Sashe 16
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Saida yagama ganin komai sannan yatashi yafita sallar magrib bayan ya kullewa salim dakinshi, daga can gidansu yawuce alla alla yake yi gobe tayi adaura aurensu da bilkisu shiyasa a wannan daren baccinshi rabi da rabine yayinda ita kuma amaryar ma gaba daya daren ranar kasa bacci tayi kwata kwata bare gashi bata salla balle tatashi tayi sallar nafila ko tarage damuwa shiyasa abun yayi mata yawa, juyi kawai tai tayi danma da alama agidan ba ita kadaici bata yi baccin ba domin tana jiyo kannen ammah sunata shan hira da yan garko awannan tsohon daren, sai daf da asubah tasamu bacci ya dauketa,wurin 6 da wani abu tatashi tayi wanka tashirya cikin daya daga cikin dinkin da fahad yayi mata,yake kawai takeyi amma zuciyarta cike take da damuwa da bacin rai, gashi ta kasa cin komai sai ruwan lipton kadai da tasha. Fahad kuwa tun asussubah yatashi dama bacci sama sama yayi shi, karfe tara zasu tafi garin garko inda acanne za adaura auren, kamar bilkisu shima kasa cin komai yayi dakyar ayiyah ta tirsasashi yasha ruwan koko daga nan wanka yayi, tun yana cikin toilet din yasoma jiyo hayaniyar mutane yan zuwa daurin aure domin kofar gidansu ne m point din, yana fitowa babu bata lokaci yazuba sabuwar farar shaddarsa harda babbar riga yasha turare, kai wannan ango yasha kyau gaskiya domin ba karamin fitowa yayiba fess, koda yafito kansa har wani sara masa yayi saboda al'ummar da yagani, abokanshi ne, yan shagonsu, abokan yayyenshi, yan uwa da yan unguwa ga uban tarin motoci jere reras, salim ne yakama hannunshi sukaje har gaban motar da zai shiga suka shiga nan kowa yashiga dama su baba sunyi gaba nan suma suka dauki hanya, haka kawai garin yayiwa fahad kyau bama shi kadai ba kusan kowa da wannan shine zuwansa nafarko garin ya burgeshi, babban masallacin garin acanne za adaura auren bayan an idar da sallar juma'a,
Bilkisu tana can gabanta sai faduwa yake wanda bata san dalili ba sai dai tana danganta hakan da wannan auren da za adaura mata shi yau gashi kuma ayau din za akaita gidansu fahad domin yau ammah ke gudanar da yininta shiyasa su maama sun kammala kintsa mata kayanta gaba daya hatta wanda zata tafi dasu gidansu fahad an shirya mata cikin daya daga akwatinta na lefe. Ana idar da sallar juma'a aka daura auren fahad da bilkisu akan sadaki naira dubu talatin,bayan an gama daurin auren sun daddauki hotuna suka dawo, direct gidansu bilkisu suka wuce lokacin tasake wanka tashirya cikin leshi riga da skirt,tun kafin tafito su meenah suka rigata sukaje sunata hotuna da ango da abokansa,ita kam adole tafita itada khulsum bayan angama yimata kwalliya,
Kasa kasa take kallonshi tana son taga koda gaskene yayi kyau din kamar yadda taji su hindu nata zuzutawa, babu laifi kam yafito sosai,shima anasa bangaren tunda ya hangota hankalinsa yayi kaura daga gareshi yakoma kanta saboda ta hadu iya haduwa shiyasa har dana sanin kwaso abokansa suzo ganinta yayi, wani kishine ke lullube zuciyarsa sama sama duk abinda yakeyi idonshi na kanta, saida suka gama yin hotuna da mutane sannan yamatso wurinta nan fa kowa yarude da daukarsu awaya, ita haushima abin yake bata,
"Barka da yau Hajjaju...,ya fama da jama'a?"
