← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 67

Sashe 1

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

[11/28, 08:14] Hafsat Rano: © _*HASKE WRITERS ASSO.*_

*KAMAR DA WASA....!*

_*NA*_

_*UMMI A'ISHA*_

_DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI._

*1*

"Masu sauraro kamar kullum anan shirin namu zai dasa aya ayau kun dai ji mun tattauna akan wata babbar matsala wato ta yadda zakaga saurayi da budurwa sun kwashe shekaru suna gudanar da soyayya amma abin haushi arabu batare da anyi aureba shin laifin waye? Mazan ko matan? kafin inyi sallama daku ina mai janyo hankalin masoya da arike amana, gaskiya da kuma kulawa sannan aguji karya da yaudara domin hakan ba abune mai kyau ba sannan daya daga cikinsu yana raunata soyayya kuma ya illatata, anan zanyi sallama daku sai Allah yakaimu sati nagaba inda zaku jini acikin wani sabon shirin naku mai farin jini wato *Sakon na masoya ne...* kamar kullum nice taku mai gabatar da shirin wato *BILKISU LUKMAN ALIYU* Nabarku lafiya...."

Ahankali yake zare earpiece din dake kunnenshi sakamakon jin wakar _Sulken so...._ ta maye gurbin zazzakar muryarta, cikeda takaici ya kifa kansa asaman keken dinkin da yake zaune akai yana dinka wata kyakkyawar doguwar riga ta mata, tunani yake aransa yanzufa shikenan bazai sake jin muryarta ba sai wani satin indai ba shirye shiryenta na baya wadanda yayi recording zaiji ba domin hatta wannan wanda ta gabatar ayau ma yayi recording dinshi yana nan ajiye cikin wayarshi. Babu zato babu tsammani yaji wani abu saman sumarshi mai kamada almakashi, hannu yasa domin yakamo abin amma yaji anjanye ahankali yabude lumsassun idanuwanshi yatashi zaune, kamar yadda yayi zato husna yagani tsaye sai faman yi masa murmushi take, maimakon ya mayar mata da martanin murmushin da take yimasa sai ya daure fuska kamar ta kawo masa sakon mutuwa.

Bata damuba tabawa kanta masauki da wata kujerar roba wadda ke ajiye agaban keken dinkinshi, bata damu da yanda sauran abokan aikinshi wadanda ke zaune akan kekunansu suna gudanar da ayyukansu yanda zasu dauketa ba domin idan da sabo tasaba, zama tayi ta tallafe kumatunta da hannuwanta tana kallonshi kamar yadda yayi sai dai shi sam ba ita yake kallo ba domin yafada duniyar tunani.

"Prince..., Prince....ina dinkin yarinyar nan?"

Sai lokacin yadawo hayyacinsa sakamakon maganar tj abokin aikinsa da ta daki dodon kunnuwansa, gefenshi ya duba ya ciro wasu kaya acikin leda ya mika masa,

"Wai meke damunka fahad?"

Kallonta yayi adage sannan cikin rashin kulawa yace,

"Mekika gani fa?"

"To ai naganka ne kamar wani marar lafiya" tayi maganar cikin kalar tausayi,

"Lafiya ta lau..." Yabata amsa yana kokarin mikewa tsaye, wata leda ta mika masa tana langwabe kai,

"Please my prince ga uniform dina ka dinka min kaji"

Batare da ya kalleta ba ya karba ya jefa cikin wani kwali dake girke gefen kekensa,wani food flask dan madaidaici mai kyau ta sake mika masa,

"Ga abinci na kawo maka"

Karba yayi ya dora saman keken dinkinsa sannan ahankali kamar wanda tayiwa dole ya furta,

"Thank u"

Jingina tayi tana kallonshi shi kuma yana kallon wayarshi, babu abinda kake ji sai karar keken dinki wanda sauran abokan aikinshi keta faman aiki. Scissors din da ke ajiye kan kekenshi ta dauka ahankali ta kai kan tararriyar sumarshi,

"Inyi maka aski?"

