Sashe 24
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Washe gari akayi salla, tun da aka sauko taketa samun baki,fahad ya hade cikin dark blue din shadda harda hula yayi kyau sosai, saida yaci abincin sallar da tayi sannan yafita, su mariyane sukayi mata rabon abinci, aranar da yamma sukaje gidansu fahad din ita dashi barka da salla da gidan yayyenshi washe gari kuma sukaje gidansu Bilkisu, bayan salla da kwana biyu kuma suka tafi garko gaida hajiya iyallo.
Bayan salla da kwana biyar saiga fahad da sabon roba roba dama tun safe taga yafice ranar bai zauna yayi baccin safen nanba,tana tsakar gida tana karatun littafin hausa yashigo gidan da babur din,dakatawa tayi da abinda takeyi ta tsaya tana kallonsa daga shi sai three quarter da bakar t shirt,sam bata san cewar ahaka yafita ba sai yanzu,
"Wannan roba robar fa...?"
"Ranki yadade nawane,dan kudina da na samu da sallar nan ne duk na tattare naje nasiyo machine dinnan"
"Allah yasanya alkhairi, kuma shine kafita har wata uwar duniya ahaka?"
Kallon jikinsa yayi bayan yakafe Babur din,
"Meya faru da bazan fita ahaka ba?"
Girgiza kai tayi taci gaba da abinda takeyi,
"Yadai kamata idan angirma asan angirma..."
Murmushi yayi yana shafa sumar kanshi,
"Hakane, bari nayi wanka naje nayi aski sumata tafara yawa..."
Bata tanka masaba yawuce ciki, saida tagama abinda takeyi sannan tatashi tana kallon babur din nashi, farine tass sabo fill sai kyalli yake yi abayan machine din wurin daura lamba andaura wani kyakkyawan abu mai kamada madubi wanda ajiki aka rubuta _prince_ adan karkace, girgiza kai tayi azuciyarta tana cewa,
"Wannan yaron kana fama da kuruciya.."
Falo tashiga baya ciki da alama yashiga wankan da yace zaiyi, bedroom tawuce domin ajiye nail cutter din da tagama amfani da ita, maganarshi tajiyo daga cikin bathroom,
"Hajjaju dan Allah kifita zan fito.... Wallahi babu kaya ajikina"
"Ni nasa kashiga wankan ahaka?"
Bakin kofar ya matso sosai,
"Gaskiya kifita, kemafa boye min kikeyi ba dole nima inboye jikina ba"
Bata kara bi takansa ba ta ficewarta dama ba zama tazo yiba saida ya tabbatar tafita sannan yafito daga shi sai towel, agurguje yashirya wai dan kar tashigo ta sameshi ahaka, kananan kaya yasaka sannan yafita falo, abincin shi da yafita baici ba ya dauko yaci sannan yafice, su ayiyah yaje yakaiwa Babur din suka gani da sauran yan uwa dake kusa ranar ko filin ball baijeba dan bashi yadawo gidanba sai bayan sallar ishah kasancewar babu wuta agari yasa bilkisu bata samu zarafin ganin askin kanshi ba da yayi, yana dining yana cin tuwon da tayi na semo miyar busasshiyar kubewa wacce taji busasshen kifi tashiga daki abinta tayi shirin bacci. Kudurtawa yayi aransa cewa nan bada jimawa ba zai kawo canji awannan zaman nasu, gaskiya yazama dole suyi rayuwa irin wacce kowanne miji da matarsa keyi, kamar kullum shimfidarsa yayi afalo ya kwanta bacci, washe gari tatashi da farin ciki domin su maama sunce mata zasu zo su wunar mata duk da itama ayau bata tashi da wuriba makara tayi, saida tafara yin wanka sannan ta fito domin shiga kitchen, yana kwance saman doguwar kujera husnah nata damunshi da kira ganin tayi masa miss called har guda uku yasashi dagawa a na hudun hakan yayi daidai da fitowar bilkisu bata ko kalleshi ba tawuce kitchen abinta, saida yagama wayar da yakeyi sannan yashiga wanka batare da ya debe shimfidarshi ba, yana gaban mirror yana taje sumarshi bilkisu tashigo binshi tayi da kallo musamman ma sumar kanshi domin wani irin aski ne akayi masa duk an saisaye gefe da gefe amma tsakiyar ba ako taba ba,
"Hajjaju na ina kwana?"
