← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 67

Sashe 21

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Turo baki tafara yi daga karshe ma dai tashi tayi tafice daga shagon ita adole tayi fushi, habibu kanin hamza dake koyon dinki ashagon ya aika yabashi kudin cefane yace yayi yakai masa gidanshi ai kuwa nan su hamza suka cigaba da tsokanarshi. Acan bangaren bilkisu kuwa yau bata da matsalar kadaici domin bayan su mariya sunzo babu dadewa su Hindu suma sukazo kuma yinar mata zasuyi cur, lokacin da aka kawo cefanen da fahad ya aiko ma meenah ce takarba ta dora musu girki, yau yanayin da bilkisu take jinta na farin ciki yafi gaban kwatantawa danma maama bata nan da abin sai yafi haka, ayanda ta fahimta daga meenah har Hindu duk ciki garesu nan dadi yasake kamata domin tana bala'in son kannen nan nata kamar yadda suma ke sonta, dama tabawa meenah tace ta dafa duk abinda takeso nan meenah tace shinkafa da miya zatayi ai kuwa Hindu tace bazai yuyuba taliya da miya za adafa saboda ita tunda tasamu ciki ta daina cin shinkafa ita kuma meenah tace itama bata cin taliya yanzu sai shinkafa kadai, dariya abin yabawa bilkisu tace to duk su kwantar da hankalinsu sai adafa shinkafa da taliya kowanne daban mai son shinkafa yaci mai son taliya shima yaci ita kam gaba daya zataci shinkafar da taliyar dahaka dai tasamu nasarar raba wannan fadan. Sai la'asar fahad yadawo gidan domin yana son zuwa filin ball, yana zuwa su mariya na shirin tafiya yadauko dari biyu zai basu su hau napep bilkisu ta hana tashiga bedroom dinta ta dauko dari hudu tabasu tace kowa yadauki dari bibbiyu sannan ga naira dari su biya napep din, yana shiga falo yaga su meenah,

"Ya fahad sannu da zuwa..."

Shifa idan suna cewa yayan nan jin kansa yakeyi asama yana huruwa,

"Gaskiya munyi fushi sai yau zaku zo mana, maman hudah tun jiya tazo"

Dariya Hindu tayi,

"Ayi mana afuwa ya fahad insha Allah sai kunma gaji da ganinmu agidan nan"

"A'a bazamu gaji dakuba, koda kuwa zaku zo kullum"

Ahaka bilkisu tashigo ta samesu abincinsa ta dauka ta kai masa daki tafito tana cemasa,

"Ga abincin ka can kashiga kaci"

"Nagode hajjaju"

Tashi yayi yawuce ciki, shinkafa da taliya da salad yagani, dama yunwa yake ji shiyasa babu bata lokaci yazuba yafara ci saida yakoshi sannan yashiga wanka agurguje domin yaga kamar yakusa makara, kayan ball dinsa yasaka dark blue yadauki combos dinshi a hannu yafita, sallama sukayi dasu Hindu dan yasan dakyar idan zai dawo yasamesu, sai bayan da yatafi sannan bilkisu ta dauko jakar kudinta tabawa su meenah su kirga mata tanata basu labarin abubuwan da suka kasance lokacin da tana gidansu fahad gaskiya abin ya kayatar dasu bama ita kadaiba dan abinda suka lissafa kudin da aka tara mata dubu talatin da bakwai da dari biyar har dari biyar din da ta baiwa su mariya dazu dubu talatin da takwas kenan, dubu biyar biyar tabasu harda na maama tace itama akai mata.

