← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 67

Sashe 27

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Bata saurareshi ba tafice daga dakin, binta da kallo yayi yana yimata dariya acikin zuciyarshi, dama ita kadai ake jira tana zuwa suka tafi,itada maryam da mariya aka sauke agidanta tana shiga wanka tafara yi sannan tayi sallar ishah domin batayi ba a asibitin acikin wannan daren takira maama da ammah duk ta sanar dasu rashin lafiyar fahad da asibitin dayake kwance ahalin yanzu sannan takira khulsum wacce har tafara bacci itama tasanar da ita, dayake jiya batayi isasshen bacciba shiyasa yau tunda ta kwanta bata tashiba sai da asubah duk da hakama ta makara sallah domin har masallatai sun jima da idarwa......

*Littafin kamar da wasa na siyarwa ne yar uwa idan har kinada bukata ki siya ki karanta domin yana dauke da dunbin darrusa na rayuwar da muke ciki yau, ka karanta halak dinka yafiye maka alkhairi akan karanta hakkin wani.*

*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO.*

*KAMAR DA WASA...!*

_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*

*25*

***Kitchen tashiga bayan ta idar da salla sukuma su mariya suna kokarin gyara mata gidan, saida ta shirya lafiyayyen abincinta tazuba a flask wanda zata kai asibiti sannan ta zubawa su mariya suka ci daga nan tabasu kudin napep saboda sai sun koma gida sannan zasu shirya su tafi makaranta danma dai sunyi wanka agidanta da sunje gida uniform kawai zasu saka, bedroom tashiga bayan ta sallami su maryam sun tafi, tana kokarin daura towel idonta yakai kan wayar fahad dake ajiye saman bedside drewar tana karar neman agaji, koda taje gaban wayar sunan husnah tagani ajiki nan wayar takatse wani kiran yasake shigowa, ko kadan bataji tana sha'awar daga wayarba har tayi tagama sai lokacin ta dauka ta jona masa a charge kasancewar akwai wuta. Wanka tashiga tayi tafito ta kintsa adan hanzarce sannan tayi breakfast kafin ta hada komai wanda zata tafi dashi tarufe gidan tatafi, shatar napep ta dauka yakaita har asibitin lokacin karfe bakwai da wurin rabi,iya ya abba ne kadai awurin da alama babu wanda yazo tunda yanzu garin yawaye, saida suka gaisa ta tambayi yamai jiki sannan tashiga ciki, idonshi akan kofa shiyasa tana shigowa idanuwansu sukayi arangama da juna, murmushi taga ya sakar mata kasalalle yana kwance rigingine kanshi tallafe bisa hannunshi na dama,

Har gaban gadon takarasa zata zauna, hannu yamika mata yakamo nata, zama tayi tana kokarin ajiye handbag dinta bayan ta dire kayan da tazo dashi. Kallonta yake tamkar yau yafara ganinta domin ba karamin haduwa yau dinnan tayiba, leshi ne ajikinta dark pink anyi mata gown tasha lafaya itama pink duk ta lullube jikinta, juyawa tayi ta kalleshi,

"Sannu yajikin?"

Daga mata kai yayi yana matsa mata yatsunta bata kai ga sake yin wata maganar ba Abba yashigo dauke da brush da toothpaste,

"Gaskiya mijinki jinyarsa akwai takurawa.... Ni yanzu ma gida zanje anjima zan dawo"

Murmushi bilkisu tayi ta dan karkatar da kai tana kallon fahad wanda idanuwanshi ke lumshe,

"Meya faru yayanmu?"

"Shifa idan yana ciwo nafarko bazaiyi bacciba sannan na biyu bazai ci abincin ba na uku bazai sha magani ba sannan komai sai anyi masa kamar wani jariri, yanzu gashi yanace sai ankawo masa brush kuma bari kigani ko yayi brush din bafa cin komai zaiyi ba kuma Dr yace zai dan iya cin abinci kadan kadan bawai dayawa ba"

"Sannu da kokari, Allah yabada lada....,ayi mana afuwa amma"

Bude idanuwa fahad yayi ya kalleta yana jin wani irin sabon sonta yana shigarshi,

"Yanzu dai gashi sai kusan yanda zakuyi kiyi masa brush din"

"A'a babban yaya ai sai ka taimaka min"

Da taimakonshi suka samu yayi brush din sannan ta zubawa abba abinci yafita waje yaci, Dr ne yashigo shida wasu nurse maza guda biyu yaduba jikin fahad sannan yafita yabar nurse din domin su gogewa fahad wurin da aka yankashi, ai ana saka audugar da aka tsoma cikin ruwan spirit ya runtse idanuwansa tareda sake damke hannun bilkisu tun nurse din Suna tsokanarsa sun zaci shagwaba ce har kowa ya fahimci dagaske yake domin kuka yasaka musu saida aka gama suka fita Abba yashigo tsayawa yayi yana kallon fahad wanda har lokacin bai daina kukanba,

"Kai wai menene amfanin kukan ne? Dallah malam tashi kaci abinci saboda ni tafiya zanyi"

Ko motsi baiyi ba bare asaka ran zai yarda yaci abincin, shi dama idan lafiyarsa kalau yana son abinci sosai amma idan bashida lafiya to shida abinci sai ahankali, gyara zama bilkisu tayi tafara lallashinshi,

Gefen lifayarta tasaka tafara goge masa fuskarshi, kanshi tashiga shafawa sannan ahankali ta sunkuya daidai kunnenshi tafara yimasa rada,

"Kaifa yanzu ba yaro bane kagirma, kayi hakuri.... Yi shiru katashi kaci abinci, dan kadan zan baka dama kai na dafowa..."