Saida tasake kallon kanshi sannan ta amsa da,
"Lafiya lau, yanzu dama wannan shine askin da kake cewa zakayi? Gaskiya yakamata kasan kagirma wallahi"
Wani dan malalacin murmushi yayi ya kalleta ta cikin mirror din yana cigaba da taje kanshi,
"Wai hajjaju sai kiyita cewa nagirma bayan har yanzu ban girmaba tunda babu wani abu da ya canja.... Ina dai saka ran zan girman very soon wallahi kuma no marcy"
"Ni ba dogon bayani na tambayeka ba, waccan shimfidar da ka kwana akai wa kabarwa ya dauke maka?"
"Matata mana..."
Kallonshi tayi sosai sannan tajuya tafita batace dashi komai ba, koda yagama yafito yanata tutturo baki ya harhada kayan ya kwashe yakai ciki sannan yasake fitowa lokacin tagama hada komai na karyawa saida yayi breakfast sannan yamike yana kallonta,
"Ranki yadade mu mun tafi shago zamu karasa dinka kayan da basu samu shiga da salla ba"
"Allah yabada sa'a"
"Amin godiya nake"
Gidan tagyara bayan fitarsa tana gamawa takoma kitchen tahada wanke wanke tafara bayan tagama tashiga bedroom tana gyarawa taji sallamar su maama nan gida ya rude da farin cikin ganin junansu da sukayi su ukune sukazo har huda ta hudu bajewa sukayi afalo suna shagali.
A lissafin bilkisu yau zata koma aiki shiyasa tatashi da wuri tayi komai nata na aikin gida sannan tayi shirin fita nan fahad yace zai kaita a machine dinsa dama bata taba hawaba ba wai dan tasoba tayarda, tana gama shiryawa shima yafito da three quarter da body hug,
"Kasan me? Nifa bazaka kaini ahaka ba gaskiya, meyasa kake hakane?"
"Gaskiya hajjaju kina yawa..."
Ciki yasake komawa yasako jallabiya ruwan kasa yadawo yadauketa suka tafi yau kam jinsa yake acikin wani yanayi wanda bai taba tsintar kansa ba, kusancinsu da bilkisu ya haifar mata da wani lamari mai girman gaske kun san yanda lifan yake wurin zaman baida wani girma, abakin gate din office dinsu ya ajiyeta bai bari taga idonshi ba yayi wani kasa da ido, saida yaga shigarta ciki sannan yajuya yatafi. Da tatashi ma shi yaje ya daukota yasamu khulsum nata yimata tsiya itama tana ramawa, koda ya kawota gida baiko shigaba yakoma shago. Da daddare kuwa har tafara bacci taji shigowarsa dakin yana kokarin yin shimfida agaban gadonta, kallonshi tayi bayan tasa hijab tatashi zaune,
"Ji mana malam, me zakayi?"
"Bacci, yau anan zan kwana"
"Saboda wanne dalili?"
"Wallahi yau tsoron kwana ni daya nakeyi, dan Allah karki koreni"
Komawa tayi takwanta tana cewa,
"Tun da lokacin da kake kwana afalon bakaji tsoronba sai yanzu?"
"To ai ban taba tsorata ba sai yau shiyasa"
Juya masa baya tayi taja bargo tarufe gaba daya jikinta tana cewa,
"Nidai idan kagama ka kashe min wuta pls"
Duk da baya son duhu amma babu yadda ya iya haka yakashe wutar tunda yanaso ya kwana adakin atunaninsa tahakanne kadai zai sa yakara samun kusanci da ita. Washe gari tana son taje kitso ta can kuma zata biya ta gidansu khulsum domin ta dubata saboda taga text dinta cewar bata da lafiya yau, shine yakaita duk inda zataje bayan tagama yakoma daukota, kallonshi tayi sama da kasa yana sanye da koriyar t shirt mai gajeren hannu da hoton tsintsaye ajiki anrubuta angry birds, sai bakin wando mai kyau amma dan tsiya an yanke gwiwar an wani tsagashi shiyasa ga gwiwarsa nan awaje ga wani dan banzan askin da ya sarkaba yanzu irin wadanda yan kwallo keyi ko musicians awani saisaye gefe da gefe amma kuma tsakiyar atara uban suma, ita duk ma ashigar tasa wannan askinne yafi yimata takaici,shi dai kallon tsaf yake yimata ta cikin bakin glass din dake fuskarsa kasancewarshi mai hasken fata glass din ba karamin kyau yayi masa ba dama yanzu baya raboda saka glass tunda yasai babur saboda iska da kwarukan dake fadawa mutum ido idan yana tuki,
Yanda take kare masa kallo haka shima yake kare mata kallon batare da ta saniba,
"Wai kai dan Allah sai yaushe zaka girma ne? Kullum kai kenan cikin shiga marar kan gado"
"To hajjaju wai yau kuma meye laifin shigar tawa?"
