Sashe 37
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Thank you"
Basu wani bata lokaci ba takarba tatafi yau dai yayi niyyar cin girkinta shiyasa yakira salim awaya yazo suci tare, jalop din macaroni da dankali yaji sadden sai kamshi yake tare sukaci shi dai fahad tsakura kawai yake saboda baya zagewa yaci abinci yanzu. Sosai al'amarinsa da husnah aka samu cigaba domin yana sakar mata fuska yanzu sabanin da ammafa har gobe bai taba jin sonta yana yawo acikin jininsa ba kawai dai yana biye mata ne kuma yanajin shakuwa mai karfi tsakaninsu.Duk da baya son karatu kusa da gida yacike D.E kamar yadda Yaya auwal yace yanzu kawai zaman jiran admission yakeyi.
***
Bilkisu kam ranar da sukayi fada da wise tayi kuka kamar me dakyar hamood yashawo kanta ta canja kaya yakaita chemist aka yimata plasta awurin aka manne da audiga da bandeji, suna dawowa kuma yakalleta yana fadin,
"Shawarar da zan baki babu ruwanki da shiga sabgar wise domin ita dambe awajenta ba komai bane sannan tafi karfinki saboda harda maza dambe take...."
Cikin masifa da jin haushi bilkisu ta kalleshi,
"To yanzu me kake nufi? Nufinka kenan wannan ciwon da taji min taci bulus bazaka tsawatar mata ba?"
"Kinga bilkisu dan Allah kibarni naji da bakin cikin satar da akayi min, nidai nafada miki babu ruwanki da ita idan kuma bahaka ba to jiki magayi...."
Tsabar bakin ciki kasa cewa komai tayi har yafita daga dakin, tagumi ta rafka tama rasa wanne irin tunani yadace tayi. Tun daga wannan rana takoma rayuwar daki domin bata fitowa sai idan wani abu zatayi shiyasa zaman gaba daya ya dameta kuma ya gundireta wannan dalilinne yasata yanke shawarar tunkarar hamood da maganar komawarta aiki ko tasamu tarage kadaicin da take ciki tunda ko babu komai fitar zaiyi keeping dinta busy, aranar da daddare bayan yashigo ta sameshi da maganar wani kallo yayi mata irin na yan iska sannan yaci gaba da abinda yakeyi yana cewa,
"Mai gado kenan, wai ke wacce irin macece? Atunaninki zan amince dake har inbarki kifita aiki bayan alhalin nasan har yanzu wannan karamin yaron ba daina sonki yayiba? Ai sai kuhada kai kurinka ha'intata..."
Cikin bacin rai ta kalleshi bakinta har rawa yake yi,
"Hamood kallon da kake yimin kenan? Wannan itace sakayyar da zaka yimin? Idan har Zan iya hada baki da fahad inci amanarka to meya hana inzauna tare dashi tun farko?"
"Look mai gado dan Allah karki nemi yimin hayaniya yanzu saboda agajiye nake i have to rest so pls walk out....."
Bakinta abude da mutukar mamaki tajuya tafice zuwa dakinta rasa wanne irin fassara zata yiwa wadannan kalaman na hamood tayi, wato dai yanaso yace mata bai yarda da itaba? Kasa bacci tayi a wannan daren shiyasa tunda sassafe takira abbanta awaya ta sanar masa nan yace zai kira hamood din tabashi number dinsa, wurin 9 yashiga dakinta yace tatashi zasuje gidansu abbanta na nemansu duk wannan maganar yana yinta ne cikin daurewar fuska, haka suka je gidan babu wanda ke cewa ko uffan Abba yana zaune falonsa yagama karyawa amutukar ladabce hamood yagaida Abba da Ammah kowannensu ya amsa fuska asake sannan Abba yayiwa hamood maganar da yakirashi dominta wato na komawar bilkisu aiki,
"Hamood mai gado ta kirani tace tana son zata koma aiki amma da tayi maka maganar kanuna kamar baka aminceba domin ma tamkar har yanzu baka gama yarda da itaba hakane....?"
