← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 62 OF 67

Sashe 62

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Tashi yayi yaje ya tsiyayo ruwan zafi a flask yazo yazauna gefenta yazame hular kanta nan gashinta dake jike ya bazu tasa hannu ta sake maidashi baya, rigar tata ya dan ja zuwa sama nan santala santalan laps dinta suka bayyana sai shining suke, tun daga kan kafarta yake gasa mata har zuwa cinyarta babu karya kuwa taji dadi mutuka domin ciwon yaragu da kaso mai yawa, lokacin da yagama harta dan fara gyangyadi, tashi yayi yaje ya ajiye komai da yadauko sannan yadawo, shammatarta yayi kawai taji ya cakumo kirjinta tashi tayi cikeda masifa yayi saurin guduwa yana cewa, "Ai ba ayin aikin banza a kano nima na karbi ladan aikina..."

Batayi magana ba tajuya ta gyara kwanciyarta taja bargo, saida ya tabbatar da tayi bacci sannan yakoma kan gadon ya kwanta kusa da ita yana wasa da gashin kanta. Husnah kam yau acike take famm da fahad saboda bai taba yin hakaba gaba daya yau sun wani kule adaki shida Bilkisu sunki fitowa, to me suke nufi? Kitchen tashiga ta dafa farar taliya sannan tayi sos din kwai tafito duk ranta ajagule, zama tayi afalo taci abincin ta ganin har tagama bai fitoba yasata sadadawa taje ta dan labe amma tsitt kamar babu kowa acikin dakin, komawa falo tayi taci gaba da zama har magriba tayi sannan ta tashi taje tayi salla tasake fitowa lokacin suma su bilkisu sun tashi, tana kwance kan rug din salla da carbi ahannunta fahad na kusa da ita yana yimata maganar abinci, labewa husnah tayi tana saurarensu,

"Hajjaju me zakici to idan bazaki ci wannan fanken ba?"

Saida taja wasu sakwanni sannan tayi magana ahankali,

"Ni babu abinda zanci..."

"No, zakici wani abu gaskiya, zaki ci indomie?"

Daga masa kai tayi yatashi yafita, yana fita yaga husnah wacce babu zato taga yabude kofa yafito,

"Uhmmm ya fahad dama zuwa nayi in tasheku naga baku fitoba shine nace may be baku san lokacin salla yayiba....."

Fuskarsa babu yabo babu fallasa yace,

"Mun tashi, zo muje ki dafa min indomie...."

Hade rai tayi tajuya tana kunkuni,

"Tabdijam... Nice ma zan dafawa matarka abinci? Impossible wallahi bazai yuyu ba"

Jin abinda tafada yabashi mamaki,

"Husnah nikike fadawa haka ko? Wato bazan saki abu kiyi ba?"

"To ai naga bakai zaka ciba.... Matarka zaka kaiwa fa"

"To matar tawa ita kika yiwa bani kika yiwa ba? Zaki wuce muje kitchen ko sai nayi miki rashin mutunci"

Turje turje tafara yi tana buga kafa akasa ganin haka yasashi wucewa cikin kitchen din batare da yasake bi ta kanta ba, da kansa yadafa musu manyan indomie guda uku sannan yasoya kwai yajuye yanufi dakin Bilkisu tana kwance har lokacin tana tasbihi,

"Tashi kici abincin hajjaju..."

Yunkurawa tayi ta tashi ta dauki fork ta debo takai bakinta tafara taunawa kenan taji yace,

"Kanwarki ce ta dafa mik...."

Ai bai karasa ba yaga ta tsaya da taunar da takeyi ta kafeshi da ido,

"Wasa nake yimiki wallahi ni na dafa... Kin san dai ai wani time din ina girki a kd"

Jin ya rantse yasa ta cigaba da ci tana kunkuni,

"Ni kar ka kara saka wannan nonsense wife din naka cikin sha'anina..... Ban son raini..."

Murmushi kawai yayi yana kallonta gaskiya Bilkisu tana da bala'in son girma,

"Daina zagar min mata..."

Yi tayi kamar bata jishiba, fork yadauka shima suka cigaba da cin abincin tare, bayan sun gama ta hada tea tasha, shikam yana nan nane adakin kamar cingum har sukayi sallar ishah, sai bayan da yayi shirin bacci sannan yafita zuwa dakin husnah tana kwance cikin kayan bacci tana waya da Ruky tana bata labarin abinda yafaru wai har ita fahad zai ce ta dafawa wannan tsohuwar wife din tashi abinci? Ita kuwa tace bazata dafaba, zugata Ruky taci gaba dayi tana cemata wallahi karta yarda idan bahaka ba rainata zasuyi kuma bilkisu gani zatayi kamar yafi sonta, tana jin fahad ta katse wayar ta gimtse fuska, kallonta yayi shima fuskar tashi gimtse,

"Asma'u har ni zance kiyi min abu ki k'i yi ko? Dama kin rainani har haka ban saniba? Good nagode ba laifinki bane nawa ne...."

"Haba ya fahad kayi hakuri pls... Ni wallahi da kaine zakaci zan dafa maka..."