"Oho..."
Daga haka ta tattare skirt dinta ta hau machine din, juyawa yayi ya kalli kafarta duk kwaurinta awaje yau bata saka safa ba,
"Ranki yadade ki sake jan skirt din naki kirufe kafarki"
"Muje kawai ko naja ba rufewa zaiyi ba tunda ba zani bane"
Saida ya tura baki sannan yafigi machine din yaringa bin lungu wai dan kar yabi ta cikin gari mutane su ganta.
***
Ahalin yanzu basuda wani matsala a zamansu sai dai fa har gobe zamane suke yinsa irin na yaya da kani bawai mata da miji ba domin har yau dagashi har ita basu san menene aurenba suna dai zaune ne kawai tsawon watanni biyar da aurensu, tun ranar da yace mata yana jin tsoron kwana shi kadai yadawo kwana cikin dakin amma yana kasa ita kuma hakimar na kan gado,yau tunda asuba taga kiran maama tana dagawa taji tace mata ankai meenah asibiti ana zaton ko haihuwace, nan tayi maza tashiga kitchen domin hada abincin da zata tafi musu dashi asibiti dama shiyasa yanzu bata kashe wayarta da daddare saboda tana tunanin za anemeta saboda daga meenah har Hindu cikinsu yatsufa, fahad yana kwance yanata baccinsa bai san meyake gudana ba saida tagama komai tayi wanka sannan ta tasheshi lokacin karfe 6 nasafe, da kayan dake jikinsa ya dauki key zai fita ta dakatar dashi,
"Ba dai ahaka zaka fita ba ko?"
Fasa fitar yayi yaje yacire armless din rigar dake jikinsa yasaka jallabiya harda hula sannan yafita, suna tafe yana ta kunkuni,
"Wai sai anyi abu ace wani kagirma bayan har yanzu ayaronka kake tunda babu abinda ya canja... Hmmmm zan girman dai akwai lokaci"
Bayan salla da kwana biyar saiga fahad da sabon roba roba dama tun safe taga yafice ranar bai zauna yayi baccin safen nanba,tana tsakar gida tana karatun littafin hausa yashigo gidan da babur din,dakatawa tayi da abinda takeyi ta tsaya tana kallonsa daga shi sai three quarter da bakar t shirt,sam bata san cewar ahaka yafita ba sai yanzu,
"Wannan roba robar fa...?"
"Ranki yadade nawane,dan kudina da na samu da sallar nan ne duk na tattare naje nasiyo machine dinnan"
"Allah yasanya alkhairi, kuma shine kafita har wata uwar duniya ahaka?"
Kallon jikinsa yayi bayan yakafe Babur din,
"Meya faru da bazan fita ahaka ba?"
Girgiza kai tayi taci gaba da abinda takeyi,
"Yadai kamata idan angirma asan angirma..."
Murmushi yayi yana shafa sumar kanshi,
"Hakane, bari nayi wanka naje nayi aski sumata tafara yawa..."
Bata tanka masaba yawuce ciki, saida tagama abinda takeyi sannan tatashi tana kallon babur din nashi, farine tass sabo fill sai kyalli yake yi abayan machine din wurin daura lamba andaura wani kyakkyawan abu mai kamada madubi wanda ajiki aka rubuta _prince_ adan karkace, girgiza kai tayi azuciyarta tana cewa,
"Wannan yaron kana fama da kuruciya.."
Falo tashiga baya ciki da alama yashiga wankan da yace zaiyi, bedroom tawuce domin ajiye nail cutter din da tagama amfani da ita, maganarshi tajiyo daga cikin bathroom,
"Hajjaju dan Allah kifita zan fito.... Wallahi babu kaya ajikina"
"Ni nasa kashiga wankan ahaka?"
