← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 67

Sashe 20

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ehh yafita" bilkisu tabata amsa tana harararta kasa masa saboda haushi suke bata idan taji sunce mishi yayan nan wallahi, ganin tasake samun yar tayin hira su anty fauzy suka yimata sallama suka tafi, ledoji ta cika musu da kayan zakin da maama takawo mata ta rakasu har kofar gida anan suke sanar da itama gidajensu zasu wuce basai sun koma gidan ayiyah ba saboda dama sun rigada sunyi sallama, wurinsu khulsum takoma bayan taga tafiyarsu nan hira ta barke bare yanzu sai su kadai har magrib suna gidan ta hanasu tafiya tace sai fahad yadawo. Bayan sallar magrib kuwa babu jimawa sai gashi yadawo yana rikeda CD flate din bikinsu da yakarbo, maama yaya sama yaya kasa ta ringa kiranshi dashi dama suna shiri sosai musamman ma dayake tana kamada bilkisu fari kawai tafi bilkisu duk dinsu ma sun fita haske saboda ammah suka biyo ita kadaici ta dauko kalar abba tayi baki amma bakin shima bawani can dayawa ba sai dai baza asata alayin farare ba, ganin yadawo suka yimusu sallama suka fita ai harda fahad arakasu kofar gida bayan sunga tafiyarsu suka koma ciki lokacin babu wuta saida fitilar wayarshi yayi amfani ya haska musu suka shiga ciki, tana shiga taga wayarta dake kan kujera tana kara tana dauka taga su elmustspha ne,kamar yadda tazata saida tagaji da surutunsu dakyar sukayi sallama ta kashe wayar tana kallon fahad wanda ke jiranta ta kammala wayar,

"Yadai?"

"Akwai abinci ne?"

"Da akwai guntu, kacinye ma kawai"

"To kekuma fa?"

"Karka damu zansha tea ya isheni"

"Shikenan..."

Dining yanufa ita kuma ta kishingida jikin kujerar tana dora rayuwar duniya a ma'auni na zahiri ba badini ba. Har ya gama cin abincin yadawo cikin falon bata bar tunani ba saida yazauna ya murza yatsunshi guda biyu asaitin fuskarta sannan ta dawo hayyacinta ta kalleshi,

"Ranki yadade lafiya kuwa?"

Ajiyar zuciya ta sauke,

"Lafiya lau kawai dai nagajine wallahi"

"To kije kici abinci mana ki kwanta ki huta"

"Gaskiya kam haka yakamata inyi bari natashi"

Tea taje ta hada tadawo falon ta zauna tasha zafi kuwa yace muje zuwa daki tashiga domin wanka zatayi ta kwanta tana cire kaya yadanno kai bayan yaturo kofa, tukwicin harara yasamu shiyasa cikin azama yafada toilet yayi alwala yafito bai yadda ya kalli wurin da takeba yafice daga dakin bayan yadauki abin salla,

"Haka kawai wai mutum da halal dinshi amma ayita nuna masa fin karfi da iko..." Haka yaketa fada cikin kunkuni lokacin da yafita falo, abin sallar ya shimfida yatada kabbarar sallar ishah. Dan neman fada bai shiga dakinba saida ya daidaici ta kwanta domin yaga yadaina ganin haske sai duhu alamun takashe fitilar data kunna, tashi yayi ya dauki abin sallarshi yanufi cikin dakin yasan bata son haske gashi tun yana salla aka dawo da wuta amma ita bata saniba,yana shiga ya lalubi makunna ya kunna nan wani fitinannen haske ya gauraye dakin, dan karamin tsaki taja tayi saurin rufe jikinta,

"Wai dan Allah menene haka? Shigo min dakin da kayi cikin wannan lokacin bai isheka ba har sai ka kunna min haske..."

"Yi hakuri dama nazaci ko baki san andawo da nepa bane..."

"To da aka dawo da ita me zanyi mata? Ko nace maka ina bukatane?"

"Ni na san abinda zakiyi da itane madam.... Nidai kawai na fada mikine"

Banza tayi masa ta juya baya tayi kwanciyarta,

"Malam idan kagama nidai ka rage min hasken nan ya takura min..."