Sake daure fuskarshi yayi yakai hannu ya doke almakashin,

"Kibari bana so, nafada miki bana son wasan banza"

Murmushi tayi tana sunkuyar da kanta,

"To kayi hakuri"

Baice mata komai ba yatashi da niyyar fita nan itama ta mike tana kallonshi ganin haka yasa shi yafasa fitar yawuce can wani lungu kusa da wata drawer ya kwanta, duk da tana son su fita tare amma haka tayi hakuri tawuce tatafi ba don taso ba.

Yajima kwance awurin yana jin sauran yan shagon sunata gulmarsa shida husna amma bai tanka ba har saida lokacin sallar la'asar yayi sannan yatashi,alwala yayi ya shiga masallaci duk da yana son ganin salim abokinshi amma sai yashare yashiga salla wanda acan din yahadu da salim din.

Yana fitowa daga salla keke napep yatare yanufi gida, atsakar gida ya iske mahaifiyarshi tana wanki koda yakarasa kusa da ita kamar yadda yazata kananan kayanshi take wanke masa.

"Ayiyah wankinne dai?"

Murmushi tayi tajuyo ta kalleshi,

"To ai ba komai nakeyi ba shiyasa nace gara inwanwanke maka sauran kayan ma na hadasu zuwa gobe zan bayar akai awanko maka"

"Godiya nake Ayiyah tah, Allah dai yabar min ke"

"Amin autana, maza kaje ga abincinka can a falo na tanadar maka"

Yunkurawa yayi ya mike daga tsugunnen da yake hakan yayi daidai da fitowar mamu,

"D'an nema kadawo ashe?"

"Hajiya mamu wallahi nadawo, kina daga ciki kenan?"

"Andai ji kunya, gandamemen saurayi dakai amma baka iya wanki ba"

Kafin yayi magana ayiyah tayi caraf ta cafke zancen ta hanyar bawa mamuh amsa,

"Tunda yana da masu yimasa ai ko ya iya bashida amfani"

Wata shewa mamu ta saka tana karasowa inda suke,

"To nidai naga yanda za ayi duk ranar da akayi masa aure"

"Yakuwa za ayi? Matarsa ce zata rinka yimasa"

"Idan ta iya ko?"

"Sai ta koya" inji ayiyah, jan yar karamar kujerar tsugunno mamu tayi ta zauna kusa da ayiyan, shi dai bazai iya cigaba da kallon wannan dramar tasu ba shiyasa yawuce dakin ayiyah fuskarshi shimfide da murmushi domin idan da sabo yasaba ganinsu ahaka kusan tun tasowarsa ahaka yake ganinsu bai taba jinsu suna fada ba kai idan baka saniba baka taba cewa kishiyoyine dan ko yanzun ma da suka gama wannan rahar hira ya jiyosu suna yi kuma da alama wankin mamuh take taya ayiyah. Zama yayi saman daddumar dake shimfide cikin falon yasoma bude kwanukan dake jere reras awurin wanda yasan shi aka tanadarwa domin kullum haka ayiyah keyi masa kamar wani mai gida, funkaso da miyar taushe yagani sai shinkafa da wake da manja da salad sannan ga zubo nan mai sanyi da kankara aciki cikin wani madaidaicin jug, hannun riga ya nade yasoma zuba shinkafa da waken domin kusan abubuwan nan na soye soye irinsu waina, sinasir, funkaso duk ba damunshi sukayi ba dan haka yazage yaci shinkafa da wakensa yayi dam yasha sanyayyen zobonshi daga haka ya mike ya fito,su ayiyah har sun kammala wankin sun fada wani aikin kuma sunayi suna hira shiyasa ma ko ganin fitowarshi basuyi ba, dakinsu ya nufa wanda yake cikin soron dake hanyar kofar gida yabude yashiga daga shi sai yayanshi Abba adakin amma yanzu abban baya nan yana can jami'ar Maiduguri wato unimaid yana karantar computer science dan haka sai shi kadai adakin yanzu, kayan jikinshi yarage yabar gajeren wando kadai bayan ya Kara kofar dakin, kan dundumemiyar katifar dake malale adakin yahau ya kwanta bai kai ga rufe idanuwansa ba yajiyo alamun karar shigar sako cikin wayarshi, akasalance ya mika hannu yadauko wayarshi kirar Galaxy S10,BILKISU shine password din kan wayar tashi nan yabude yasoma duba text din duk da baiyi saving number dinba yagane husna ce domin har ya haddace number dinta saboda yanda take damunsa arana sai ta kirashi akalla sau biyar ko fiyeda haka banda text massages kai idan takira ma taji shiru abune mai sauki yaganta ashagonsu ta biyo sawunshi yarasa gane kan wannan yarinyar gashi ta tsani ta ganshi da wata mace suna ko maganane alhalin kuma shi aikinsa na matane tunda dinkin mata shine sana'arshi. Sakon yabude yasoma karantawa kamar haka... _"Ya fahad yakake, ina fata lafiya kake, abincin yayi dadi?"_ murmushi yayi ya ajiye wayar bayan yasata a silent domin shi sai yanzu ma yatuna da wani abincin da ta kawo masa dazu saboda can yabaroshi ashago bararrajewa yayi saman katifarshi domin yin bacci duk da yasan ayiyah ta hanashi wannan dabi'ar ta baccin yamma amma babu yanda zaiyi ne sakamakon yagaji dayawa gashi ya jima bai samu isasshen bacci ba kullum yana kan keke yana dinki.