Bakin kofar ya matso sosai,
"Gaskiya kifita, kemafa boye min kikeyi ba dole nima inboye jikina ba"
Bata kara bi takansa ba ta ficewarta dama ba zama tazo yiba saida ya tabbatar tafita sannan yafito daga shi sai towel, agurguje yashirya wai dan kar tashigo ta sameshi ahaka, kananan kaya yasaka sannan yafita falo, abincin shi da yafita baici ba ya dauko yaci sannan yafice, su ayiyah yaje yakaiwa Babur din suka gani da sauran yan uwa dake kusa ranar ko filin ball baijeba dan bashi yadawo gidanba sai bayan sallar ishah kasancewar babu wuta agari yasa bilkisu bata samu zarafin ganin askin kanshi ba da yayi, yana dining yana cin tuwon da tayi na semo miyar busasshiyar kubewa wacce taji busasshen kifi tashiga daki abinta tayi shirin bacci. Kudurtawa yayi aransa cewa nan bada jimawa ba zai kawo canji awannan zaman nasu, gaskiya yazama dole suyi rayuwa irin wacce kowanne miji da matarsa keyi, kamar kullum shimfidarsa yayi afalo ya kwanta bacci, washe gari tatashi da farin ciki domin su maama sunce mata zasu zo su wunar mata duk da itama ayau bata tashi da wuriba makara tayi, saida tafara yin wanka sannan ta fito domin shiga kitchen, yana kwance saman doguwar kujera husnah nata damunshi da kira ganin tayi masa miss called har guda uku yasashi dagawa a na hudun hakan yayi daidai da fitowar bilkisu bata ko kalleshi ba tawuce kitchen abinta, saida yagama wayar da yakeyi sannan yashiga wanka batare da ya debe shimfidarshi ba, yana gaban mirror yana taje sumarshi bilkisu tashigo binshi tayi da kallo musamman ma sumar kanshi domin wani irin aski ne akayi masa duk an saisaye gefe da gefe amma tsakiyar ba ako taba ba,
"Hajjaju na ina kwana?"
Saida tasake kallon kanshi sannan ta amsa da,
"Lafiya lau, yanzu dama wannan shine askin da kake cewa zakayi? Gaskiya yakamata kasan kagirma wallahi"
Wani dan malalacin murmushi yayi ya kalleta ta cikin mirror din yana cigaba da taje kanshi,
"Wai hajjaju sai kiyita cewa nagirma bayan har yanzu ban girmaba tunda babu wani abu da ya canja.... Ina dai saka ran zan girman very soon wallahi kuma no marcy"
"Ni ba dogon bayani na tambayeka ba, waccan shimfidar da ka kwana akai wa kabarwa ya dauke maka?"
"Matata mana..."
Kallonshi tayi sosai sannan tajuya tafita batace dashi komai ba, koda yagama yafito yanata tutturo baki ya harhada kayan ya kwashe yakai ciki sannan yasake fitowa lokacin tagama hada komai na karyawa saida yayi breakfast sannan yamike yana kallonta,
"Ranki yadade mu mun tafi shago zamu karasa dinka kayan da basu samu shiga da salla ba"
"Allah yabada sa'a"
"Amin godiya nake"
Gidan tagyara bayan fitarsa tana gamawa takoma kitchen tahada wanke wanke tafara bayan tagama tashiga bedroom tana gyarawa taji sallamar su maama nan gida ya rude da farin cikin ganin junansu da sukayi su ukune sukazo har huda ta hudu bajewa sukayi afalo suna shagali.
A lissafin bilkisu yau zata koma aiki shiyasa tatashi da wuri tayi komai nata na aikin gida sannan tayi shirin fita nan fahad yace zai kaita a machine dinsa dama bata taba hawaba ba wai dan tasoba tayarda, tana gama shiryawa shima yafito da three quarter da body hug,
"Kasan me? Nifa bazaka kaini ahaka ba gaskiya, meyasa kake hakane?"
"Gaskiya hajjaju kina yawa..."
Ciki yasake komawa yasako jallabiya ruwan kasa yadawo yadauketa suka tafi yau kam jinsa yake acikin wani yanayi wanda bai taba tsintar kansa ba, kusancinsu da bilkisu ya haifar mata da wani lamari mai girman gaske kun san yanda lifan yake wurin zaman baida wani girma, abakin gate din office dinsu ya ajiyeta bai bari taga idonshi ba yayi wani kasa da ido, saida yaga shigarta ciki sannan yajuya yatafi. Da tatashi ma shi yaje ya daukota yasamu khulsum nata yimata tsiya itama tana ramawa, koda ya kawota gida baiko shigaba yakoma shago. Da daddare kuwa har tafara bacci taji shigowarsa dakin yana kokarin yin shimfida agaban gadonta, kallonshi tayi bayan tasa hijab tatashi zaune,
"Ji mana malam, me zakayi?"
