Sashe 52
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Baice komai ba yakoma yaja mata kofar, wanka yaje yayi yafita bai wani jimaba yakawo kayan miyar yasake komawa kai tsaye gidan anty asabe yawuce ta can suka tafi kasuwa tare da ita, kayan lefen husnah suka hado sannan suka sabunto lefen Bilkisu nada suka sassauyo kayan ciki da akwatunan saboda kafin yakoma makaranta za akai lefen husnah sannan za ayanke rana, wuni cur sukayi akasuwa shida anty dan sai yamma liss suka koma gida duk da tana ta cewa yazauna yaci abinci yace a'a girkin amarya zaije yaci,
"Babu ko kara ko fahad?" Ta fada tana dariya, baiyi magana ba yasaka sau cikinsa yanufi gida.
Kamar yadda jiya bata san fitarsa ba haka yauma batare da ta saniba yayi tafiyarsa shiyasa abun ya tsaye mata arai, tana kitchen tana girkin abincin rana khulsum tazo dauke da danta khalifa,tare suka karasa wuni da yamma tatafi, khulsum na tafiya bayan takoma ciki tayi wanka tana shiryawa fahad yadawo, yunwa yakeji sosai sannan gashi yagaji lilis, rigar shaddar dake jikinsa yacire ya zamana daga shi sai yar farar singileti da dogon wando, zama yayi kan table yafara bude abincin dake wurin, jallop din shinkafa ne sai hadin vegetables salad mai dauke da dafaffen kwai aciki. Yana tsaka da cin abincin yajiyo karar wayarshi amma bai iya tashiba saboda yana jin dadin abincin sosai ba kadan ba, yayi missing girkinta da ita kanta gaba daya, saida ya koshi dam sannan yataso yana rikeda tissue yana goge bakinsa, dai dai lokacin itama tafito daga cikin daki, kallon juna sukayi tazo tawuce shi tanufi dining area ta bude fridge ta dauko banana milk shake ta zuba acikin glass cup tazo tawuce daki, ganin abinda ta debo yasashi shima komawa dining area din yazuba cikin cup ya shanye yana lumshe ido saboda gardi da dadi gashi yadau sanyi ba karya, rigarshi da ya cire yaje ya dauka tareda wayarshi yashiga daki, zama yayi saman katifa yana kokarin kiran husnah saboda itace ta kirashi dazu, tana dagawa yace,
"Am sorry my love.... Dazu kin kirani time din ina tare da antynki ne ina cin girkinta mai dadi...."
Duk da taji haushin maganarsa amma saita waske tanuna kamar bataji zafin hakan ba tace,
"Babu komai my prince dama zan fitane zamuje kasuwa nida Fa'iza...."
"Adawo lafiya my love.... Allah yatsare"
Daga haka sukayi sallama yakatse wayar dama tun lokacin da suka jone da husnah ko ba ya gari idan zata fita saita tambayeshi shiyasa har sun dade da sabawa da wannan tsarin sam basa kallonsa asabon abu. Irin zaman da su Bilkisu suka faro shi suka cigaba da yi na ba ruwan kowa da kowa, gaisuwa kuwa tab rabon da taji fahad ya gaisheta har ta manta gashi yanzu wani sabon salon wulakanci da ya koya shine sai yarinka kiranta da Bilkisu, idan zaiyi mata magana sai dai yakira sunanta, yauma da zai fada mata sakon su ayiyah tana daki tana ware kayan sawarta tana karasa shiryawa cikin drewar, zama yayi gefen gadonta yace,
"Am Bilkisu ayiyah tabani sako.... Tace wai gobe za akai lefen ya Abba gidansu salim idan kinada lokaci kije akai dake...."