Sosa keya yasoma cikeda ladabin karya yace,
"Abba wallahi bahaka nake nufiba, nidai kawai banida ra'ayin matata tayi aikine nafiso tazama full hause wife"
"To shikenan ke mai gado kinji abinda yace, tunda baya bukata kiyi hakuri...
Kibari anjima zan turo miki kudi a account dinki sannan duk sanda kike da wata matsala ki sanar dani..."
"Shikenan Abba, nagode madalla"
Tafada tana share hawayenta, anan hamood yatafi yabarta zata wuni bayan yatafi su amma Nasiha suka yiyyi mata har tasaki ranta, tun kafin tabar gidan taga abba yatura mata dubu dari biyar cikin account dinta, bayan sallar magrib tana niyyar tafiya saiga Abba yadawo shida ya mudan wanda yakawoshi gida daga garko domin yau can abban yaje kuma cikin rashin sa'a motar da suka tafi da ita tasamu matsala ganin zata tafi Abba yace ya mudan yakaita gida, baya tashiga suka tafi lokacin da sukaje kofar gate din gidan anan ta sauka suna yin sallama da ya mudan hamood yadanno motarsa shida wise hakimce agaba kamar kullum tayi daurinta na ture kaga tsiya.........
*_Ummi Shatu_*
*Wannan littafin na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
34 ***Tana shirin barin wurin hamood yakaraso shida wasila wani mugun kallo ya watsa musu ita da ya mudan sannan ya danna hancin motarsa zuwa cikin gida, bata kara ko mintuna ukuba tashiga itama tabar ya mudan zaune yana jimami tambayar zuciyarsa yake tayi,
"Wai dama wannan shine mijin da bilkisu ta aura?"
Yayiwa kansa tambayar nan tafi sau dari kawai tunani yake shin yafadawa bilkisu gaskiya ko kuma karya fada saboda ko babu komai ai yar uwarsa ce daga karshe dai yabi shawarar zuciyarsa na kawai yaja bakinsa yayi shiru domin gudun abinda zaije yazo jan motarsa yayi yabar wurin yanufi gida.
Bilkisu adarare tashiga cikin gidan saboda iya kallon da hamood kadai yayi musu ya isa sanar mata cewa there is something wrong, tana shiga falo suna tsaye shida wise juyowa gaba daya yayi yana harararta,
"Daga ina kike? Maigado bafa zan lamunci yawon ta zubar ba acikin gidan nan..."
Ita tsabar takaici ma sakin baki tayi tana kallonsa, har saida yadiga aya sannan tayi magana,
"Lallai hamood, ya mudan nefa dan uwana abba yasa yakawo ni tunda kai bakaje ka daukoni ba..."
"Ni bawanki ne da zanje na daukoki ko kuwa ni driver dinkine? Kishiga hankalinki kin gane ko..... Aikin banza kawai Malam haka kawai najawa kaina masifa naje na jajibo yar matsiyata...."
Zaro ido bilkisu tayi tana kallonsa,
"Hamood ni kake kira da yar mutsiyata? Wallahi karyar mutum yakira iyayena da wannan sunan, yayan matsiyatan dai suna inda suke..."
Daga haka tawuce sama tana shiga daki tazauna tana ta surutu ita daya cikin masifa,
"Haba wannan wacce irin rayuwace wai? Mutum kullum idan banda cin mutunci da jaraba bashida zance.... Ni wallahi zaman gidanka yafita akaina gaba daya nagaji da igiyar aurenka haba...."
