← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 40 OF 67

Sashe 40

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ai Dr yace babu wani ciki yanzu... Yace bata da komai, gara ma da Allah bai bata ba domin hada zuri'a da irinsu wannan hamood din hatsarine... Allah yabata masu albarka nan gaba" maama tafada tana kokarin mayar da kwallar da take kokarin cikowa idanunta, ammah dai har akayi aka gama bata tofa tata ba suna nan zaune sunata yimata sannu har Abba yazo yadubata yatafi hakama mazajensu duk sunzo sun dubata, khulsum amarya itama daren ranar sai gata, kowa yaga bilkisu sai yaji tausayinta sakamakon kumburar da fuskarta tayi tsabar duka. Lokacin da dare yayi meenah ce tace zata kwana da ita amma ammah tace a'a kowa yatafi gidansa inyaso Rabi mai aikinta sai tazauna su kwana tare hakan kuwa akayi, ita dai bilkisu kasa baccinma tayi sakamakon suyar da zuciyarta keyi motsi kadan zata furta,

"Allah ya isa..." Acikin zuciyarta kokuma afili. Saida tayi kwana uku agadon asibiti sannan tafara tashi har ta zauna kuma an danyi sa'a kumburin fuskar tata ya dan ragu, har ranar babu wanda yayi mata maganar hamood may be suna son abar asibitinne tukunna sai asanar mata abinda yafaru, aranar tana zaune maama na kusa da ita agefen gadon tana bare mata ayaba tana ci sai ga hajiya iyallo ita da yakumbo mai gado, tunda iyallo tashiga dakin take tsinewa hamood,

"Ni dama wallahi wannan yaron ban yarda dashiba... Yaro sai kace dan dambe wani murgujeje dashi... Wallahi tsohon mijinki shine miji mai gado... Yaro mai kunya ko gaisheka yakeyi idanuwansa akasa bazai taba yarda ya hada ido dakaiba amma shi wannan idonsa atsakar ka yake sai yasaka idonsa cikin naka sannan zaiyi maka magana....Allah yasawwake,Allah ya kwashe masa albarka macuci"

Tun abun na bawa su maama haushi har yadawo yana sakasu dariya, iyallo nata faman hamuki ya mudan yashigo wanda dama shine yakawo su,yana yiwa bilkisu yajiki iyallo tahau cewa,

"Ai shikenan yanzu sai acika min burina ayi hadin nan.. Ni dama tun farko mudansiru naso abawa aka ki..."

"Dan Allah iyallo mu ki kyalemu muji da abinda muke ji..." Maama tafada tana hararar gefe,

"To fitsararriya dadinta ma dai bake naceba balle kiyimin rashin arziki... Fitsararriya kawai.."

Shi dai ya mudan ficewa yayi daga dakin da alama shima baiji dadin maganar iyallo ba ko meye dalili? Bilkisu kuwa jin iyallo ta ambaci fahad har tana yabonsa yasata dulmiya kogin tunani.....

*Wannan littafin na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*

*_Ummi Shatu_*

*Wannan littafin na siyarwane me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*

_BILKISU_

37 ***Har iyallo ta karici bambaminta tagama bilkisu batace uffan ba kusanma gaba daya yanzu tadaina fahimtar abinda suke cewa domin tadade da yin nisa acikin kogin tunani tabbas maganar iyallo gaskiya ce fahad yarone mai kunya kuma nagartaccen namiji domin ita kanta ta shaida hakan duk da har yanzu bata jin zata iya zaman aure dashi domin yayi mata kankanta shekarunta sunfi nasa, to tayaya zatayi rayuwar aure dashi? Tayaya zai rabeta amatsayin matarsa? Haba ai da kunya,jikinta yanzu yafara bata cewar wannan abunda yafaru da ita harda hakkin fahad kila Allah ne yayi masa sakayyar cutarwar da tayi masa itada hamood shiyasa ya hanasu jin dadi da farin ciki a lokacin zaman aurensu, ita kanta sai yanzu take ganin wautarta da rashin wayon da ta aikata gaskiya hamood ya shammaceta ya cutar da ita, wasu hawaye masu zafi taci gaba da zubarwa ganin haka yasa iyallo sake dagewa wurin tsinewa hamood ita kuwa bilkisu ita kadai tasan dalilin kukanta gashi kukan zuci takeyi marar sauti sai dai kawai aga hawaye na zuba alhali likita yace irin wannan kukan yafi illa dan haka ta nisanceshi amma ita kanta tasan bazata taba iya hana wadannan hawayen zubaba domin direct suke tahowa daga can cikin zuciyarta.