"Nima ai kin takura min..." Yafada cikin kunkuni, bata bi takanshi ba ta mayar da idonta tarufe, saida yagama jula jularshi sannan yakashe yashiga wanka, acan yashirya yafito yana ta kukkumbura baki kamar tana ganinshi, acikin duhun ya kwashi kayan shimfidarshi yayi falo yaje ya shimfida a position din jiya sannan yakoma ya dauki pillow irin daukar nan na ehh ina cikin fushi dan kawai fincikar shi yayi yai gaba,

"Ahh malam menene haka? Karka yaga min pillow mana..."

Yaji tace yana daf da isa bakin kofa,

"Sai anyaga din" sai dai shi tashi maganar yadda bazata jiyoba yayi, bude kofa yayi yafita yaje ya kwanta,

"Haka kawai dan kinga kin fini shine zakiyita takura min.... Allah sai nima na rama wata rana tom"

Shi kadai yake maganarshi har yagaji yahakura yayi shiru, yauma kamar jiya raba dare yayi yana chaten daga bisani yasauka yayi addu'ar bacci.....

*Book dinnan na saidawa ne yar uwa idan kinada bukata ki siya saiki karanta.*

*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO.*

*KAMAR DA WASA....!*

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

*21*

***Yau anyi sa'a bai tashi da daddare ba saida asubah lokacin har anshiga masallaci, alwala yashiga yayi yafito anan cikin bedroom din yayi salla sai bayan da ya idar sannan yakoma makwancinsa yasake dora wani sabon baccin dan har bilkisu tatashi tayi wanka tashirya yana bacci saida ta shiga kitchen sannan yatashi, da kanshi ya nade shimfidar da ya kwana yashigar cikin dakin ya ajiye komai a muhallinsa sannan yashiga wanka ganin shi kadai ne adakin yasashi fitowa daga shi sai dan karamin wandonshi iya cinya dan baima kai rabin cinyar ba, lokacin ita kuma tana kitchen tana girki sai ta tuna jiya maama tace mata da dasu Hindu zasuzo amma sunce zasu mata yau ita kuma ta manto almiskinta da wani turarenta Arabian night a handbag din meenah wannan dalilin ne yasata cewar bari ta dauko wayarta takira meenah ta tuna mata kar akuma manto mata su yau ma. Tana fitowa falo taga baya nan alamar yatashi kenan, bedroom din tashiga itama kanta tsaye, tana shiga yana fitowa cikin sauri yayi baya zai koma bathroom din ita kuma fita tayi daga dakin takoma falo ta tsaya ita bata wuce kitchen dinba haka kuma bata koma dakin ba saida ta daidaici yagama kintsawa sannan ta bude ta shiga, yana gaban mirror yana taje sumarshi da cumb yasa bakin jeans da bakar t shirt mai gajeren hannu, ta cikin mirror din suka hada ido yaturo baki yana kallonta,

"Gaskiya daga yanzu idan zaki shigo kema ki rinka taking excuse.... Haka kawai kinzo kin wani kalleni"

Ita maganar tashi ma dariya tabata, wucewa tayi ta dauki duka phones dinta saida tazo saitinshi sannan ta tsaya,

"Kai excuse din kake nema kafin kashigo min daki? Kafara tukunna sai nima infara"

Tura mata baki yayi yana shagwabe fuska,

Ta cikin mudubin yake binta da kallo tana jujjuya masa baya lokacin data doshi kofa domin fita kasancewar dinkin jikinta riga da skirt ne wanda ya dinka mata lokacin bikin kannenta, karasa fesa turarenshi yayi ya ajiye gaban mirror dinta sannan yafita, afalo ya tarar da ita tana yin waya da meenah tana tuna mata sakonta dake cikin jakarta domin tana sa ran gobe zata fara salla, zama yayi yana jiran tagama, kitchen tawuce taje ta kwashe dankalin da take soyawa ta soya kwai sannan ta debo zuwa kan dining, bai jira anyi masa tayiba yataso yazo ya zauna,

"Sannu da aiki, ina kwana?"