"Alhamdulillah"
Shine abinda tafada kawai suka cigaba da hotuna, ana gamawa bilkisu takoma gida, angwaye dai daga can wurin walima suka wuce wadda zasu gabatar afilin makaranta. Bayan su Abba sun dawo kiran bilkisu yayi domin abata sadakinta sannan yakara yimata Nasiha shida waliyyinta, duk saida tabi ta bata kwalliyar fuskarta da hawaye da kuka shiyasa tun daga lokacin ba akara samun kanta ba har dare lokacin da za arakata domin fada ne na iyaye daga wannan yagama sai wannan yazo yayi nasa, ya mudan shima harda zuwa yayi mata nasihar azauna lafiya sannan yabawa maama dubu goma yace abata Allah yasanya alkhairi, tun bayan magriba su khulsum ke binta tatashi tashirya amma taki tashi saida aka fadowa ammah ai iyallo naji tazo tahau fada babu shiri tatashi tashiga bathroom tayi wanka tafito, abinci kam rabonta dashi tun jiya da rana, kayan da zata saka sai faman jikeshi da turare su meenah keyi kamshin har hawa mata kai taji yanayi, hatta pant din da zata saka gani tayi maama na shafeshi da almiski, tabe baki tayi tazauna gefen gado ta bude drewar din gadonta ta dauko pad ta warce pant din a hannun maama azuciyarta tana cewa,
"Yara kwayi kwa gama"
Bra din da zata saka ma itama saida suka tsuma ta da turare daga nan kuma suka dawo kanta itama zasu shafeta da madarar turare, tana ki tana komai saida suka shafa mata sannan tasaka kayanta tanemi wuri ta zauna duk da tanaji ana cewa tafito amma taki koda motsi saida su hajjaye suka zo suka fito da ita, saida aka kaita wurin ammah da abba tayi musu sallama sannan aka fita da ita inda motoci ke jira, kawarta khulsum ce agaba sai su iyallo da suka sakata atsakiya ba awuce dasu ko inaba sai gidansu fahad inda dangi sukayi dafifi suna jiran zuwansu, dakin ayiyah aka kaita tana lullube cikin babban mayafi, saida aka gama yan gaishe gaishe da taya juna murna sannan aka damka amanarta a hannun su ayiyah daga nan yan kawo amarya suka tafi bayan su maama sun shigo mata da akwatinta.
Duk dauriyarta saida tayi hawaye lokacin da taga kowa yatafi anbarta acikin mutanen da bata saniba,mutane sai zuwa ganinta akeyi amma babu Wanda yasamu nasarar ganin fuskarta saboda a lullube take. Har wurin karfe goma saura mutane basu daina shigowa ba sai gajiya su anty Fauziyya sukayi sukace arakata masaukinta ta kwanta ta huta, yaya asabe ce takama hannunta suka fita tarakata dakin dake soro wato dakinsu fahad su maryama kuma suka biyosu da akwatin kayanta da food flasks din abinci guda biyu, zame mayafin kanta tayi bayan sun gaggama ficewa tafara bin dakin da kallo, babu wani tarkace dayawa aciki sannan dakin baida girma caan dan madaidaicine mai dauke da babbar katifa anshifideta da sabod bed sheet sai akwati babba guda daya amma dakin fes yake yasha sabon fenti da jan carpet malale aciki ga kofar toilet nan komai dai neat, bata ko taba Food flasks din da aka kawoba taci gaba da zamanta shiru har goma da wani abu sai lokacin taji gidan ya danyi shiru alamar mutane sun ragu, sha daya saura yan mintuna taji alamun bude kofa gyara mayafinta tayi ta lullube jikinta,fahad ne yashigo rikeda leda,yana sanye da danyen boyel kalar ruwan siminti kanshi babu hula, sallamar da yayi kawai ta amsa daga nan ta guntse bakinta, agefen katifar ya zauna yana zaro wayarshi daga aljihu,
"Hajjaju yagajiya?"
"Alhamdulillah"
Bai kara magana ba yamaida hankalinsa kan wayar hannunshi, ita dai tana zaune ta jingina da pillow sai karkada kafa take kamar wata sarauniya, sunfi minti biyar ahaka babu wanda yasake cewa uffan sai karar fanka da ta cika dakin, ledar da yashigo da ita yamika mata gabanta ya ajiye,
"Ki ci abinci gashi nan..."
Batayi magana ba ta dauke kai,
"Kinji...."
"Naji..."