"Adda labour dan Allah kiyi hakuri kidaina kukan nan haka.... Maganin me kukan zaiyi ne?" Mama tafada cikin rakwarkwabewar fuska,

"Mamaa yazama dole inyi kuka... Barni in koka ko zuciyata zatayi sanyi...."

"Kidai yi hakuri kuma ki daure dan Allah...."

"Maama..... Bazan.... Baz....."

Ai bata kai ga karasawa ba kirjinta ya sarke idanuwanta suka kakkafe, wata gigitacciyar kara maama tasaka yayinda su iyallo kuma suka hau zuba salati, karar da maama tafasa itace ta janyo hankalin ya mudan yashigo cikin dakin cikin tashin hankali ganin abinda ke faruwa yasa shi fita da sauri zuwa office din likita, maama na rike da ita tana gunjin kuka likita yashigo yafitar dasu ta hanyar basu umarnin su fice daga dakin, yajima akanta sannan yafita har lokacin jikin maama bai daina rawaba da nasu iyallo domin su duk atunaninsu mutuwa bilkisu tayi amma sai likita yace musu bahaka bane su kwantar da hankalinsu da ranta kuma insha Allah zata samu lafiya, ita dai bilkisu na can bata san abinda ke faruwa ba domin tadade da rabuwa da hankalinta, lokacin da su ammah sukazo ma baccinta take tasha sai ruwa da ake kara mata, tsaki meenah taja tasamu wuri ta zauna kusa da Hindu bayan tadawo daga leken bilkisu ta window din dakin da take ciki,

"Wai dan Allah sai yaushe za abar baiwar Allahn nan tahuta ne? Haba jama'a Karin ruwa yaki karewa...."

"To ya za ayi Ameenah... Allah dai yabata lafiya..." Inji ammah, zama sukayi jugum jugum har sai da likita yakira ammah nan suka rankaya gaba daya suka tafi, dan takaitaccen bayani yayi musu dangane da matsalar da bilkisu tasamu amma yace yanzu sun samu nasarar shawo kan matsalar sai dai yanada kyau ta guji tunani da shiga bacin rai domin maganar gaskiya zuciyarta na daf da bugawa saboda damuwa, duk cikinsu babu wanda bai kokaba sai Ammah kadai itace ke basu hakuri, zuwa dare bilkisu ta farfado hakan ya dan kwantar musu da hankali musamman ma da sukaga duk wuraren da yataru jini ajikinta ya barbaje, babu laifi taji sauki sosai sannan ta samu lafiya matsalar kawai dorin hannunta ba akunce ba likita yace sai nan da sati biyu haka suka yita faman kaiwa da komowa har zuwa lokacin da aka kunce dorin aka sallamesu, duk bilkisu tabi tasake kekashewa kamar wadda tayi shekara akwance. Lokacin da suka koma gida ba karamin mamaki tashiga ba domin ganin kayanta gaba daya nasawa andebosu da duk wani abu wanda yake mallakinta ne, ita dai har ta kwana ta yini tasake kwana babu wanda yayi mata maganar hamood ko wata magana mai kama da haka, shi kansa abba baiyi mata maganar ba iyakaci idan taje ta gaisheshi suka gaisa shikenan amma bai yimata maganar hamood ba haka itama ammah duk da suna zama suna yin hira, sai akwana na biyarne maama tasake dawowa gidan domin dubata itada hudah harda farfesun kaji da dambunshi wanda ta iyowa bilkisu, cikeda sha'awa bilkisu ke kallonta domin har cikinta ya dan fara turowa duk da dai tanada girman ciki amma kowa yaganta yaga mai juna biyu, saida suka sha hira afalon ammah ganin lokacin salla yayi yasa bilkisu tafiya dakinta tayi wanka tazura doguwar riga tayi salla tana idarwa maama tashigo tana rikeda hannun hudah, kwantar da ita tayi kan gadon bilkisu sannan ta yunkura zata tashi nan bilkisu tayi hanzarin dakatar da ita,

"Yawwa maama wai dan Allah waye yakaini asibiti ne? Sannan hamood kuwa yayi sakin?"