"Naji...." Tafada atakaice saboda tasoma kosawa da wannan rashin kirkin nashi akan me zai rinka kiran sunanta kai tsaye? Duk da bawai yau yafara ba amma yau kamar hakan yafi kona mata rai. Washe gari da yamma bayan tadawo daga aiki ta shirya tatafi gidansu fahad sai kaffa kaffa ayiyah takeyi da ita, dama tasan bata da matsalar uwar miji dan ayiyah na mutukar sonta hakama sauran yan uwan mijinta kawai dai abinda ta lura shine matar ya sunusi wato anty juwairiyya bata faran faran da ita tun wancan lokacin har yanzu dan tun aurensu nafarko taketa kukkushe Bilkisu tana cewa ai fahad tsohuwar yayarshi ya auro dan wannan a haihuwar kajima ai ta haifeshi, ko yauma da ta shigo gidan kowa yanata murna da lale marhabun da ita amma banda Anty juwairiyya shiyasa itama takama class dinta daga gaisuwa bata kara cewa komai ba,tarba ta girmamawa aka yimusu agidansu salim akwatuna shida masu kyau suka kaiwa nusaiba bayan an karbi kayan da babu jimawa suka koma gidansu fahad lokacin magriba tayi, Bilkisu tafito tsakar gida tana alwala sai ga fahad yashigo daga masallaci yake anty juwairiyya na ganinshi tafara cewa,
"Kaga sabon ango....kaima nanda wani satin zamuje Kaduna mukai maka naka...."
Baiyi magana ba sai murmushi kawai duka hannayenshi na cikin aljihun rigar farar shaddar da take jikinsa,gun Bilkisu yakarasa ya tsaya kusa da ita tana alwala,
"Zaki tafi yanzune injiraki ko sai anjima sai indawo in daukeki?"
Jin abinda yace ba karamin dadi yayiwa Bilkisu ba saboda tasan dai ko babu komai anty juwairiyya zata gane fahad na yinta kuma tanada wani matsayi na musamman agareshi,rausayar da kai tayi ta kalleshi sannan tace,
"Da sallah nake son nayi... Ko sauri kakeyi?"
"A'a kiyi mana... Kiyi sai mutafi"
"Yawwa nagode" tafada tana kokarin shiga falon ayiyah inda anty juwairiyya ke tsaye tana kallonsu sai jan fahad take da maganar bikinsa shida husnah amma yaki biye mata suyi saboda shi yanada wani abu guda daya akan Bilkisu, idan daga shi sai itane baya raga mata ahalin yanzu amma idan agaban mutane ne ko wani to yana nuna har gobe yana sonta yana martabata, shiyasa abun bai cika damun Bilkisu ba saboda sai idan iya shi da itane yake nuna shine oga dole ta girmamashi. Har ta idar da salla bai bar kofar falonba yana tsaye da wayarshi a hannu yana dannawa, lokacin da take yiwa ayiyah sallama tana jiyo anty juwairiyya nace masa,
"Ko da amaryar ake soyewa ne dan kanina...."
"Kai anty nifa gaskiya kin saka min ido da yawa..." Yafada yana dariya, sosai Bilkisu taji dadin amsar da yabata, fitowa tayi rikeda irin kayan snacks din da aka basu agidansu salim wanda anty asabe ta zubo mata, karba yayi daga hannunta yawuce gaba tana biye dashi abaya har waje, su ya Abba na zaune akofar gida shida salim sai taji duk kunya ta kamata musamman ma lokacin da zata hau bayan babur din nashi dole saida ta dafa kafadunshi duka guda biyun, har sukaje gida babu wanda yace da wani ci kanka sai dai idan sun dan shiga kwari ko gargada yaji ta rikeshi da haka suka je gida. Cikin yan kwanakin aka kammala komai na zuwa kd domin kai lefenshi komai iri daya yayi ma husnah da Bilkisu bai banbanta ba ita Bilkisu ma bata san wacce wainar ake toyawa ba, ita dai kawai abinda tasani shine bazata taba daukar raini ba nashi ko na matarshi, ranar da aka tafi kai lefen ma bai fada mata ba saboda har gobe irin zaman da ya zabar musu sukeyi, ita anata ganin ai ba ita yadace ta rinka shan kanshi ba ko kuma ta nemi shiri dashi, shiyasa gaba dayansu ba wani dadin zaman sukeji ba saboda kowa baya sakarwa kowa, har aka kai lefen aka saka rana wata biyu babu wanda ya gaya mata batama saniba gaba daya, shi kam fahad shirin komawarsa makaranta yasaka gaba yana kammalawa ya tafi bayan yabar mata duk abinda yasan zata bukata. Wani lokacin Mariya ko maryama ayiyah ke turo mata su tayata kwana amma ba kullum ba, tunda yatafi kuma bai kirata ba sai bayan kwana hudu da tafiyarsa nan dinma iyakarta gaisuwace daga nan ya tambayeta ko da akwai abinda take bukata tace babu shikenan yace mata sai anjima, hakace take faruwa har yayi sati uku da tafiya a lokacin ne yazo gida weekend, tun ranar Thursday yazo yana son komawa Monday ko Tuesday,lissafin bikinsu kuwa saura sati hudu babu yan kwanaki, a wannan zuwan da yayi yai niyyar fadawa Bilkisu maganar aurenshi da husnah, ranar ya fada mata da safe tana karyawa zata tafi aiki saboda Monday ce shikuma yana kwance kan three sitter yana kallo, a laptop dinshi,
"Bilkisu aure zanyi fa...., yau saura sati uku da kwana biyu..."