Daf da lokacin sallar magrib suka tafi ji tayi kamar ta rikesu ta hanasu tafiya amma babu damar hakan domin mijin meenah ne yazo daukarsu zasu bi su ajiye Hindu, ciki takoma tarasa me zatayi saboda babu wani sauran aikin da yarage ma agidan domin su Hindu sunyi mata komai kafin su tafi sai dai dan girkin dare da zata yiwa fahad wannan kuwa indomie ma zata dafa masa, dadinta ma daya da wuta shine tasamu damar fara kallon sabon series din da Bollywood ke nunawa mai suna zahba walam ya'ood, tana tsaka da kallon fahad yadawo, wanka yafara wucewa yayi sannan yazo yayi sallar magrib daga nan bai kuma fitaba sai salim da yayi masa waya wai zaizo yagaida anty amarya kafin ishah kuwa sai gashi shiyasa tare ta dafa musu indomie din da dafaffen kwai,kan dining takai musu lokacin suna kallon ball atashar sport +,daki tawuce da yar guntuwar tata indomie din acikin flate taje ta zauna taci koda tagama ma anan tayi zamanta ta bude laptop dinta tashiga YouTube domin yin kallo, sai wurin 9 sannan salim yatafi, duk da haka bata koma falon ba taci gaba da zamanta adaki daga karshe tayi shirin bacci ta kwanta bata san lokacin da fahad yazo yayi nasa shirinba dan yau bai kunna fitila ba.

Haka suka cigaba da zama idan zai shigo daki wai dole sai yayi knocking tabashi izini shima idan yana ciki idan zata shigo sai tayi knocking yabata izini ahaka har sukayi 2 weeks kuma lokacin ne zata fara fita aiki duk da cewa acikin sati biyun nan rana daidai ce da baza suyi baki ba su ayiyah ma itada mamuh sunzo sunga daki sunyi fatan alkhairi, ranar friday maama tazo dama ranar bilkisu bata fitaba amma shi fahad yana shagonsu yan shagon nasu su tj sun hura masa wutar wai dole sai yau sunje gidanshi sunci girkin amarya, daga karshe dai text massage yayi mata yace,

_Princess dan Allah ki taimaka kiyi girkin mutum biyar wallahi yan shagonmu sun dameni wai sai sunzo.... Pls hajjaju._

Lokacin da taga sakon bata yimasa reply ba amma tafadawa maama abinda yaturo ai kuwa maama tazage ta tayata suka shirya shiryayyen girki duk da cewa unguwar ba asaida abubuwa amma saida bilkisu tafita da kanta ta samo almajiri ta aikeshi can bakin titi yaje ya iyo mata siyayyar duk abinda takeso bayan yakawo mata tace anjima can yazo yakarbi abinci,

Bayan sun gama girkin wanka tashiga tayi tasha doguwar riga ta atamfa ta danyi kwalliya sama sama, tana kitchen tana zuba musu abincin itada maama wacce ke daki tana salla suka shigo, fuskarta asake ta karbesu ta kalli fahad dake wani jin kansa asama shi ga mai gida murmushi tayi,

"Sannu da zuwa, table is ready"

"Thank you sweet heart"

Basu hau dinning dinba domin yayi musu kadan sai anan tsakiyar falon suka baje ba karamin dadi fahad yajiba domin girkine na fita kunya su bilkisu sukayi shi white rice and vegetables stew ga hadadden salad yasha dafaffen kwai abin dai ba acewa komai sannan ga drinks agefe mai dan Karen sanyi kowa saida abin ya burgeshi, tafiya tayi wurin maama tabasu wuri bayan sun gama ya leko cikin dakin suka gaisa da maama yakara gaba bashi yadawo ba sai magriba saboda yau babu zuwa filin ball ita tarasa me yake ji a ball dinnan da kullum sai yaje ranar juma'a ne kawai baya zuwa. Ranar litinin tafara fita aiki sai dai wannan karon karfe uku take tashi sabanin da, zamansu da fahad normal babu wata matsala tayanda take so yake bida ita kullum kuma afalo yake kwana aikin gida kuwa wannan almajirin data samu shine yake yimata shara da mopping idan da aike ta bashi amma fa har yau fahad bai san dashi ba saboda lokacin da almajirin zaizo baya nan wani lokacin kuma kafin yatashi daga bacci dasafe zaizo yayi aikinsa yatafi amma banda falon sai tace wannan yabarshi zatayi yau dai da Allah yayi za ahadu fahad na gidan baije ko inaba dama weekend ne yana da dinkuna ashago amma baya jin zai fita yanzu sai yamma yana kwance afalo daga shi sai three quarter iya gwiwa da riga armless yana kallo sai yaji anbude gida anshigo harda sallama tashi yayi yafita jin muryar namiji yana fita yaga saurayi zaiyishi atsaye hakama ahaife kilama yafishi ahaifen,

"Lafiya? Ya akayi?"