"To ke waye yace miki ita zataci...?" Wannan tambayarce ta so kada mata hanjin cikinta shiyasa takasa bashi amsa tayi shiru,

"Babu damuwa nagode, saida safe"

Juyawa yayi yafita tabi bayanshi da harara,daga shi har bilkisun haushinsu takeji. A falo fahad ya zauna ya kirasu mukhtar yana tambayarsu ya school sukace normal ne kawai yaci gaba da hutawarsa, dariya yayi sukayi sallama dashi ya wuce dakin Bilkisu bayan yaje ya rufe ko ina na gidan, kwance ya isketa cikin riga da wando na bacci masu dan kauri amma abubuwan dake tsokale masa ido gasu nan abayanne,dariya yaso yi saboda ganin ta jera pillow a tsakaninsu,

"Dan sammin kadan intaba dan Allah Bilkisu..."

Juya masa baya tayi nan tajishi yana dariya kasa kasa yana cewa,

"Yarinya jiya tasha....."

Juyawa tayi ta harare shi duk yawani bi ya hasketa da hasken dake wayarshi,

"Kafa dameni... Bacci nake ji"

Kashe hasken taga yayi,nan tagyara kwanciyarta tana mamakin shi wai ita yake kira da yarinya lallai yaga gadon baccinta dole yakirata da haka. Duk yadda taso kar yarab'u jikinta saida ya kwakumeta cikin dare dole ahaka sukayi bacci. Washe garima haka suka wuni cur adaki saida yamma tafita tashiga kitchen ta girka tuwon semo miyar kuka, aranar yabar dakinta yakoma dakin husnah duk haushinsa husnah keji saboda ganinta ya raina mata hankali yazo sai wani bacci yaketa faman yimata. Bilkisu dai saida tayi kwana biyar bataje aiki ba har saida taji ta garau, fahad shima bai koma makaranta ba acewarsa sai wani satin har lokacin bai sake attempting na kusantar ta ba amma sai dai tana shan dakuma haka zaiyita fakarta yana taba mata kirji gata ita kuma ba gwanar saka bra ba wani lokacin ko fita zatayi bata son tasaka amma yanzu tasan fahad bazai bariba dan ko jiya da tafito zata fita aiki yana falo kallo daya yayiwa gurin yagane bata saka ba janta daki yayi sakamakon husnah na wurin,

"Baki saka bra ba why?"

Musawa tayi tana ta turo baki, hannu yakai ta rike tana harararsa,

"Kibari naji mana tunda kince kin saka...."

Tureshi tayi tawuce gaban wardrobe ta dauko tawuce bathroom fita yayi yana dariya, lokacin da taje office khulsum tsokanarta tarinka yi tana cewa amarya take gashi nan har tafara wani shining gaskiya ko ita ta fahimci hakan amma tazaci ko Shea butter din da tafara shafawa ne na cikin lefenta. Ana gobe fahad zai koma kd adakinta yake shiyasa ranar ma yayi mata wayo saida yabarta tafara bacci sannan yaje ya far mata sosai yauma yaci galaba domin saida yafara rudata ya kasheta da soyayya sannan yayi abinda yayi niyyar yi, ranar ma sunsha kuka shikuma yasha yakushi da cizo amma bai hakuraba saida yayi abinda yaso shiyasa lokacin da yabarta bata da karfi ko na sisin kwabo, bai ma yarda yayi wanka adakinba dakin husnah yagudu can yaje yayi wanka yayi alwala yafito haushi da bakin ciki kamar zasu kashe husnah ganin yazo yayi wanka anan dan ko magana ma kin yimasa tayi. Saida karfe 6 tayi sannan yakoma dakin Bilkisu tana kwance har lokacin idanuwanta sunyi fici fici saboda kuka dan jiyama sosai ta dandana kudarta fahad fa babu damane a wannan fagen domin akwai rike wuta gashi ta fahimci irin mazan nanne masu dogon zango baya samun nutsuwa cikin karamin lokaci shiyasa take shan wuya a hannunshi, sunkuyawa yayi agabanta yadafa hannayenshi akan gadon yana kallonta,bige hannayen nashi tayi nan yafado mata, kallonta yayi yana murmushin rashin kunya,

"Kina bukatar kari ne?"

Harara ta watsa masa sannan ta yunkura dakyar ta tashi aranta tana tunanin wai meyasa yake yimata wayo ne har haka? Ita ina nata wayon yake tafiyane?

Bata kara bi takanshi ba tawuce toilet yauma saida ta dage wurin gasa jikinta sannan taji dadi sai kunkuni taketa yimasa tana kiransa da mugu, shikuma ga rashin zuciya da zarar yaga wuri sai yayi tsokana aranar da yamma ya tattara yayi tafiyarsa kd kuma yace sai yajima basu ganshi ba, aranar da yatafi da daddare ita yafara kira awaya kafin husnah duk Bilkisu bata son hirar nan tashi saboda mafi yawanta baran baramace da rashin kunya aciki daga karshe cemata yayi wai dan Allah tacire kayan baccinta suyi video call, kawai mamaki fahad ke bata bata taba sanin dan air ne shi mai lasisi ba sai a yan kwanakin nan dan wata maganar ma idan yafada ita da ba itace tafada ba kunyace take hanata motsi, harda fushi yayi saboda taki yarda suyi video call bayan sunyi sallama tafita kitchen dafa Lipton da lemon grass taji husnah tafito falo tana waya da fahad wai dan Bilkisu taji saboda dama taji motsin fitowarta, dariya bilkisu ita abinma yabata wato ita husnah bata san kwantai ma tasamuba na hirar tunda saida yafara kiranta suka debe awa da awanni yana yimata magana shine ita dan ankirata yanzu harda su zuwa tura haushi? Bata kulata ba tawucewarta daki.
Chapter 62 · 0% Book details