"Yawwa katashi lafiya"

Ta amsa masa tana zuba nata dankalin acikin flate tana gamawa ta tura masa sauran gabanshi,

"Lafiya lau hajjaju.." Yafada yana lankwasa yan yatsunshi suna yin kas kas,

"Wai kai meyasa baka iya ninke kayaba idan kacire? Sai kawai ka rinka watsa min su cikin drewar any how?"

Dakatawa yayi da hada tea din da yakeyi ya kalleta yana shafa sumarshi,

"Ranki yadade wai dan Allah meyasa banida wahalar laifi ne awurinki....? Allah yabaki hakuri zan gyara"

"Ba maganar bakada wahalar laifi bane, ai gaskiya ce"

"To shikenan dai tunda ai nabaki hakuri"

Daga shi har ita babu wanda yasake magana cin abincinsu kawai suka sa agaba, itace tafara tashi nan yabita da kallo dama tun dazu jikinta yake bata irin kallon kurullar da yake yimata sannan tasha kamashi yana satar kallon kirjinta lokacin da suna cin abinci shiyasa tawuce bedroom tasako hijab har gwiwa tazo taci gaba da hidimominta, baki yatabe yatashi bayan yagama da komai na wurin,

"In kinyi hakuri ma ni gidan zan fice inbar miki yanzun nan..."

Yafada acikin zuciyarshi, tana tsaye tana shara da standing broom duk da falon babu wani datti, kusa da ita yazo yatsaya,

"Ranki yadade ni zan fita neman kudi, dinkuna ne kecan suna jirana sunfi kala ashirin gara naje na dan rage..."

"Allah yabada sa'a, amma cefane fa wazan bawa ya siyo min?"

"Bari idan naje shago zan aiko yaro ya kawo miki"

"Shikenan"

Fita yayi yaji shiru batace komai ba sai yakara dawowa,

"Yadai?"

"Uhmm ai banji kinyi min addu'a bane"

"Adawo lafiya, Allah yabada sa,a"

"Amin hajjaju, wallahi har naji dadi, i luv u irin wujiga wujiga dinnan"

Ita dariya ma yabata kawai ta girgiza kai taci gaba da shararta, saida tagama komai nata sannan tayi baki wasu mata guda biyu wadanda makotanta ne amma da dan tazara tsakaninsu sai dai duk kana iya hango gidajensu daga kofar gidanta, sosai ta karbesu da fara'a da kuma sakin fuska da zasu tafi ta dibar musu kayan zaki cikin leda tarakasu kofar gida sannan tadawo ta zauna tama rasa me zatayi gashi laptop dinta na wurinsu meenah duk yau zasu kawo mata da tana nan da ta dan rage zaman nan haka dan dole dai sai kallo ta kunna.

Fahad gidansu yafara zuwa ya iske su maryam nata shiri wai gidansa zasu tafi bai hanasu ba dan yaga jininsu yahadu da na bilkisu, bayan sun gaggaisa dasu ayiyah yatafi shago ai yana shiga aka fara tsokanarsa,

"Ga ango ga ango"

Dariya yayi yarinka binsu daya bayan daya suna gaisawa, kayan da ya yanyanka yaciro zai fara hadawa,

Bai jima da zuwaba saiga husnah jikinta ma farin uniform ne da alama daga lecture tafito ashe ko jiyama saida tazo dubashi taga bai fito ba,

Zama tayi agabanshi ta kura masa ido lokacin da yake dinki wani kyau na musamman taga yayi shiyasa kishi ya turnuketa nan da nan,

"Husnah ya makaranta...?"

Badan tasoba tasaki ranta gudun karya gane amma shi tuni yakaranci yanayin da take ciki domin dama yasan bakin kishinta akansa,cikeda son yasake kular da ita yace,

"Baki tambayi matata ba"

Tabe baki tayi ta dauke kai, yana kokarin juya rigar da yake dinkawa tarike rigar tana kallonshi,

"Prince katsaya mana mugama hirar sai ka cigaba da dinkin"

"To husnah ai yanzu ma hirar mukeyi"
Chapter 20 · 0% Book details