"Ehh nazo aikine.. Nine meyiwa hajiya aiki"

"Aiki? Aikin me?"

"Shara nake yimata da iyo cefane"

"To daga yau karka kara zuwa na sallameka, karka yarda ka kara dawowa"

Saida yaga tafiyar almajirin sannan yarufe gidan yasa sakata yashiga ciki, yau kam babu maganar neman izini kawai yafada mata daki tana kan gado da bra ajikinta da skirt tana kwalliya da alama daga wanka tafito,

"Menene ma'anar wannan abun da kikayi maigado? Ya zaki kawo min almajiri gidana batare da sanina ba..."

Tuni ta dauki hijabinta tasaka tana kallonshi,

"Almajirin ne wani abu? Yaron da na girmeshi"

"Ke kike ganinshi yaro amma ni awurina ba yaro bane, ya zaki dauko wanda ko atsaye yana daidai dani, ai sai akasa banbance dani dashi wanene mai gidan, wannan ma ai tsaf zaiyi min duka"

"To yanzu me kakeso ayi wai?"

"Ai narigada na sallameshi..."

Har yajuya zai tafi tariko rigarshi,

"Da ka koreshi din to yanzu wa zan rinka aika?"

"Ni ki aikeni mana, ai gara ni kisani aikin kuma kiyita aikena da ki kawo min wancan gardin ki ajiye min agida wanda ko adake tsaf zaiyi min duka yanda nake dan kadan dinnan dani..."

Sakinshi tayi yafita yanata yi da bakinshi wanda kusan rabi kishine acikin maganganun nashi. Aranar da yamma suka shirya sukaje gidan Anty Fauziyya suka gaisheta acan sukayi sallar magrib sannan suka dawo gida da zummar gobe ma zasu jewa yaya asabe da su anty kubra. Yau da zaiyi wanka da daddare rasa kayan baccin da zai saka yayi saboda shi baya maimaita kaya idan yasaka guda daya sai anwanke yake sakawa gashi tunda yazo gidan sakawa kawai yake yana tarawa ba awankewa dama ayiyah ce keyi masa wankin inner wears dinshi manyan kayan kuma wanki yake kaiwa to yanzu babu ayiyah, tsayawa yayi agaban drewar din bayan yarike kugunshi da hannunshi guda daya......

*Dan Allah idan har kin san baki siyaba to karki karanta.*

*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO.*

*KAMAR DA WASA...!*

_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*

*22*

***Shagwabe fuska yayi ya juya ya kalli bilkisu wacce ke sanye da hijab ajikinta amma aciki sleeping dress ne riga da wando iya gwiwa,hankalinta gaba daya yana kan system din da take dannawa,

"Wai yau wanne kayan zan saka...?"

Dagowa tayi ta kalleshi sannan ta maida kanta kan laptop dinta,

"Da nice nake fada maka wanda zaka saka?"

Shiru yayi mata zuwa can yayi kwafa,

"To wallahi yau karki fito bayan na kwanta dan babu mamaki tsirara zan kwana..."

Tabe baki tayi,

"Kayi duk yadda kaso..."

Jallabiya ya dauka daga cikin kayansa yanufi bathroom yanata kukkumburo baki,

"Wai haka kawai mutum yanada mata amma komai shi zai yiwa kansa..."

"Magana kake yine?"

Yaji tafada yana kokarin shiga toilet din,

"Ni ba dake nake ba"
Chapter 21 · 0% Book details