Sashe 48
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Malam idan kagama karufe min kofar bayan kafita", ganin dagaske fitar zatayi tabar masa dakin yasashi ajiye wayar yamike dasauri yasha gabanta,
"Wai me kike nufine? Karfi da yaji nema kikeyi ki goga min kashin kaji ko bakin fenti...."
"Allah ko?"
Matsarta yayi yana kallonta fuskarta gaba daya babu annuri,
"Wai ke mai kike nufi? Dan kawai kinji mace ta dauki wayata? Waima ina ruwanki ne, budurwata ce wadda zan aura sunanta Dr murja medical Dr ce a asibitinmu she's 35 years old, ita kuma wannan husnah ce itama budurwata ce nurse ce yanzu haka tana yin bsc nursing dinta a BUK she's 22 years old nanda yan watanni zan aureta,sai me kuma kike son ji....?"
Ita kanta a lokacin nan tasan bata cikin nutsuwarta bata san dalili ba, cikin fushi da bacin rai tace,
"To kasan kana da duk wadannan meye naka na damuwa da lallai saika aureni? Ai da sai kaje kazauna dasu..."
Murmushin rainin hankali yayi mata yana jan dan gemunshi na rashin kunya,
"Waye yadamu saiya aureki? Ni? Lallai... .."
Afirgice ta kalleshi cikeda mamaki, idanuwansu ne suka sarke da juna cikin fada tace,
"To ai ba adole.... Kana iya sawwake min kowa sai yahuta tunda bakaine ka damu da aurenba"
"Hmmm Bilkisu kenan....!"
Haushine da mamaki suka sake kamata har ta daga kai ta kalleshi akaro na biyu, har lokacin yana wasa da gemunsa,
"Da kike cewa in sawwake miki da nine na aureki? Ai bani na aureki ba ina zaman zamana aka ce an aura min ke, tunda bakida ra'ayi kamar yadda nima banida interest akai kina iya zuwa kisamu wadanda suka daura kisasu su warwareshi....." Yakarasa maganar yana daga kafada,
"Ni kake fadawa haka?"
"Yes ai gaskiya nafada miki ni ban nemi aurenki ba sadaka aka aura min saboda ance wannan tsohon dan duniyar yaudararki yayi daga karshe ya sakeki..."
Kwallace taciko mata ido takai hannu zata dakeshi yarike yana yimata murmushi mai kona zuciya,
"Fahad sakeni... Ka sakeni.....ko ana aure dole ne?"
"Oho ni nasani ne? Nima ai dolen aka yimin tunda inada wadanda nakeso aka tashi aka bani matar sadaka"
Wannan Kalmar ba karamin kona mata rai tayiba dan har saida tanemi sliver abakinta tarasa saboda dimuwa wai ita yakirada matar sadaka, shikuwa gegewa yayi ta gefenta yadauki wayarshi yafice nan ta durkushe tasoma kuka, tunda tazo duniya bata taba jin bacin rai irin nayau ba, tamkar zata mutu haka takeji, kwana tayi tana kuka wannan dalilinne yasa dasafe ta tashi da matsanancin zazzabi da ciwon kai sai kakkarwar sanyi take yi ga wani irin lafiyayyen ciwon kai asibiti ammah tasata agaba suka tafi suna zuwa akace jininta ne yayi kasa bama hawaba kasa yayi nan aka bata gado sai rawar jiki takeyi idabuwanta faful da hawaye duk sun kumbura.....
*_Ummi Shatu_*
*me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
45***Taimakon gaggawa aka fara neman bata domin inbanda kadawa babu abinda jikinta keyi kamar wacce ke tsakiyar kankara, bayan kamar wasu mintuna wadanda bazasu gaza 30 ba nurses din suka zo wurin ammah suna yimata bayanin yakamata fa suje su samo jini saboda su basuda shi anan, duk da ammah bataso ta sanarwa su Hindu to amma babu yadda za a yi dole sai sun sani, wannan gayawa wannan da haka duk zancen ya yadu a junansu babu bata lokaci duk suka yiwa asibitin tsinke,text maama ta turawa fahad amma kasancewar yana cikin lab yana aiki bai ganiba.