"Bacci, yau anan zan kwana"
"Saboda wanne dalili?"
"Wallahi yau tsoron kwana ni daya nakeyi, dan Allah karki koreni"
Komawa tayi takwanta tana cewa,
"Tun da lokacin da kake kwana afalon bakaji tsoronba sai yanzu?"
"To ai ban taba tsorata ba sai yau shiyasa"
Juya masa baya tayi taja bargo tarufe gaba daya jikinta tana cewa,
"Nidai idan kagama ka kashe min wuta pls"
Duk da baya son duhu amma babu yadda ya iya haka yakashe wutar tunda yanaso ya kwana adakin atunaninsa tahakanne kadai zai sa yakara samun kusanci da ita. Washe gari tana son taje kitso ta can kuma zata biya ta gidansu khulsum domin ta dubata saboda taga text dinta cewar bata da lafiya yau, shine yakaita duk inda zataje bayan tagama yakoma daukota, kallonshi tayi sama da kasa yana sanye da koriyar t shirt mai gajeren hannu da hoton tsintsaye ajiki anrubuta angry birds, sai bakin wando mai kyau amma dan tsiya an yanke gwiwar an wani tsagashi shiyasa ga gwiwarsa nan awaje ga wani dan banzan askin da ya sarkaba yanzu irin wadanda yan kwallo keyi ko musicians awani saisaye gefe da gefe amma kuma tsakiyar atara uban suma, ita duk ma ashigar tasa wannan askinne yafi yimata takaici,shi dai kallon tsaf yake yimata ta cikin bakin glass din dake fuskarsa kasancewarshi mai hasken fata glass din ba karamin kyau yayi masa ba dama yanzu baya raboda saka glass tunda yasai babur saboda iska da kwarukan dake fadawa mutum ido idan yana tuki,
Yanda take kare masa kallo haka shima yake kare mata kallon batare da ta saniba,
"Wai kai dan Allah sai yaushe zaka girma ne? Kullum kai kenan cikin shiga marar kan gado"
"To hajjaju wai yau kuma meye laifin shigar tawa?"
"Oho..."
Daga haka ta tattare skirt dinta ta hau machine din, juyawa yayi ya kalli kafarta duk kwaurinta awaje yau bata saka safa ba,
"Ranki yadade ki sake jan skirt din naki kirufe kafarki"
"Muje kawai ko naja ba rufewa zaiyi ba tunda ba zani bane"
Saida ya tura baki sannan yafigi machine din yaringa bin lungu wai dan kar yabi ta cikin gari mutane su ganta.
***
Ahalin yanzu basuda wani matsala a zamansu sai dai fa har gobe zamane suke yinsa irin na yaya da kani bawai mata da miji ba domin har yau dagashi har ita basu san menene aurenba suna dai zaune ne kawai tsawon watanni biyar da aurensu, tun ranar da yace mata yana jin tsoron kwana shi kadai yadawo kwana cikin dakin amma yana kasa ita kuma hakimar na kan gado,yau tunda asuba taga kiran maama tana dagawa taji tace mata ankai meenah asibiti ana zaton ko haihuwace, nan tayi maza tashiga kitchen domin hada abincin da zata tafi musu dashi asibiti dama shiyasa yanzu bata kashe wayarta da daddare saboda tana tunanin za anemeta saboda daga meenah har Hindu cikinsu yatsufa, fahad yana kwance yanata baccinsa bai san meyake gudana ba saida tagama komai tayi wanka sannan ta tasheshi lokacin karfe 6 nasafe, da kayan dake jikinsa ya dauki key zai fita ta dakatar dashi,
"Ba dai ahaka zaka fita ba ko?"
Fasa fitar yayi yaje yacire armless din rigar dake jikinsa yasaka jallabiya harda hula sannan yafita, suna tafe yana ta kunkuni,
"Wai sai anyi abu ace wani kagirma bayan har yanzu ayaronka kake tunda babu abinda ya canja... Hmmmm zan girman dai akwai lokaci"