Tun daga ranar tsakaninta da hamood babu daddadar magana abu kadan sai zagi ita dai ji take ankusa zuwa gabar da dole zata bar gidansa domin gudun kada cutar hawan jini ta kamata saboda kullum cikin bacin rai take da damuwa idan yau basu debota da hamood ba to sai sun haura da wise shiyasa duk tabi ta lalace ta fige, tana cikin wannan halin bikin khulsum yazo bilkisu nason taje ayi komai da ita kamar yadda khulsum din tayi mata amma fafur hamood ya hana sai bikin dai yabarta ranar da za afara bikin tun sassafe tabar gidan domin dama jinta take kamar akan kaya, gidan hamood ya zame mata tamkar kurkuku, duk ankon da aka fitar ta turawa khulsum kudi ansiya mata dama ko takan hamood bata bi ba domin wani wulakanci yake ji kwana biyun nan, zuwanta gidan bikin cikin mutane yasata mancewa da damuwarta domin ga kawayensu nan yan makarantarsu da abokan aikinsu, kwana uku aka dauka ana yin bikin sai da aka kai amarya gidanta sannan bilkisu tasamu zama. Lokacin da ta koma gida babu kowa agidan daga hamood har wise din asalima ita daya ta kwana agidan, washe gari ma haka kai saida tayi kwana uku ita daya ce kwal cikin gidan tana rayuwarta takira hamood yace mata yana abuja amma yau ko gobe zai shigo so take yadawo ayi wacce za ayi domin yakamata su nemi magani saboda tagaji da wannan zaman na cuta domin akwai cutarwa acikinsa. Tana zaune falo tana kallon tashar zee world mai gadi yayi mata knocking, hijab tasa ta leka cemata yayi sunyi bako wai hamood ne ya aiko shi, fita compound din gidan tayi, kamar a mafarki taga dr Abrar wato tsohun saurayin khulsum kawarta domin kamarma shi zai auri khulsum din Allah ne dai baiyiba kawai,
"Ahhhh likita... Yau kai nake gani?"
Murmushi yayi yafito daga cikin motarsa,
"Hajiya Bilkisu yan jarida..., ya aikinku? Ina kawarki ashe tayi aure ta kini ko?"
Dariya bilkisu tayi,
"Likita ba kinka tayi ba kawai dai Allah ne baiyi zaku zama ma'aurata ba..."
"Adai yimin dadin baki irin na yan jarida..."
"Ba dadin baki bane gaskiya ce kawai Dr..."
"Wai dama kece wacce hamood yace inkawowa sakon nan?"
"Ehh nice..."
Tafada cikin murmushi,
"Ok to amma meyasa ban taba ganinki a asibitinba? Ai akwai tarurruka da ake shirya muku domin wayar muku dakai da kuma shawarwari da ake baku na musamman domin kula da lafiyarku... Idan har zakubi ka'ida to ko mai lafiya bazai fiku walwala da tsawon kwana ba...."
"A'a likita wai meke faruwa ne? Wanne ciwo kenan?"
Gyara tsayuwarsa yayi, cikin murmushi yace,
"Karki damu bilkisu u know am a Dr,wai dan nasanki ko kin sanni isn't something bad duba da yanayin aikinmu am always confidential soo feel free, wallahi da asibiti ma kikazo bazan taba nunawa cewar nasanki ba that's the rule.... Mu a ka'idar aikinmu koda ace kasan mutum when he comes to u with such case zaka nuna kamar ma baka taba ganinsa ba sai ranar unless shine yayi maka magana i hope u understand?"
Goge fuskarta tayi da gumin dake tsattsafowa tasake kallon Dr abrar dakyau,
"Likita dan Allah fada min in a simple way da zan fahimta saboda ni duk wadannan maganganun naka babu wanda na fahimta am confuse...."
"Bilkisu kenan.... Wai bake hamood yacewa zai aiko akawo muku magani ba? Last 3 days yaje hospital wurina karbar drugs dinsu wanda yakesha saboda lalurar da yake dauke da ita but unfortunately ranar babu maganin ba akawo ba kuma yace min tafiya zaiyi amma idan ankawo intaimaka inkawo masa gida zan samu matarsa sai nabata saboda itama tanada bukata u know he's my childhood friend...."
"Nidai to... Amma wallahi har yanzu ban ganeba da dai wasila na nanne may be ita yake nufi not me..."
"Wasila....?, wasila kuma? Har yanzu suna tare da wasila?"
"Likita kasanta ne...?"
"Ehhh ai itace ta jona masa HIV din... Can wurin yawon barikinsu suka hadu, dama suna tare?"
"Kana nufin ba matarsa bace?"