Tun abinda yafaru jiya tsakaninsa da Bilkisu da zarar yatuna sai yayi murmushi ita daukar kanta takeyi watta babba bayan shikuma awurinshi mararbarta da jaririya kadanne gaba daya yagama rainata sanine bata gama yiba, dayake yau juma'a manyan kaya yasaka saboda ta can zai wuce masallaci, duk da cewar karshen makone hakan bai hanasu samun ayyuka da yawa ba shiyasa bashi yasamu kansa ba saida lokacin sallar juma'a yayi. Har saida yafito daga salla sannan yaga text din maama tana sanar dashi Bilkisu babu lafiya sannan ana bukatar jini, harda kwatanccen asibitin da take kwance, batare da yakoma asibiti ba yawuce inda maama tafada masa an kwantar da Bilkisu, wani dan karamin asibitin kudine dake nan unguwar tasu sai dai da dan tazara tsakaninsu da gidansu, a reception yaga meenah wacce taje kiran wata nurse wadda zata auna jinin mijinta aga ko zaiyi daidai da na Bilkisu,
"Ya fahad sannu da zuwa..."
"Yawwa meenah, ya mai jikin?"
"Dasauki tana ciki muje"
Tare suka karasa wurinsu ammah wadanda ke tsaye akofar dakin da Bilkisu take harda mijin meenah ganin fahad yasa amma gyara lullubinta suna gaisawa kuma tawuce tabar wurin, shi dinma hakan yafi sakewa shiyasa yasamu damar cemusu abar jinin mijin meenah shi sai adebi nasa dan baya ko tantama nashi zaiyi mata saboda shi jininsa irin wanda zai iya bawa kowa ne, tare suka tafi lab da nurse akayi komai da yakamata aka debi jininsa leda daya da rabi bai samu tashi ba awannan lokacin ya dan kwanta sai bayan kamar mintuna ishirin sannan yatashi yana dai dan jin jikinsa babu karfi but babu wani jiri ko hajijiya, wurinsu Hindu yakoma dama sunata zuwa suna lekashi suna komawa, suna zaune su uku daga Hindu sai maama sai meenah ammah tatafi gida da yan jikokinta haka shima mijin meenah yatafi, sannu suke tayi masa yana amsawa shi idanma banda yar yunwar da yakeji ai da zai dan jima a asibitin,
"Tafarka ne?" Ya tambaya yana kallon kofar dakin da Bilkisu ke ciki,
"Ehh amma yanzun dai gaskiya bacci takeyi...amma ai zaka iya shiga"
Juyawa yayi yashiga, tana kwance tayi fayau da ita ana kara mata jinin wanda har guda dayan yakusa karewa, jingina yayi ajikin bango ya harde hannuwanshi akirjinshi yana kallonta, hijabi ne ajikinta saboda sanyi sai doguwar riga ta atamfa, fuskarta ya kalla yaga ta wani bata fuska kamar irin idonta biyun nan ba bacci takeyiba, murmushi yasaki mai kayatarwa sannan ahankali yafurta,
"Hajjaju ana fada da jinina kenan......"
Ahankali yakarasa gaban gadon duk fuskarta akode amma idanuwanta luhu luhu akumbure ga bakinta ya bushe sosai irin yadda yake yi dinnan idan mutum yana cikin halin jinya,
"Am very sorry soul mate... Nasaki kuka ko? Am sorry kiyafe min...."
Kamar tana jinsa yaga tasake bata rai harda dan turo baki,
"Are we fighting?" Yafada yana murmushi, bakin da ta dan turo yakai nashi kai ya tsotsa sannan yadago yana murmushi,
"Ai nace miki am sorry.... Stop fighting with my blood Mana baby.... I said am very sorry about what i did... Pls forgive me kinji.... Ki yafewa dan kaninki...!"