Tabaya ya kwanta rigingine yana kallon sama yana danna wayarshi zuwa can yadago ya kalleta,
"Bazaki ci abincin ba ne? To kitashi kiyi wanka ki kwanta"
Shiru tayi batayi magana ba yayinda shikuma yatashi zaune ya buda ledar dake ajiye agabanta yadauko malt guda daya ya balle ya dan sha sannan ya ajiye, Flaks din da ke ajiye ya bubbude, sakwara ce da miyar ganye tasha kaji gashi ta soyu, dama yunwa yakeji dan shima rabonshi da abinci tun yaushe mikewa yayi yashiga bathroom ya daurayo hannunshi yadawo yaja abincin gabanshi yafara ci tana zaune tana kallonshi dama guda ukuce sakwarar babu bata lokaci yatashi da guda biyu, kallonshi tayi adage,
"Malam jimana...."
Dagowa yayi ya kalleta,
"Ai abincin nawane ba naka ba so zaifi kyau idan kabar min kayana haka"
Tsame hannunshi yayi daga cikin miyar yamayar da murfin ya rurrufe sannan yajanyo ledar gabanta yabude, gasasshiyar kaza ce mai romo sai kayan sanyaya makoshi malt guda biyu da fresh milk zindimemiyar roba, kazar yabude yasoma yaga yana ci yana korawa da malt,
Harararshi tayi ta janyo flask din gabanshi tana turo baki budewa tayi itama tafara ci tana kallonshi yanata cin kazarshi,
"Gaskiya wannan yaron akwai mugun ci....tab"
Sai da yaci rabin kazar sannan yamike yashiga bathroom, wanka yazarce dayi shiyasa yajima aciki, tana cin abincin tana sake jinjina kuruciyarsa to inbanda kuruciya menene na zama yacinye kazar da ita yasiyowa?
Itama da kazar ta dora bayan ta cinye sakwarar amma bata ci da yawaba domin cinya kadai taci da dan abinda ba arasa ba saboda tarihi ko nan gaba zata tuna da taci kazar aurenta. Tana kammalawa yana fitowa daga wankan da kayanshi ajikinshi gaban akwatin kayanshi yatsaya yabude yaciro riga da wando roba kamar sport wear yakoma bathroom din yasaka sannan yafito tana zaune inda take yazo ya kwanta saitin kafafunta bayan yaja pillow daya, babu jimawa yayi baccinshi,saida taga yayi bacci sannan ta mike tashiga bathroom ita a ka'idarta idan tana period indai zatayi fitsari to saita canja pad, shiyasa saida ta dauki pad acikin handbag dinta sannan tashiga toilet, jikinta kawai tagyara amma batayi wanka ba ta canja pad tafito, akwatin kayanta tabude wai kozata samu kayan da zata saka tayi bacci dasu amma abin haushi duk night wears din bazata iya sakawa ba domin duk marassa nauyine kuma asha shagarai tasan da biyu su meenah suka yimata haka gashi ita bata iya kwana da kaya ajikinta ba, daga karshe dai sai hakura tayi tamaida akwatin tarufe, juyawa tayi ta kalleshi yawani baje yana baccinsa cikin kwanciyar hankali ga sanyin fanka yana fifitashi, bra din jikinta ta cire tabar kayan dake jikinta taje gefen katifar ta zauna ta kishingida, wayarta taciro ta duba misalin karfe daya nadare agogon wayar ya nuna mata, kashe wayar tayi tai addu'a ta shafa sannan tamaida kanta kan pillow dayake itama amutukar gajiye take bata wani jimaba bacci yace muje zuwa......
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO*
*KAMAR DA WASA...!*
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
*18*
Bilkisu tana can gabanta sai faduwa yake wanda bata san dalili ba sai dai tana danganta hakan da wannan auren da za adaura mata shi yau gashi kuma ayau din za akaita gidansu fahad domin yau ammah ke gudanar da yininta shiyasa su maama sun kammala kintsa mata kayanta gaba daya hatta wanda zata tafi dasu gidansu fahad an shirya mata cikin daya daga akwatinta na lefe. Ana idar da sallar juma'a aka daura auren fahad da bilkisu akan sadaki naira dubu talatin,bayan an gama daurin auren sun daddauki hotuna suka dawo, direct gidansu bilkisu suka wuce lokacin tasake wanka tashirya cikin leshi riga da skirt,tun kafin tafito su meenah suka rigata sukaje sunata hotuna da ango da abokansa,ita kam adole tafita itada khulsum bayan angama yimata kwalliya,
Kasa kasa take kallonshi tana son taga koda gaskene yayi kyau din kamar yadda taji su hindu nata zuzutawa, babu laifi kam yafito sosai,shima anasa bangaren tunda ya hangota hankalinsa yayi kaura daga gareshi yakoma kanta saboda ta hadu iya haduwa shiyasa har dana sanin kwaso abokansa suzo ganinta yayi, wani kishine ke lullube zuciyarsa sama sama duk abinda yakeyi idonshi na kanta, saida suka gama yin hotuna da mutane sannan yamatso wurinta nan fa kowa yarude da daukarsu awaya, ita haushima abin yake bata,
"Barka da yau Hajjaju...,ya fama da jama'a?"
