyi da kowa,komai su maama sukace tayi sai tace baza tayiba, kunshi, kitso, gyaran kai duk taki yi bare asa ran zatayi gyaran jiki. Ana saura kwana uku ta tare hajiya iyallo tazo amma wannan karon ita kadai tazo ko yafindo mai gado basu taho tareba wai tana can tana kula da jikokinta wadanda aka yiwa shayi har su shida, ko kadan Bilkisu bata so zuwan iyallo ba wannan karon kamar waccan saboda yanzu abubuwan da iyallon takawo ita ba amfani zatayi dasu ba, kuma haka kawai sai inzauna inta dirkar kayan gyaran jiki saboda wannan yaron? Haka take ta tambayar kanta, tsumi ne hadadde irin na mutanen kauye sai tukudi da gumba amma fafur taki sha sai su maama ne suka rabe atsakaninsu. Lokacin da khulsum tazo kuwa saida suka yi fada da Bilkisu saboda takawo mata hadin kankana da kwakwa sannan kuma tace mata yakamata suje ayi mata kitso da kunshi amma tayi biris, tabe baki khulsum tayi tace,
"Duk dai wannan zille zillen da kikeyi bashi zai hana mu mikaki gidanshi ba jibi ehe... Kuma dole abashi hakkinsa ta dadin rai idan anki kuma ya kwata ta karfin tsiya....."
Shiru Bilkisu tayi bata kulata ba taci gaba da abinda takeyi, nan tasake jiyo maganar khulsum tana cewa,
"Badanma ina tausayawa mutum ba kar dan karamin cikin dake jikinsa ya zubeba ai wallahi da sai na zuga fahad yayiwa mutum lisss..."
"Wai ke kika yimin cikin? Ni kidaina jamin jaraba malama..."