Goshinta yayiwa light kiss sannan yasake yiwa lips dinta wadanda ada suke abushe amma tun lokacin da ya tsotsesu suka dawo kamar anshafa musu lipstick, sakin hannunta yayi wanda da yakama yana murzawa cikin nashi saboda tsabar taushinsa,
"Tunda kin ki hakura am going, anjima zan dawo kinji...."
A kumatu yasake bata wani kiss din sannan yatashi yana kallonta murmushi yasake yi saboda yadda taketa hade rai tana motsa baki kamar mai yin fada alhali kuma bacci ma takeyi yasan abinda ke zuciyarta ne taketa amayoshi lokacin baccinta. Da baya da baya yake tafiya yana murmushi har lokacin idanuwanshi na kan fuskarta, saida yazo daf da bakin kofa sannan yayiwa tafin hannunshi kiss ya hura mata, ganin yana kokarin juyowa yasa su maama dake leke ta glass din kofa saurin guduwa kowaccensu kunshe da bakinta dan kar yaji, bude kofar yayi yafita yana kallon su maama wadanda ke tsaye cirko cirko kamar marassa gaskiya,
"Maman hudah lafiya dai ko?"
"Lafiya lau ya fahad, mun dan fita ne dawowarmu kenan..."
Dan bata fuska yayi sannan yace,
"Ku da kuke da patient ina kuma zakuje dan Allah?"
"Ahhh ya fahad bafa nisa mukayi ba..." Inji Hindu,
"Nidai dan Allah ga amanata nan zanje gida idan huta anjima zan dawo, pls and pls ku kular min da ita... Idan tana bukatar wani abu akirani.. " yakarashe maganar yana kallon maama wacce ke dariya,
"Insha Allah zamu kula da ita kamar kana wurin..." Inji meenah,
"Yawaa nagode, bari naje..."
Juyawa yayi yatafi suna sake yimasa sannu, shi sai yanzu yafara jin dan ciwon kai kadan kadan da dan jiri jiri yasan bawai dan andebi jinin bane may be saboda ciwon dake tare dashi ne, tunda yabar wurin su meenah ke gulmar abinda suka gani,
"Ya fahad dinnan kamar wani salihi ashe shima number 1 ne..." Hindu tafada tana dariya,
"Ai kibari kawai adda labour fa tahuta amma takasa ganewa.." Mamaa tabata amsa,
"Gentle dashi wallahi..." Inji meenah, hirar dai suka bata lokaci sunayi kasan idan kaga mai son wanda ya shafeka kaima sonshi kakeyi watakila dalilin kenan da yasa suke kaunar fahad.
Daurewa yayi yakai kanshi gida duk da jirin da yakeji, yana shiga yawuce ciki baiko kalli dakinsu ba dake soro,
Falon ayiyah yashiga yawuceta zaune gaban murhu tana karasa daka kuli kulin da zata yiwa baba kwadon zogale wanda idan yadawo daga masallaci zai ci, ita kuma mamuh tafita zuwa gidansu salim,
Anan tsakar falon ya kwanta yayi pillow da damtsen hannunshi, ahaka yaji motsin shigowarsu mariya daga makaranta,
"Sai yanzu kuke dawowa daga makaranta ko? Kun tsaya wasa ahanya ko?"
"Allah ya fahad sai yanzu muka samu napep..." Maryam tafada tana cire sandal din dake kafarta,
"Bari natashi nakamaku zama ku fadi gaskiya..."
Sun fara rantse rantse kenan ayiyah tashigo dauke da kwanukan zogalen da ta dafa,
"Kai da naga kamarma bakada lafiya amma shine zakazo kafada yara da fada ko fahad?"
Murmushi yayi sannan yatashi zaune,
"Ayiyah lafiyata kalau fa kawai dai jinina aka dan diba..."
"Jini? Meya faru?" Ayiyah tafada tana mikewa tsaye daga durkushen da tayi tana ajiye kwanuka,
"Babu komaifa... Bata da lafiya ne wai kuma ana bukatar jini shine aka debi nawa"
Yana fadar haka ayiyah tagane Bilkisu yake nufi,
"To Allah ya sawwake yabata lafiya.... A asibiti take kenan?"
"Ehhhh, ayiyah taimaka kibani zogalen nima inci..."