Saida ta dan ja numfashi sannan cikin halin ko inkula tace,
"Allah yabada sa'a... Ko akwai wani abu da zanyi baya ga haka?"
Girgiza kai yayi yana murmushin takaici bai san sai yaushe Allah zai karbi addu'arshi yasa Bilkisu ta soshi kamar yadda yake sonta ba, ita kuwa tsabar takaici da bacin rai ko gama cin abincin ba tayiba tabarshi ta tashi ta dauki wayarta da handbag dinta tafita dama tun dazu mai napep din dake kaita aiki yazo. Fahad kwanciyarsa yaci gaba dayi har saida husnah ta kirashi tace yataimaka yazo ya dinka mata atamfarta domin da ita take son tatafi gida jibi, jibi zata gama exams dinta kuma idan tatafi bazata dawoba sai bayan bikinsu saboda hutun session ne, tashi yayi duk jikinsa babu karfi yayi wanka yashirya cikin kananan kaya, bakar riga da milk colour din trouser, zama yayi ya karya sannan yafita yasamu husnah a shagonsu salim tana jiransa, tsokanarsu salim yafara yi yana waka yana cewa ga amarya ga ango, tare suka haura saman shagonsu fahad inda zaiyi mata dinkin.
"Babu ko kara ko fahad?" Ta fada tana dariya, baiyi magana ba yasaka sau cikinsa yanufi gida.
Kamar yadda jiya bata san fitarsa ba haka yauma batare da ta saniba yayi tafiyarsa shiyasa abun ya tsaye mata arai, tana kitchen tana girkin abincin rana khulsum tazo dauke da danta khalifa,tare suka karasa wuni da yamma tatafi, khulsum na tafiya bayan takoma ciki tayi wanka tana shiryawa fahad yadawo, yunwa yakeji sosai sannan gashi yagaji lilis, rigar shaddar dake jikinsa yacire ya zamana daga shi sai yar farar singileti da dogon wando, zama yayi kan table yafara bude abincin dake wurin, jallop din shinkafa ne sai hadin vegetables salad mai dauke da dafaffen kwai aciki. Yana tsaka da cin abincin yajiyo karar wayarshi amma bai iya tashiba saboda yana jin dadin abincin sosai ba kadan ba, yayi missing girkinta da ita kanta gaba daya, saida ya koshi dam sannan yataso yana rikeda tissue yana goge bakinsa, dai dai lokacin itama tafito daga cikin daki, kallon juna sukayi tazo tawuce shi tanufi dining area ta bude fridge ta dauko banana milk shake ta zuba acikin glass cup tazo tawuce daki, ganin abinda ta debo yasashi shima komawa dining area din yazuba cikin cup ya shanye yana lumshe ido saboda gardi da dadi gashi yadau sanyi ba karya, rigarshi da ya cire yaje ya dauka tareda wayarshi yashiga daki, zama yayi saman katifa yana kokarin kiran husnah saboda itace ta kirashi dazu, tana dagawa yace,
"Am sorry my love.... Dazu kin kirani time din ina tare da antynki ne ina cin girkinta mai dadi...."