***

Murmushi tasaki ahankali wanda yayi sanadiyyar bayyanar fararen hakoranta sannan ya bayyanar da kyawawan beautiful point dinta wadanda ke kara kawata kyakkyawar fuskar da Allah yayi mata. Wayar dake makale a kunnenta take jujjuyawa cikeda annashuwa,

"Yes half soul, yanzu dai kabari sai nakoma gidan kawai sai naturo maka...."

Dan Jim tayi tana sauraron abinda yake fada bata kai ga bashi amsaba tamike daga kujerar datake zaune wacce ke rukunin kyawawan kujerun dake zagane cikin zungureren office din wanda ke dauke da kayan alatun more rayuwa banda na'urar sanyaya daki wacce ta cika dakin da sanyi wanda bazai cutar da jikin dan adam ba, jakarta ta dauka wadda take ajiye bisa dogon teburin da ke tsakanin rukunun jerarrun kujerun masu fuskantar juna, hakan yayi daidai da shigowar khulsum kawarta,

"Noorul kalb ga khulsum ta shigo zamu tafi ni ina ganin kawai kabari sai naje gida din kawai sai muyi waya ko?" Batare da khulsum tajiyo amsar da yabata ba taga tayi murmushi sannan ta amsa da,

"Zataji half soul, me too"

Daga haka ta katse wayar tana kallon khulsum,

"Wai har kin kammala voicing din?"

"Tun yaushe, ina can inata jiranki amma najiki shiru ashe kina nan kina soyewa"

Murmushi tayi ta saba jakar hannunta suka doshi kofa domin fita daga office din,

"Nima fa yanzun nan nagama fassara labaran kasuwancin nan kin san yanada wahala shine kuma hamood yakirani,namanta ma yace yana gaisheki"

"Ina amsawa, am yawwa kafin namanta wai ke mekike shirya mana ne abikin nan?"

Juyawa tayi ta kalli khulsum sannan ta harareta,

"Me zan shirya muku kuwa, ko nice amaryar da zakiyi min wannan tambayar? Ban son wulakanci"

Murmushi khulsum tayi ta dafa kafadarta,

"Bakece amarya ba amma ai kece babbar yaya kuma uwar biki kinga kuwa yazama dole kiyi wani abu"

Lumshe idanuwanta tayi sannan ta budesu bayan yanayin fuskarta ya sauya cikin sakannin da basu gaza biyu zuwa ukuba,

"Ni yanzu duk ba wannan ba wallahi abunda ke damuna guda dayane zuwan Grandma dinmu iyallo, yanzu tana zuwa zatabi ta uzzurawa mutum ta daga masa hankali, tun lokacin bikin mamaa take damuna gashi yanzu bikin Hindu da meenah yazo, ni wallahi ji nake kamar inbar gidan sai angama bikin nadawo"

Murmushi khulsum tayi bayan taja ta tsaya kamar yadda taga tayi,
Chapter 1 · 0% Book details