"Allah ya sawwake, gashi ai dama babanku na dafawa..."
"Wai me kike nufine? Karfi da yaji nema kikeyi ki goga min kashin kaji ko bakin fenti...."
"Allah ko?"
Matsarta yayi yana kallonta fuskarta gaba daya babu annuri,
"Wai ke mai kike nufi? Dan kawai kinji mace ta dauki wayata? Waima ina ruwanki ne, budurwata ce wadda zan aura sunanta Dr murja medical Dr ce a asibitinmu she's 35 years old, ita kuma wannan husnah ce itama budurwata ce nurse ce yanzu haka tana yin bsc nursing dinta a BUK she's 22 years old nanda yan watanni zan aureta,sai me kuma kike son ji....?"
Ita kanta a lokacin nan tasan bata cikin nutsuwarta bata san dalili ba, cikin fushi da bacin rai tace,
"To kasan kana da duk wadannan meye naka na damuwa da lallai saika aureni? Ai da sai kaje kazauna dasu..."
Murmushin rainin hankali yayi mata yana jan dan gemunshi na rashin kunya,
"Waye yadamu saiya aureki? Ni? Lallai... .."
Afirgice ta kalleshi cikeda mamaki, idanuwansu ne suka sarke da juna cikin fada tace,
"To ai ba adole.... Kana iya sawwake min kowa sai yahuta tunda bakaine ka damu da aurenba"
"Hmmm Bilkisu kenan....!"
Haushine da mamaki suka sake kamata har ta daga kai ta kalleshi akaro na biyu, har lokacin yana wasa da gemunsa,
"Da kike cewa in sawwake miki da nine na aureki? Ai bani na aureki ba ina zaman zamana aka ce an aura min ke, tunda bakida ra'ayi kamar yadda nima banida interest akai kina iya zuwa kisamu wadanda suka daura kisasu su warwareshi....." Yakarasa maganar yana daga kafada,
"Ni kake fadawa haka?"
"Yes ai gaskiya nafada miki ni ban nemi aurenki ba sadaka aka aura min saboda ance wannan tsohon dan duniyar yaudararki yayi daga karshe ya sakeki..."
Kwallace taciko mata ido takai hannu zata dakeshi yarike yana yimata murmushi mai kona zuciya,
"Fahad sakeni... Ka sakeni.....ko ana aure dole ne?"
"Oho ni nasani ne? Nima ai dolen aka yimin tunda inada wadanda nakeso aka tashi aka bani matar sadaka"
Wannan Kalmar ba karamin kona mata rai tayiba dan har saida tanemi sliver abakinta tarasa saboda dimuwa wai ita yakirada matar sadaka, shikuwa gegewa yayi ta gefenta yadauki wayarshi yafice nan ta durkushe tasoma kuka, tunda tazo duniya bata taba jin bacin rai irin nayau ba, tamkar zata mutu haka takeji, kwana tayi tana kuka wannan dalilinne yasa dasafe ta tashi da matsanancin zazzabi da ciwon kai sai kakkarwar sanyi take yi ga wani irin lafiyayyen ciwon kai asibiti ammah tasata agaba suka tafi suna zuwa akace jininta ne yayi kasa bama hawaba kasa yayi nan aka bata gado sai rawar jiki takeyi idabuwanta faful da hawaye duk sun kumbura.....
*_Ummi Shatu_*
*me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
45***Taimakon gaggawa aka fara neman bata domin inbanda kadawa babu abinda jikinta keyi kamar wacce ke tsakiyar kankara, bayan kamar wasu mintuna wadanda bazasu gaza 30 ba nurses din suka zo wurin ammah suna yimata bayanin yakamata fa suje su samo jini saboda su basuda shi anan, duk da ammah bataso ta sanarwa su Hindu to amma babu yadda za a yi dole sai sun sani, wannan gayawa wannan da haka duk zancen ya yadu a junansu babu bata lokaci duk suka yiwa asibitin tsinke,text maama ta turawa fahad amma kasancewar yana cikin lab yana aiki bai ganiba.