Ahankali ahankali yasoma rage kukan nashi har yadaina gaba daya sai ajiyar zuciya da yake ajiyewa, mikewa tayi da niyyar yiwa ya abba magana amma sai taga wayam wato yafice yabasu wuri kenan, tea ta hada masa mai kauri bai kai rabin cup ba ta taimaka masa ya dan tashi yanata cije lips, yana hawaye yana shan tea din wai ahakanma dan itace amma da wanine da sai ansha fama dashi kafin yasha, wainar kwai guda daya da dankali guda biyar ta sake bashi yana ci yana yamutsa fuska yana gamawa ta mayar dashi ya kwanta, wayarshi ta ciro ajakarta tabashi yakarba ya ajiye agefen pillow din da yake kai, su ayiyah ne suka shigo harda baba lifayarta taja tarufe fuskarta kadan tasauka kasa ta gaidasu bayan sun gaisa tafice waje ta zauna bisa bencin dake kofar dakin anan ammah ta sameta itada Rabi mai aikinta, tare suka shiga ammah ta dubashi sannan tafito itada rabi suka bar ammah acan wurunsu ayiyah. Sunata hirarsu da Rabi har khulsum tazo itama tashiga ta dubashi tafito tatafi saboda wurin aiki zata tafi. Wurin misalin karfe 10 saiga maama dasu meenah abban hudah yakawo su anan suka shantake kamar ba dubiya suka zo ba domin anan ammah tatafi tabarsu,kowaccensu rikeda yarta har su anty fauziyya sukazo suma dauke da girke girken da suka iyo, shikuwa marar lafiyar yana daki kwance shida salim suna hira amma dayake jiya baiyi baccin kirki ba da daddare yanzun sai hamma yake danyi.

Bayan anyi sallar azahar suna gama cin abinci salim yaleko yakira bilkisu tashi tayi batare da ta bude warmer din da rabi takawo ba yanzu, dakin tashiga fahad na baje sai faman lumshe idanuwa yake, hannu yamika mata yajata gefenshi,

"Zo ki tayani baccin rana luv"

Ita abinma maimakon yabata haushi kunya yabata saboda ga abokinshi zaune kan gadon marassa lafiyar dake makotaka da na fahad amma babu patient akai, maganarsa tasake juyowa ahankali domin tunda aka kawoshi asibitin ma sai yanzu ne sukaji yayi magana amma da ko me yarike maganar oho,

"Zo muyi baccin rana hajjaju"

Dan satar kallon wurinda salim yake tayi amma sai taga shi hankalinsa ma ba awurinsu yakeba domin yana ga kan wayar fahad dake hannunsa, jin kunyar gwasaleshi tayi agaban abokinshi domin tasan babu wanda yasan irin zaman da sukeyi kusan kowa yazaci zaman aure sukeyi na hakika, tana can duniyar tunani ya hardota da hannunshi zuwa kan kafadarshi bai tsaya ananba yashiga shafar bayanta kamar wata jaririya, lumshe idanuwa tayi tai shiru kamar mai yin baccin da gaske shi dai mutumin abu biyune suka taru suka hadar masa lokaci guda ga ciwo ga kuma wani abu dake sauka asassan jikinsa gaba daya wanda yafi kamada kasala kasala, gajiya gajiya, ji yayi bazai iya jure wannan kamshin nata dake barazanar tarwatsa tunaninsa ba, bakinshi yakai kan goshinta yabata kiss mai sanyi sannan ya soma kokarin lulluba da lifayar jikinta anan ne kuma taso bashi matsala amma sai ya shagwabe fuska,

"Allah sanyi nakeji fa..."

"To akawo maka bargo?"

Girgiza kai yayi harda makale kafada,

"Ni naki nakeso, dan wannan mayafin naki zai isheni.."

Yar kokawa sukayi kafin ta farga yashige cikin lifayar tata ya kwakuma akirjinta amma fa duk abinnan dake faruwa bai motsa kafafunsa ba iyakacin hannayensa da kanshi ne yake motsawa, salim dake zaune yana jin duk abinda ke faruwa tunda ya kallesu sau daya bai sake iya kallonsu ba sai bayama yajuya musu domin sunyi mutukar bashi kunya. Mintuna kadan taji jikinsa ya dan saki alamar yayi bacci da dabara da komai tasamu ta zare jikinta ta tashi tafita bayan ta gyara masa kwanciyarshi yadda bazai takuraba, tana komawa wurinsu maama sai kuma duk ta tsargu da kus kus din da sukeyi musamman ma da ta kama Hindu na gulmarta da ido itada meenah,

"Adda labour ya mai jiki?" Inji maama, banza tayi da ita ta karbi Minal dake hannun hindu ta rike tana lakutar kumatun yarinyar,

Duk dan bikin da suke tayi tana jinsu bata tanka ba daga karshe ta jawo warmer din da ammah ta aiko musu da ita tabude domin bata san ko wanne irin kalar abinci bane, farfesun koda ne cikin warmer din sai tashin kamshi yake wannan dalilin ne yasata niyyar baiwa fahad yaci domin naman ya dahu ligif zai iya ci,

"Maman hudah zuba muku kuci ni ba ci zanyiba sai dai shi ku bar masa"
Chapter 27 · 0% Book details