Komawa maama tayi ta zauna tana kallon bilkisu,

"Adda labour wallahi ranar hudah muka kai asibiti nida abbanta, gaba daya sai najini ba anutse ba sannan hankalina duk yatafi gareki shine fa nace masa mubiya inganki dakyar ma yayarda wai yana gudun makara a office, ina shiga na iskeki cikin wannan halin hamood yanata kwallo dake.... Abban hudah ne ya daukeki yakai cikin mota bayan nakiraki shine muka wuce dake asibiti, sai bayan da akayi admitting dinki sannan nakira su ammah..."

Jijjiga kai bilkisu tayi cikin damuwa sannan ahankali tace,

"To ya maganar sakin? Ya sakeni?"

Kai maama ta daga mata cikeda damuwa,

"Ya sakeki bayan sun debota da Abba domin Abba waya yayiwa uncle dinsa yasanar dashi komai nan uncle din nasa ke cewa shi dama bashida wani hadi dashi inbanda almajiranta da yazo yi har Allah yahadasu yake wanke wanke agidansa dahaka yazama tamkar dan gida.... Ke intakaice miki zance ma shi kansa hamood din saida Abba yasa aka nemoshi sukayi babu dadi dan cewa yayi shi bazai sakeki ba har sai anbiyashi komai nasa tun daga kayan lefe har sadaki... Sai da Abba yabiyashi sannan ya sakeki saki biyu..."

Tagumi bilkisu ta rafka tana jin kirjinta nayi mata suya,

"Lallai hamood yacika marar mutunci.... Nimafa akwai kudina a hannunshi wanda Abba yabani yace wai in ranta masa wani mutum yasiyarwa da mota to kuma yanzu yadawo masa da ita shine zai cika yabashi kudinsa saboda already kudin hannunshi ya tura za a kawo musu sabbin cars...."

"Babu komai adda maigado kawai kiyi addu'a insha Allah bazaki tagayyara ba kuma sai Allah yasaka miki... Ni wallahi idanma son samune tsohon mijinki yadawo kusake dinkewa.... Allah sarki ya fahad bawan Allah komai nasa na mutunci...."

Shiru bilkisu tayi tana saurarenta har saida taji tayi shiru sannan tasauke nannauyar ajiyar zuciya tana kallonta,

"Maama kenan...."

"Wallahi dagaske adda labour fahad shine yafi dacewa dake saboda yanada yakana da alkunya..."

Rasa abin cewa tayi daga karshe taja bakinta tayi shiru tana jin maama sai faman kwarzanta fahad take tayi.

Sam abinda maama ta fada baiyi tasiri acikin zuciyarta ba sai dai yatsaya mata arai fiyeda tunanin mai tunani domin daren ranar kawai tunanin rayuwar da tayi agidansa tayita yi tana tuna dabi'unsa da kuma halayensa wadanda ko makiyinsa bazai kushe ba, tarasa a wanne aji yadace tasaka wannan al'amari, shin yanzu idan fahad yadawo zata iya aminta dashi? Wannan shine tambayar da tayiwa zuciyarta amma sai ta girgiza kanta,

"Dan mutunci kam bani da ja yanada mutunci da hankali amma zamana tareda shi a matsayin miji da mata.... Hmmm" sai kuma tayi shiru takasa karasawa, karshenta dai wannan dare sai bacci barawo shine yasamu nasarar saceta lokacin da take tsaka da tunani tana tambayar kanta wai meye dalilin da yasa kowa ke yimata fatan fahad yadawo gareta?.

_FAHAD_
Chapter 40 · 0% Book details