Tun abinda yafaru jiya tsakaninsa da Bilkisu da zarar yatuna sai yayi murmushi ita daukar kanta takeyi watta babba bayan shikuma awurinshi mararbarta da jaririya kadanne gaba daya yagama rainata sanine bata gama yiba, dayake yau juma'a manyan kaya yasaka saboda ta can zai wuce masallaci, duk da cewar karshen makone hakan bai hanasu samun ayyuka da yawa ba shiyasa bashi yasamu kansa ba saida lokacin sallar juma'a yayi. Har saida yafito daga salla sannan yaga text din maama tana sanar dashi Bilkisu babu lafiya sannan ana bukatar jini, harda kwatanccen asibitin da take kwance, batare da yakoma asibiti ba yawuce inda maama tafada masa an kwantar da Bilkisu, wani dan karamin asibitin kudine dake nan unguwar tasu sai dai da dan tazara tsakaninsu da gidansu, a reception yaga meenah wacce taje kiran wata nurse wadda zata auna jinin mijinta aga ko zaiyi daidai da na Bilkisu,
"Ya fahad sannu da zuwa..."
"Yawwa meenah, ya mai jikin?"
"Dasauki tana ciki muje"
Tare suka karasa wurinsu ammah wadanda ke tsaye akofar dakin da Bilkisu take harda mijin meenah ganin fahad yasa amma gyara lullubinta suna gaisawa kuma tawuce tabar wurin, shi dinma hakan yafi sakewa shiyasa yasamu damar cemusu abar jinin mijin meenah shi sai adebi nasa dan baya ko tantama nashi zaiyi mata saboda shi jininsa irin wanda zai iya bawa kowa ne, tare suka tafi lab da nurse akayi komai da yakamata aka debi jininsa leda daya da rabi bai samu tashi ba awannan lokacin ya dan kwanta sai bayan kamar mintuna ishirin sannan yatashi yana dai dan jin jikinsa babu karfi but babu wani jiri ko hajijiya, wurinsu Hindu yakoma dama sunata zuwa suna lekashi suna komawa, suna zaune su uku daga Hindu sai maama sai meenah ammah tatafi gida da yan jikokinta haka shima mijin meenah yatafi, sannu suke tayi masa yana amsawa shi idanma banda yar yunwar da yakeji ai da zai dan jima a asibitin,
"Tafarka ne?" Ya tambaya yana kallon kofar dakin da Bilkisu ke ciki,
"Ehh amma yanzun dai gaskiya bacci takeyi...amma ai zaka iya shiga"
Juyawa yayi yashiga, tana kwance tayi fayau da ita ana kara mata jinin wanda har guda dayan yakusa karewa, jingina yayi ajikin bango ya harde hannuwanshi akirjinshi yana kallonta, hijabi ne ajikinta saboda sanyi sai doguwar riga ta atamfa, fuskarta ya kalla yaga ta wani bata fuska kamar irin idonta biyun nan ba bacci takeyiba, murmushi yasaki mai kayatarwa sannan ahankali yafurta,
"Hajjaju ana fada da jinina kenan......"
Ahankali yakarasa gaban gadon duk fuskarta akode amma idanuwanta luhu luhu akumbure ga bakinta ya bushe sosai irin yadda yake yi dinnan idan mutum yana cikin halin jinya,
"Am very sorry soul mate... Nasaki kuka ko? Am sorry kiyafe min...."
Kamar tana jinsa yaga tasake bata rai harda dan turo baki,
"Are we fighting?" Yafada yana murmushi, bakin da ta dan turo yakai nashi kai ya tsotsa sannan yadago yana murmushi,
"Ai nace miki am sorry.... Stop fighting with my blood Mana baby.... I said am very sorry about what i did... Pls forgive me kinji.... Ki yafewa dan kaninki...!"
Goshinta yayiwa light kiss sannan yasake yiwa lips dinta wadanda ada suke abushe amma tun lokacin da ya tsotsesu suka dawo kamar anshafa musu lipstick, sakin hannunta yayi wanda da yakama yana murzawa cikin nashi saboda tsabar taushinsa,
"Tunda kin ki hakura am going, anjima zan dawo kinji...."