Duk da taji haushin maganarsa amma saita waske tanuna kamar bataji zafin hakan ba tace,
"Babu komai my prince dama zan fitane zamuje kasuwa nida Fa'iza...."
"Adawo lafiya my love.... Allah yatsare"
Daga haka sukayi sallama yakatse wayar dama tun lokacin da suka jone da husnah ko ba ya gari idan zata fita saita tambayeshi shiyasa har sun dade da sabawa da wannan tsarin sam basa kallonsa asabon abu. Irin zaman da su Bilkisu suka faro shi suka cigaba da yi na ba ruwan kowa da kowa, gaisuwa kuwa tab rabon da taji fahad ya gaisheta har ta manta gashi yanzu wani sabon salon wulakanci da ya koya shine sai yarinka kiranta da Bilkisu, idan zaiyi mata magana sai dai yakira sunanta, yauma da zai fada mata sakon su ayiyah tana daki tana ware kayan sawarta tana karasa shiryawa cikin drewar, zama yayi gefen gadonta yace,
"Am Bilkisu ayiyah tabani sako.... Tace wai gobe za akai lefen ya Abba gidansu salim idan kinada lokaci kije akai dake...."
"Naji...." Tafada atakaice saboda tasoma kosawa da wannan rashin kirkin nashi akan me zai rinka kiran sunanta kai tsaye? Duk da bawai yau yafara ba amma yau kamar hakan yafi kona mata rai. Washe gari da yamma bayan tadawo daga aiki ta shirya tatafi gidansu fahad sai kaffa kaffa ayiyah takeyi da ita, dama tasan bata da matsalar uwar miji dan ayiyah na mutukar sonta hakama sauran yan uwan mijinta kawai dai abinda ta lura shine matar ya sunusi wato anty juwairiyya bata faran faran da ita tun wancan lokacin har yanzu dan tun aurensu nafarko taketa kukkushe Bilkisu tana cewa ai fahad tsohuwar yayarshi ya auro dan wannan a haihuwar kajima ai ta haifeshi, ko yauma da ta shigo gidan kowa yanata murna da lale marhabun da ita amma banda Anty juwairiyya shiyasa itama takama class dinta daga gaisuwa bata kara cewa komai ba,tarba ta girmamawa aka yimusu agidansu salim akwatuna shida masu kyau suka kaiwa nusaiba bayan an karbi kayan da babu jimawa suka koma gidansu fahad lokacin magriba tayi, Bilkisu tafito tsakar gida tana alwala sai ga fahad yashigo daga masallaci yake anty juwairiyya na ganinshi tafara cewa,
"Kaga sabon ango....kaima nanda wani satin zamuje Kaduna mukai maka naka...."
Baiyi magana ba sai murmushi kawai duka hannayenshi na cikin aljihun rigar farar shaddar da take jikinsa,gun Bilkisu yakarasa ya tsaya kusa da ita tana alwala,
"Zaki tafi yanzune injiraki ko sai anjima sai indawo in daukeki?"
Jin abinda yace ba karamin dadi yayiwa Bilkisu ba saboda tasan dai ko babu komai anty juwairiyya zata gane fahad na yinta kuma tanada wani matsayi na musamman agareshi,rausayar da kai tayi ta kalleshi sannan tace,
"Da sallah nake son nayi... Ko sauri kakeyi?"
"A'a kiyi mana... Kiyi sai mutafi"
"Yawwa nagode" tafada tana kokarin shiga falon ayiyah inda anty juwairiyya ke tsaye tana kallonsu sai jan fahad take da maganar bikinsa shida husnah amma yaki biye mata suyi saboda shi yanada wani abu guda daya akan Bilkisu, idan daga shi sai itane baya raga mata ahalin yanzu amma idan agaban mutane ne ko wani to yana nuna har gobe yana sonta yana martabata, shiyasa abun bai cika damun Bilkisu ba saboda sai idan iya shi da itane yake nuna shine oga dole ta girmamashi. Har ta idar da salla bai bar kofar falonba yana tsaye da wayarshi a hannu yana dannawa, lokacin da take yiwa ayiyah sallama tana jiyo anty juwairiyya nace masa,
"Ko da amaryar ake soyewa ne dan kanina...."