Basu wani bata lokaci ba takarba tatafi yau dai yayi niyyar cin girkinta shiyasa yakira salim awaya yazo suci tare, jalop din macaroni da dankali yaji sadden sai kamshi yake tare sukaci shi dai fahad tsakura kawai yake saboda baya zagewa yaci abinci yanzu. Sosai al'amarinsa da husnah aka samu cigaba domin yana sakar mata fuska yanzu sabanin da ammafa har gobe bai taba jin sonta yana yawo acikin jininsa ba kawai dai yana biye mata ne kuma yanajin shakuwa mai karfi tsakaninsu.Duk da baya son karatu kusa da gida yacike D.E kamar yadda Yaya auwal yace yanzu kawai zaman jiran admission yakeyi.
***
Bilkisu kam ranar da sukayi fada da wise tayi kuka kamar me dakyar hamood yashawo kanta ta canja kaya yakaita chemist aka yimata plasta awurin aka manne da audiga da bandeji, suna dawowa kuma yakalleta yana fadin,
"Shawarar da zan baki babu ruwanki da shiga sabgar wise domin ita dambe awajenta ba komai bane sannan tafi karfinki saboda harda maza dambe take...."
Cikin masifa da jin haushi bilkisu ta kalleshi,
"To yanzu me kake nufi? Nufinka kenan wannan ciwon da taji min taci bulus bazaka tsawatar mata ba?"
"Kinga bilkisu dan Allah kibarni naji da bakin cikin satar da akayi min, nidai nafada miki babu ruwanki da ita idan kuma bahaka ba to jiki magayi...."
Tsabar bakin ciki kasa cewa komai tayi har yafita daga dakin, tagumi ta rafka tama rasa wanne irin tunani yadace tayi. Tun daga wannan rana takoma rayuwar daki domin bata fitowa sai idan wani abu zatayi shiyasa zaman gaba daya ya dameta kuma ya gundireta wannan dalilinne yasata yanke shawarar tunkarar hamood da maganar komawarta aiki ko tasamu tarage kadaicin da take ciki tunda ko babu komai fitar zaiyi keeping dinta busy, aranar da daddare bayan yashigo ta sameshi da maganar wani kallo yayi mata irin na yan iska sannan yaci gaba da abinda yakeyi yana cewa,
"Mai gado kenan, wai ke wacce irin macece? Atunaninki zan amince dake har inbarki kifita aiki bayan alhalin nasan har yanzu wannan karamin yaron ba daina sonki yayiba? Ai sai kuhada kai kurinka ha'intata..."
Cikin bacin rai ta kalleshi bakinta har rawa yake yi,
"Hamood kallon da kake yimin kenan? Wannan itace sakayyar da zaka yimin? Idan har Zan iya hada baki da fahad inci amanarka to meya hana inzauna tare dashi tun farko?"
"Look mai gado dan Allah karki nemi yimin hayaniya yanzu saboda agajiye nake i have to rest so pls walk out....."
Bakinta abude da mutukar mamaki tajuya tafice zuwa dakinta rasa wanne irin fassara zata yiwa wadannan kalaman na hamood tayi, wato dai yanaso yace mata bai yarda da itaba? Kasa bacci tayi a wannan daren shiyasa tunda sassafe takira abbanta awaya ta sanar masa nan yace zai kira hamood din tabashi number dinsa, wurin 9 yashiga dakinta yace tatashi zasuje gidansu abbanta na nemansu duk wannan maganar yana yinta ne cikin daurewar fuska, haka suka je gidan babu wanda ke cewa ko uffan Abba yana zaune falonsa yagama karyawa amutukar ladabce hamood yagaida Abba da Ammah kowannensu ya amsa fuska asake sannan Abba yayiwa hamood maganar da yakirashi dominta wato na komawar bilkisu aiki,
"Hamood mai gado ta kirani tace tana son zata koma aiki amma da tayi maka maganar kanuna kamar baka aminceba domin ma tamkar har yanzu baka gama yarda da itaba hakane....?"
