← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 42 OF 67

Sashe 42

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dariya abin yabawa fahad jin mijin mamaa na kiransa da wai Yaya bayan kuma yagirme masa ahaife sosai, karbar pampers din dake hannunta fahad yayi bayan yamikawa abban huda awwab, dama pampers kadai tazo siyawa awwab irin babban nan, wurin biyan kudi fahad yaje yahada yabiya har da nasu duk da sunata cewa yabarshi, har zai tafi maama ta dakatar dashi ta karbi number dinshi domin ita dai haka kawai take kaunar fahad shiyasa ba ason ranta aurensu ya mutuba dan dai kawai kaddara tashiga cikine.Lokacin da yakoma gida magrib tayi shiyasa saida yatsaya yayi salla sannan yashiga cikin gida yakaiwa su ayiyah abunda yasiyo musu, sunata saka masa albarka yadauko abincinsa shida Abba yafito domin abban ma yana gari tun watanni biyu da suka wuce yagama service yanzu haka yana zuwa bureau of statistics acan yake dan taba kwadago,

Yana zama gefen katifa kamar da tunanin bilkisu yazauna domin gaba daya hirar da sukayi da maama ce tafara dawowa cikin tunaninsa, sama sama yaci abincin yana daf da kammalawa yaji anfara kiran sallar isha kasancewar yanayi yasauya yanzu da wuri ake yinta, tashi yayi yafita masallaci bayan yadawo ya cire rigar sanyin dake jikinsa ya kwanta da sauran rigunan ajikinsa da safa akafarsa bargo yaja ya lulluba sannan yajawo laptop dinshi yakunna, gaba daya tunanin bilkisu ne ke neman addabar ruhinsa duk da yanata kokarin ganin hakan bai kasanceba. Duk abinda yasan idan yayi zai dauke masa hankali kar yakai ga tuna bilkisu yayi amma abin yafaskara, laptop din ya ajiye agefensa ya kunna wa'azin marigayi sheikh Albani Zaria yana saurara wanda yarage volume din sosai, daga kanshi yayi ya kalli sama kawai yana dulmiya cikin kogin tunani, ji yake kamar zai sake fadawa tafkin kaunarta akaro na biyu duk da bazai so hakanba, yasan kawai yana yaudarar kansa ne wurin kokarin hana zuciyarsa tunaninta domin abinda zuciyar take so ne, kamanninta bazasu taba gushewa daga cikin zuciyarshi ba, to tayaya ma zuciyarshi zata manta da ita alhalin silar sonta ne ya illatata har tasamu rauni daga wani bangare na jikinta, jin anturo kofa za ashigo yasashi maida hankalinsa ga kofar, yaya abba ne yashigo yana rataye da jakar laptop dinshi yana sanye cikin farin yadi,

"Amma gaskiya yau kayi over time... Duk cikin aikinne haka?" Yafada cikin sanyin murya sannan kuma ayanda yayi maganar ahankali yayita irin yadda yakeyi duk lokacin da ciwonshi yatashi hakan yasa Abba karasowa cikin faduwar gaba,

"Na dan biya ta gidan Anty asabe ne wai zan yimata register din wani abu nasu na malaman makaranta.... Wai amma lafiya kuwa?"

Murmushi fahad yayi yana gyara kwanciyarshi zuwa barin dama tayadda zai fuskanci Abba dakyau,

"Lafiya lau nake meka gani?"

"Naji maganarka ne ahankali... Amma kasha maganinka kuwa?"

"Nasha dazun nan, ka kwantar da hankalinka fa lafiya lau nake Allah"

Sai lokacin Abba yajishi yadan samu sukuni, ajiye jakarshi yayi yakalli fahad,

"Wannan sandararren abincin fa...?"

"Nakane mana..."

"Tab, ni ai yanzu ruwan zafi zansha, bari nashiga cikin gida nasa su Mariya su dafa min..."

"Su Maryam na aikatuwa hannun samarin gidannan... Idan kowa yayi aure dai sa huta suma" inji fahad,

Daukar flask din abincin abba yayi yanufi hanyar fita yana cewa,

"Ni ai ko nayi aure da daya acikinsu zan tafi..."

"Katafi da ita tazama yar aikinku ko? Ai ayiyah bazata baka ba dama dai nine..."