A kumatu yasake bata wani kiss din sannan yatashi yana kallonta murmushi yasake yi saboda yadda taketa hade rai tana motsa baki kamar mai yin fada alhali kuma bacci ma takeyi yasan abinda ke zuciyarta ne taketa amayoshi lokacin baccinta. Da baya da baya yake tafiya yana murmushi har lokacin idanuwanshi na kan fuskarta, saida yazo daf da bakin kofa sannan yayiwa tafin hannunshi kiss ya hura mata, ganin yana kokarin juyowa yasa su maama dake leke ta glass din kofa saurin guduwa kowaccensu kunshe da bakinta dan kar yaji, bude kofar yayi yafita yana kallon su maama wadanda ke tsaye cirko cirko kamar marassa gaskiya,
"Maman hudah lafiya dai ko?"
"Lafiya lau ya fahad, mun dan fita ne dawowarmu kenan..."
Dan bata fuska yayi sannan yace,
"Ku da kuke da patient ina kuma zakuje dan Allah?"
"Ahhh ya fahad bafa nisa mukayi ba..." Inji Hindu,
"Nidai dan Allah ga amanata nan zanje gida idan huta anjima zan dawo, pls and pls ku kular min da ita... Idan tana bukatar wani abu akirani.. " yakarashe maganar yana kallon maama wacce ke dariya,
"Insha Allah zamu kula da ita kamar kana wurin..." Inji meenah,
"Yawaa nagode, bari naje..."
Juyawa yayi yatafi suna sake yimasa sannu, shi sai yanzu yafara jin dan ciwon kai kadan kadan da dan jiri jiri yasan bawai dan andebi jinin bane may be saboda ciwon dake tare dashi ne, tunda yabar wurin su meenah ke gulmar abinda suka gani,
"Ya fahad dinnan kamar wani salihi ashe shima number 1 ne..." Hindu tafada tana dariya,
"Ai kibari kawai adda labour fa tahuta amma takasa ganewa.." Mamaa tabata amsa,
"Gentle dashi wallahi..." Inji meenah, hirar dai suka bata lokaci sunayi kasan idan kaga mai son wanda ya shafeka kaima sonshi kakeyi watakila dalilin kenan da yasa suke kaunar fahad.
Daurewa yayi yakai kanshi gida duk da jirin da yakeji, yana shiga yawuce ciki baiko kalli dakinsu ba dake soro,
Falon ayiyah yashiga yawuceta zaune gaban murhu tana karasa daka kuli kulin da zata yiwa baba kwadon zogale wanda idan yadawo daga masallaci zai ci, ita kuma mamuh tafita zuwa gidansu salim,
Anan tsakar falon ya kwanta yayi pillow da damtsen hannunshi, ahaka yaji motsin shigowarsu mariya daga makaranta,
"Sai yanzu kuke dawowa daga makaranta ko? Kun tsaya wasa ahanya ko?"
"Allah ya fahad sai yanzu muka samu napep..." Maryam tafada tana cire sandal din dake kafarta,
"Bari natashi nakamaku zama ku fadi gaskiya..."
Sun fara rantse rantse kenan ayiyah tashigo dauke da kwanukan zogalen da ta dafa,
"Kai da naga kamarma bakada lafiya amma shine zakazo kafada yara da fada ko fahad?"
Murmushi yayi sannan yatashi zaune,
"Ayiyah lafiyata kalau fa kawai dai jinina aka dan diba..."
"Jini? Meya faru?" Ayiyah tafada tana mikewa tsaye daga durkushen da tayi tana ajiye kwanuka,
"Babu komaifa... Bata da lafiya ne wai kuma ana bukatar jini shine aka debi nawa"
Yana fadar haka ayiyah tagane Bilkisu yake nufi,
"To Allah ya sawwake yabata lafiya.... A asibiti take kenan?"
"Ehhhh, ayiyah taimaka kibani zogalen nima inci..."
"Allah ya sawwake, gashi ai dama babanku na dafawa..."