Sosa keya yasoma cikeda ladabin karya yace,
"Abba wallahi bahaka nake nufiba, nidai kawai banida ra'ayin matata tayi aikine nafiso tazama full hause wife"
"To shikenan ke mai gado kinji abinda yace, tunda baya bukata kiyi hakuri...
Kibari anjima zan turo miki kudi a account dinki sannan duk sanda kike da wata matsala ki sanar dani..."
"Shikenan Abba, nagode madalla"
Tafada tana share hawayenta, anan hamood yatafi yabarta zata wuni bayan yatafi su amma Nasiha suka yiyyi mata har tasaki ranta, tun kafin tabar gidan taga abba yatura mata dubu dari biyar cikin account dinta, bayan sallar magrib tana niyyar tafiya saiga Abba yadawo shida ya mudan wanda yakawoshi gida daga garko domin yau can abban yaje kuma cikin rashin sa'a motar da suka tafi da ita tasamu matsala ganin zata tafi Abba yace ya mudan yakaita gida, baya tashiga suka tafi lokacin da sukaje kofar gate din gidan anan ta sauka suna yin sallama da ya mudan hamood yadanno motarsa shida wise hakimce agaba kamar kullum tayi daurinta na ture kaga tsiya.........
*_Ummi Shatu_*
*Wannan littafin na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
34 ***Tana shirin barin wurin hamood yakaraso shida wasila wani mugun kallo ya watsa musu ita da ya mudan sannan ya danna hancin motarsa zuwa cikin gida, bata kara ko mintuna ukuba tashiga itama tabar ya mudan zaune yana jimami tambayar zuciyarsa yake tayi,
"Wai dama wannan shine mijin da bilkisu ta aura?"
Yayiwa kansa tambayar nan tafi sau dari kawai tunani yake shin yafadawa bilkisu gaskiya ko kuma karya fada saboda ko babu komai ai yar uwarsa ce daga karshe dai yabi shawarar zuciyarsa na kawai yaja bakinsa yayi shiru domin gudun abinda zaije yazo jan motarsa yayi yabar wurin yanufi gida.
Bilkisu adarare tashiga cikin gidan saboda iya kallon da hamood kadai yayi musu ya isa sanar mata cewa there is something wrong, tana shiga falo suna tsaye shida wise juyowa gaba daya yayi yana harararta,
"Daga ina kike? Maigado bafa zan lamunci yawon ta zubar ba acikin gidan nan..."
Ita tsabar takaici ma sakin baki tayi tana kallonsa, har saida yadiga aya sannan tayi magana,
"Lallai hamood, ya mudan nefa dan uwana abba yasa yakawo ni tunda kai bakaje ka daukoni ba..."
"Ni bawanki ne da zanje na daukoki ko kuwa ni driver dinkine? Kishiga hankalinki kin gane ko..... Aikin banza kawai Malam haka kawai najawa kaina masifa naje na jajibo yar matsiyata...."
Zaro ido bilkisu tayi tana kallonsa,
"Hamood ni kake kira da yar mutsiyata? Wallahi karyar mutum yakira iyayena da wannan sunan, yayan matsiyatan dai suna inda suke..."
Daga haka tawuce sama tana shiga daki tazauna tana ta surutu ita daya cikin masifa,
"Haba wannan wacce irin rayuwace wai? Mutum kullum idan banda cin mutunci da jaraba bashida zance.... Ni wallahi zaman gidanka yafita akaina gaba daya nagaji da igiyar aurenka haba...."