Baiji abinda Abba yake fada ba sakamakon karar da wayarshi tasoma yi, ganin husnah yasashi jin gabanshi yayi faduwar da har saida yasa hannu ya dafe kirjinsa,cikin sanyin murya yadauki wayar itama najin muryarshi haka yasata jin hankalinta yatashi nan tashiga tambayar ko ciwonshi ke neman tashi amma yace mata a'a saida taji sunjima suna hira baiyi wani abuba sannan hankalinta ya kwanta. Tunda suka gama waya da husnah yake cikin duniyar tunani, idanuwanshi alumshe ga wa'azi nayi cikin system dinshi amma azahirin gaskiya ba wa'azin ma yake saurara ba ahaka abba yadawo dakin yayi shirin bacci yadauki laptop din yakashe masa sannan ya kwanta saboda duk azatonshi bacci fahad din keyi bai san tunani yake tayiba tunanin bilkisu wadda yasan har gaban abada bazai taba iya raba zuciyarshi da sonta ba duk da har gobe yana jin zafin abinda tayi masa amma baya danganta hakan da laifinta ko laifinshi yabarshi amatsayin rubutacciyar kaddara wacce shida ita basu isa guje mata ba.

*_Ummi Shatu_*

BAZATA

*Littafinnan na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*

40***Sam daren ranar fahad bai samu runtsawa ba ko kadan yana ta sake sake cikin zuciyarsa ya kwance ya saka har dare yayi nisa duk da gargadin likita yana yawan fado masa zuciyarsa inda likitan ke cewa yaguji yawaita tunani haka kuma ya rinka samun isasshen bacci arana fiyeda na awa shida. Ganin dai bashida mafita sannan kuma baida guntuwar dabara yasashi fawwalawa Allah dukkan lamuransa dakyar yasamu bacci ya daukeshi wanda sanadiyyar hakan saida ya makara wurin tashi sallar asubah, sau uku Yaya Abba na tashinsa amma yana sake jan bargo balle ga uban sanyin da ake zurarawa sai bayan da aka fito daga masallaci Abba yasake tashinsa, tashi yayi yana babbata fuska kamar zaiyi kuka yanufi toilet saboda kwata kwata baya son taba ruwan sanyi a wannan lokacin sai dai hakan yazama dole. Har gari yawaye rana tafito bai tashi daga baccin da ya koma ba sama sama yake jin sallamar da Abba keyi masa bayan yashirya tsaf domin tafiya aiki, shikam sake gyara kwanciyarshi yayi yaja bargo ya lulluba amma ko minti biyu baiyi ba karar wayarshi ya tasheshi, dan guntun tsaki yaja sannan ya lalubo wayar wadda ke can karkashin pillown Abba,

"Abokina ya akayi?" Shine abinda yace bayan ya daga wayar,

"Kafita ne?" Salim yafada daga daya bangaren,

"A'a ina gida akwance...."

"To bari nazo nakarbi key din babur dinka dan Allah..."

"Sai kazo, idan kashigo ka dubashi can gaban katifa dan Allah basai ka tasheni ba...."

Daga haka yakashe wayar yasake gyara kwanciyarsa cikin sa'a bacci yafara fisgarsa amma lokacin da salim yashigo dakin saida yatashi duk da salim din bai tasheshi ba, bude kansa yayi ya leko yana lumshe idanuwa,

"A'a kaida kace kar atasheka kuma menene haka?"

Maida kansa yayi ya kwantar yana cewa,

"Dallah malam ni ka rabu dani bayan kaine ka tadani..."

Dariya salim yayi yafice daga dakin yana cemasa,

"Ka jirani inje indawo inyaso sai mu hau saman dakyau"

Koda salim yafita kasa komawa baccin yayi ganin lokaci na tafiya yasashi tashi yajanyo babbar rigar sanyinshi yasaka yafita dukkan hannayensa suna cikin rigar, cikin gida yashiga yadebo ruwan zafi yazo yayi wanka, yafito kenan yana shiryawa salim yadawo, kananan kaya yasaka yadora rigar sanyi yar madaidaiciya mai dogon hannu, zama yayi gefen katifa yana shafa mai, ahankali yace da salim,

"Abokina jiya nasamu labarin matata...."