"Alhamdulillah"
Shine abinda tafada kawai suka cigaba da hotuna, ana gamawa bilkisu takoma gida, angwaye dai daga can wurin walima suka wuce wadda zasu gabatar afilin makaranta. Bayan su Abba sun dawo kiran bilkisu yayi domin abata sadakinta sannan yakara yimata Nasiha shida waliyyinta, duk saida tabi ta bata kwalliyar fuskarta da hawaye da kuka shiyasa tun daga lokacin ba akara samun kanta ba har dare lokacin da za arakata domin fada ne na iyaye daga wannan yagama sai wannan yazo yayi nasa, ya mudan shima harda zuwa yayi mata nasihar azauna lafiya sannan yabawa maama dubu goma yace abata Allah yasanya alkhairi, tun bayan magriba su khulsum ke binta tatashi tashirya amma taki tashi saida aka fadowa ammah ai iyallo naji tazo tahau fada babu shiri tatashi tashiga bathroom tayi wanka tafito, abinci kam rabonta dashi tun jiya da rana, kayan da zata saka sai faman jikeshi da turare su meenah keyi kamshin har hawa mata kai taji yanayi, hatta pant din da zata saka gani tayi maama na shafeshi da almiski, tabe baki tayi tazauna gefen gado ta bude drewar din gadonta ta dauko pad ta warce pant din a hannun maama azuciyarta tana cewa,
"Yara kwayi kwa gama"
Bra din da zata saka ma itama saida suka tsuma ta da turare daga nan kuma suka dawo kanta itama zasu shafeta da madarar turare, tana ki tana komai saida suka shafa mata sannan tasaka kayanta tanemi wuri ta zauna duk da tanaji ana cewa tafito amma taki koda motsi saida su hajjaye suka zo suka fito da ita, saida aka kaita wurin ammah da abba tayi musu sallama sannan aka fita da ita inda motoci ke jira, kawarta khulsum ce agaba sai su iyallo da suka sakata atsakiya ba awuce dasu ko inaba sai gidansu fahad inda dangi sukayi dafifi suna jiran zuwansu, dakin ayiyah aka kaita tana lullube cikin babban mayafi, saida aka gama yan gaishe gaishe da taya juna murna sannan aka damka amanarta a hannun su ayiyah daga nan yan kawo amarya suka tafi bayan su maama sun shigo mata da akwatinta.
Duk dauriyarta saida tayi hawaye lokacin da taga kowa yatafi anbarta acikin mutanen da bata saniba,mutane sai zuwa ganinta akeyi amma babu Wanda yasamu nasarar ganin fuskarta saboda a lullube take. Har wurin karfe goma saura mutane basu daina shigowa ba sai gajiya su anty Fauziyya sukayi sukace arakata masaukinta ta kwanta ta huta, yaya asabe ce takama hannunta suka fita tarakata dakin dake soro wato dakinsu fahad su maryama kuma suka biyosu da akwatin kayanta da food flasks din abinci guda biyu, zame mayafin kanta tayi bayan sun gaggama ficewa tafara bin dakin da kallo, babu wani tarkace dayawa aciki sannan dakin baida girma caan dan madaidaicine mai dauke da babbar katifa anshifideta da sabod bed sheet sai akwati babba guda daya amma dakin fes yake yasha sabon fenti da jan carpet malale aciki ga kofar toilet nan komai dai neat, bata ko taba Food flasks din da aka kawoba taci gaba da zamanta shiru har goma da wani abu sai lokacin taji gidan ya danyi shiru alamar mutane sun ragu, sha daya saura yan mintuna taji alamun bude kofa gyara mayafinta tayi ta lullube jikinta,fahad ne yashigo rikeda leda,yana sanye da danyen boyel kalar ruwan siminti kanshi babu hula, sallamar da yayi kawai ta amsa daga nan ta guntse bakinta, agefen katifar ya zauna yana zaro wayarshi daga aljihu,
"Hajjaju yagajiya?"