Tun daga ranar tsakaninta da hamood babu daddadar magana abu kadan sai zagi ita dai ji take ankusa zuwa gabar da dole zata bar gidansa domin gudun kada cutar hawan jini ta kamata saboda kullum cikin bacin rai take da damuwa idan yau basu debota da hamood ba to sai sun haura da wise shiyasa duk tabi ta lalace ta fige, tana cikin wannan halin bikin khulsum yazo bilkisu nason taje ayi komai da ita kamar yadda khulsum din tayi mata amma fafur hamood ya hana sai bikin dai yabarta ranar da za afara bikin tun sassafe tabar gidan domin dama jinta take kamar akan kaya, gidan hamood ya zame mata tamkar kurkuku, duk ankon da aka fitar ta turawa khulsum kudi ansiya mata dama ko takan hamood bata bi ba domin wani wulakanci yake ji kwana biyun nan, zuwanta gidan bikin cikin mutane yasata mancewa da damuwarta domin ga kawayensu nan yan makarantarsu da abokan aikinsu, kwana uku aka dauka ana yin bikin sai da aka kai amarya gidanta sannan bilkisu tasamu zama. Lokacin da ta koma gida babu kowa agidan daga hamood har wise din asalima ita daya ta kwana agidan, washe gari ma haka kai saida tayi kwana uku ita daya ce kwal cikin gidan tana rayuwarta takira hamood yace mata yana abuja amma yau ko gobe zai shigo so take yadawo ayi wacce za ayi domin yakamata su nemi magani saboda tagaji da wannan zaman na cuta domin akwai cutarwa acikinsa. Tana zaune falo tana kallon tashar zee world mai gadi yayi mata knocking, hijab tasa ta leka cemata yayi sunyi bako wai hamood ne ya aiko shi, fita compound din gidan tayi, kamar a mafarki taga dr Abrar wato tsohun saurayin khulsum kawarta domin kamarma shi zai auri khulsum din Allah ne dai baiyiba kawai,
"Ahhhh likita... Yau kai nake gani?"
Murmushi yayi yafito daga cikin motarsa,
"Hajiya Bilkisu yan jarida..., ya aikinku? Ina kawarki ashe tayi aure ta kini ko?"
Dariya bilkisu tayi,
"Likita ba kinka tayi ba kawai dai Allah ne baiyi zaku zama ma'aurata ba..."
"Adai yimin dadin baki irin na yan jarida..."
"Ba dadin baki bane gaskiya ce kawai Dr..."
"Wai dama kece wacce hamood yace inkawowa sakon nan?"
"Ehh nice..."
Tafada cikin murmushi,
"Ok to amma meyasa ban taba ganinki a asibitinba? Ai akwai tarurruka da ake shirya muku domin wayar muku dakai da kuma shawarwari da ake baku na musamman domin kula da lafiyarku... Idan har zakubi ka'ida to ko mai lafiya bazai fiku walwala da tsawon kwana ba...."
"A'a likita wai meke faruwa ne? Wanne ciwo kenan?"
Gyara tsayuwarsa yayi, cikin murmushi yace,
"Karki damu bilkisu u know am a Dr,wai dan nasanki ko kin sanni isn't something bad duba da yanayin aikinmu am always confidential soo feel free, wallahi da asibiti ma kikazo bazan taba nunawa cewar nasanki ba that's the rule.... Mu a ka'idar aikinmu koda ace kasan mutum when he comes to u with such case zaka nuna kamar ma baka taba ganinsa ba sai ranar unless shine yayi maka magana i hope u understand?"
Goge fuskarta tayi da gumin dake tsattsafowa tasake kallon Dr abrar dakyau,
"Likita dan Allah fada min in a simple way da zan fahimta saboda ni duk wadannan maganganun naka babu wanda na fahimta am confuse...."
"Bilkisu kenan.... Wai bake hamood yacewa zai aiko akawo muku magani ba? Last 3 days yaje hospital wurina karbar drugs dinsu wanda yakesha saboda lalurar da yake dauke da ita but unfortunately ranar babu maganin ba akawo ba kuma yace min tafiya zaiyi amma idan ankawo intaimaka inkawo masa gida zan samu matarsa sai nabata saboda itama tanada bukata u know he's my childhood friend...."
"Nidai to... Amma wallahi har yanzu ban ganeba da dai wasila na nanne may be ita yake nufi not me..."
"Wasila....?, wasila kuma? Har yanzu suna tare da wasila?"
"Likita kasanta ne...?"
"Ehhh ai itace ta jona masa HIV din... Can wurin yawon barikinsu suka hadu, dama suna tare?"
"Kana nufin ba matarsa bace?"