"Kai anty nifa gaskiya kin saka min ido da yawa..." Yafada yana dariya, sosai Bilkisu taji dadin amsar da yabata, fitowa tayi rikeda irin kayan snacks din da aka basu agidansu salim wanda anty asabe ta zubo mata, karba yayi daga hannunta yawuce gaba tana biye dashi abaya har waje, su ya Abba na zaune akofar gida shida salim sai taji duk kunya ta kamata musamman ma lokacin da zata hau bayan babur din nashi dole saida ta dafa kafadunshi duka guda biyun, har sukaje gida babu wanda yace da wani ci kanka sai dai idan sun dan shiga kwari ko gargada yaji ta rikeshi da haka suka je gida. Cikin yan kwanakin aka kammala komai na zuwa kd domin kai lefenshi komai iri daya yayi ma husnah da Bilkisu bai banbanta ba ita Bilkisu ma bata san wacce wainar ake toyawa ba, ita dai kawai abinda tasani shine bazata taba daukar raini ba nashi ko na matarshi, ranar da aka tafi kai lefen ma bai fada mata ba saboda har gobe irin zaman da ya zabar musu sukeyi, ita anata ganin ai ba ita yadace ta rinka shan kanshi ba ko kuma ta nemi shiri dashi, shiyasa gaba dayansu ba wani dadin zaman sukeji ba saboda kowa baya sakarwa kowa, har aka kai lefen aka saka rana wata biyu babu wanda ya gaya mata batama saniba gaba daya, shi kam fahad shirin komawarsa makaranta yasaka gaba yana kammalawa ya tafi bayan yabar mata duk abinda yasan zata bukata. Wani lokacin Mariya ko maryama ayiyah ke turo mata su tayata kwana amma ba kullum ba, tunda yatafi kuma bai kirata ba sai bayan kwana hudu da tafiyarsa nan dinma iyakarta gaisuwace daga nan ya tambayeta ko da akwai abinda take bukata tace babu shikenan yace mata sai anjima, hakace take faruwa har yayi sati uku da tafiya a lokacin ne yazo gida weekend, tun ranar Thursday yazo yana son komawa Monday ko Tuesday,lissafin bikinsu kuwa saura sati hudu babu yan kwanaki, a wannan zuwan da yayi yai niyyar fadawa Bilkisu maganar aurenshi da husnah, ranar ya fada mata da safe tana karyawa zata tafi aiki saboda Monday ce shikuma yana kwance kan three sitter yana kallo, a laptop dinshi,
"Bilkisu aure zanyi fa...., yau saura sati uku da kwana biyu..."
Saida ta dan ja numfashi sannan cikin halin ko inkula tace,
"Allah yabada sa'a... Ko akwai wani abu da zanyi baya ga haka?"
Girgiza kai yayi yana murmushin takaici bai san sai yaushe Allah zai karbi addu'arshi yasa Bilkisu ta soshi kamar yadda yake sonta ba, ita kuwa tsabar takaici da bacin rai ko gama cin abincin ba tayiba tabarshi ta tashi ta dauki wayarta da handbag dinta tafita dama tun dazu mai napep din dake kaita aiki yazo. Fahad kwanciyarsa yaci gaba dayi har saida husnah ta kirashi tace yataimaka yazo ya dinka mata atamfarta domin da ita take son tatafi gida jibi, jibi zata gama exams dinta kuma idan tatafi bazata dawoba sai bayan bikinsu saboda hutun session ne, tashi yayi duk jikinsa babu karfi yayi wanka yashirya cikin kananan kaya, bakar riga da milk colour din trouser, zama yayi ya karya sannan yafita yasamu husnah a shagonsu salim tana jiransa, tsokanarsu salim yafara yi yana waka yana cewa ga amarya ga ango, tare suka haura saman shagonsu fahad inda zaiyi mata dinkin.