"Wacce mata? Husnah?"

Harararshi fahad yayi sannan yayi murmushi duk a lokaci guda,

"Yaushe husnah tazama matata? Ai ba adaura mana aureba tukunna, maganar hajjaju Bilkisu nake yimaka.."

Tsaki salim yaja cikin jin haushi yace,

"Wai dan Allah meyasa kai baka da zuciya ne? Yanzu kai ko Bilkisu da kanta tadawo gareka taroki alfarmar ka mayar da ita gidanka yadace ka yarda da hakan? Bare kuma ba itace ta nemi hakanba, wai ana so dole ne? Tunda bata sonka kayi hakuri ka rungumi mai sonka amma bawai wadda bai damu dakai ba.... Harga Allah nidai am not happy da wannan madness din naka...."

Daga ido fahad yayi yana kallonsa saboda har lokacin salim din yana tsaye,

"Shikenan....." Fahad yafada yana cigaba da shafa mai akafarshi yana gamawa yajanyo safa yasaka yasan duk yadda zai kai ga yiwa salim bayani bazai taba ganewa ba saboda shi kadai yasan abinda yakeji, tabbas yasan Bilkisu bata sonshi to amma ai shi yana sonta kuma bashi ya dorawa kansa ba da shi yadorawa kansa da tuni yajima da cire sonta daga zuciyarshi ko dan yahuta.

"Ka zauna mana, bari nakarbo mana abinci muyi breakfast sai mufita gaba daya...."

Zama salim yayi yana harararshi har lokacin haushin kalaman fahad din yakeji, babu jimawa fahad yakawo musu gurasa da miya da dafaffen shayi mai kayan kamshi, ganin har suna kokarin gama cin abincin amma salim bai saki fuska ba yasa fahad langabar da kai,

"Haba abokina kayi hakuri mana ai na hakura kamar yadda kace inyi..."

"Yadai fi maka, amma matar da taso kasheka shine yanzu kake son sake tarayya da ita"

"To ai magana tawuce, nace maka na hakura"

Lab coat dinshi ya dauka da sauran abubuwan da yake bukata suka fita tareda salim, saida yafara zuwa jami'ar bayero yaga husnah sannan yawuce asibiti domin yanzu acan take karatu tana karantar Bsc nursing, shi kansa yasan abinda ya fadawa salim ba gaskiya bane domin bazai taba iya daina son Bilkisu ba shi yanzu fargabarsa ma guda daya ce kar wani yasake zuwa ya rabashi da ita ta hanyar aureta, gaba daya yinin ranar nan haka yayishi sukuku su kansu sauran daliban wadanda aka turosu tare saida suka fuskanci akwai matsala domin kamar marar lafiya haka yazama, su bash ma da suka kirashi video call saida sukayi korafin rashin kuzarinsa domin su ba kano aka turosu ba suna can Zaria, har yagama abinda zaiyi yatafi gida bashida wadataccen kuzari tun daga wannan lokaci yake jin ciwon kai sama sama. Kwana uku da haduwarshi da maama a super market takirashi suka gaisa duk da yaso share maganar Bilkisu amma yakasa saida ya tambayeta nan suka dan taba hira sukayi sallama, saving din number yayi ya ajiye wayar, yasan zaiyi wahala salim ya fahimceshi amma zaiyi iya iyawarsa wajen ganin ya fahimtar dashi, tashi yayi ya shirya yafita bai zame ko inaba sai shagonsu salim lokacin salim din na kofar shagon shida wani mai gyaran generator ganin fahad yasashi yin murmushi, ciki fahad yashiga yana dudduba turarukan dake jere reras,

"Malam me kake nema? Kasan dai babu irin turarenka anan domin kai babbar harka kakeyi mukuma na yaku bayi muke saidawa..."

Dariya fahad yayi yazauna kan kujera yana bashi hannu, musabaha sukayi fahad na cewa,

"Zaka fara sharrin nakane da ka saba? Nifa magana nazo muyi akan Bilkisu..."

Tsaki salim yaja sannan cikin fada yace,

"Wai dan Allah kai maye ne?"

Lips fahad yalashe yana murmushi,
Chapter 42 · 0% Book details