"Alhamdulillah"
Bai kara magana ba yamaida hankalinsa kan wayar hannunshi, ita dai tana zaune ta jingina da pillow sai karkada kafa take kamar wata sarauniya, sunfi minti biyar ahaka babu wanda yasake cewa uffan sai karar fanka da ta cika dakin, ledar da yashigo da ita yamika mata gabanta ya ajiye,
"Ki ci abinci gashi nan..."
Batayi magana ba ta dauke kai,
"Kinji...."
"Naji..."
Tabaya ya kwanta rigingine yana kallon sama yana danna wayarshi zuwa can yadago ya kalleta,
"Bazaki ci abincin ba ne? To kitashi kiyi wanka ki kwanta"
Shiru tayi batayi magana ba yayinda shikuma yatashi zaune ya buda ledar dake ajiye agabanta yadauko malt guda daya ya balle ya dan sha sannan ya ajiye, Flaks din da ke ajiye ya bubbude, sakwara ce da miyar ganye tasha kaji gashi ta soyu, dama yunwa yakeji dan shima rabonshi da abinci tun yaushe mikewa yayi yashiga bathroom ya daurayo hannunshi yadawo yaja abincin gabanshi yafara ci tana zaune tana kallonshi dama guda ukuce sakwarar babu bata lokaci yatashi da guda biyu, kallonshi tayi adage,
"Malam jimana...."
Dagowa yayi ya kalleta,
"Ai abincin nawane ba naka ba so zaifi kyau idan kabar min kayana haka"
Tsame hannunshi yayi daga cikin miyar yamayar da murfin ya rurrufe sannan yajanyo ledar gabanta yabude, gasasshiyar kaza ce mai romo sai kayan sanyaya makoshi malt guda biyu da fresh milk zindimemiyar roba, kazar yabude yasoma yaga yana ci yana korawa da malt,
Harararshi tayi ta janyo flask din gabanshi tana turo baki budewa tayi itama tafara ci tana kallonshi yanata cin kazarshi,
"Gaskiya wannan yaron akwai mugun ci....tab"
Sai da yaci rabin kazar sannan yamike yashiga bathroom, wanka yazarce dayi shiyasa yajima aciki, tana cin abincin tana sake jinjina kuruciyarsa to inbanda kuruciya menene na zama yacinye kazar da ita yasiyowa?
Itama da kazar ta dora bayan ta cinye sakwarar amma bata ci da yawaba domin cinya kadai taci da dan abinda ba arasa ba saboda tarihi ko nan gaba zata tuna da taci kazar aurenta. Tana kammalawa yana fitowa daga wankan da kayanshi ajikinshi gaban akwatin kayanshi yatsaya yabude yaciro riga da wando roba kamar sport wear yakoma bathroom din yasaka sannan yafito tana zaune inda take yazo ya kwanta saitin kafafunta bayan yaja pillow daya, babu jimawa yayi baccinshi,saida taga yayi bacci sannan ta mike tashiga bathroom ita a ka'idarta idan tana period indai zatayi fitsari to saita canja pad, shiyasa saida ta dauki pad acikin handbag dinta sannan tashiga toilet, jikinta kawai tagyara amma batayi wanka ba ta canja pad tafito, akwatin kayanta tabude wai kozata samu kayan da zata saka tayi bacci dasu amma abin haushi duk night wears din bazata iya sakawa ba domin duk marassa nauyine kuma asha shagarai tasan da biyu su meenah suka yimata haka gashi ita bata iya kwana da kaya ajikinta ba, daga karshe dai sai hakura tayi tamaida akwatin tarufe, juyawa tayi ta kalleshi yawani baje yana baccinsa cikin kwanciyar hankali ga sanyin fanka yana fifitashi, bra din jikinta ta cire tabar kayan dake jikinta taje gefen katifar ta zauna ta kishingida, wayarta taciro ta duba misalin karfe daya nadare agogon wayar ya nuna mata, kashe wayar tayi tai addu'a ta shafa sannan tamaida kanta kan pillow dayake itama amutukar gajiye take bata wani jimaba bacci yace muje zuwa......
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO*
*KAMAR DA WASA...!*
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
*18*