← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 67

Sashe 12

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tunda yafito sai yarasa me zaiyi yasan dai yau yana cikeda wani farin ciki wanda bai taba jin irinsa ba, tafe yake ahankali domin zuwa yasanarwa da salim saboda magana awaya bazata yuyu ba, idonshi ne yakai kan yaran dake tsugunne gaban wata yarinya wacce ke soya awara agefen titi, wurin yakarasa yazaro dari biyar ya mikawa yarinyar,

"Ki rabawa yaran nan sadakar ta dari biyar..."

Daga haka yawuce yanajin yaran sunata murna da yimasa godiya. A shagonsu salim ya sameshi yana kwance shi kadai bayan wasu mata sun gama siyayya sun tafi. Shiga yayi ya zauna agefenshi yana fadin,

"Washh..."

Kallonsa salim yayi, "yadai abokina?"

"Katashi kaji wani labari, ansa min ranar aure yau?"

Ai kuwa tun kafin yarufe bakinsa salim yatashin yana kallonsa,

"Dawa?"

"Da hajjaju mai gado"

Dariya sunan yabaiwa salim shiyasa saida ya dan dara sannan yace,

"Lallai mutumin nan kadage sai kayiwa Abba overtaking..."

Dariya fahad yayi,

"To ya za ayi lokaci nane kawai yazo"

Dariya salim yayi,

"Allah yasanya albarka tareda alkhairinsa, ya kuma zakayi da maganar husna?"

Canja fuska fahad yayi,

"Ya kuwa zanyi, ko na taba cemaka ina sonta ne?"

Jijjiga kai salim yayi,

"Tab akwai rikici, Allah dai ya kiyaye"

"Babu wani rikici malam"

Har dare suna tare da salim, saida salim yarufe shago sannan suka tafi gida gaba daya.

Tunda bilkisu tabar gida bata dawoba sai yamma tana dakinta bayan tafito daga wanka taji wayarta na kara, su elmustapha ne dan haka ta daga tana tsaki tasan maganar dai bata wuce ta kudi,

"Elmustapha ya akai?"

Daga can tajiyo muryar el'ameen yana cewa,

"Adda labour amarya, nine shi yashiga school"

"Amarya kuma?"

Dariya taji yayi mata sannan yace,

"To Allah yasanya alkhairi mudai aturo mana picx din babban yaya"

Daga haka yakatse wayar, ita dai kanta daurewa yayi jin abinda el'ameen yace, to meyake nufi, da haka ta kammala shiryawa ta sanya yar doguwar riga marar nauyi mai hannun shimi kalar ruwan hoda sannan tasa hijab tafita, farar shinkafa da miya tasa Rabi ta zuba mata tashiga dakin ammah wacce ke kwance tana kallon shirin dadin kowa,

"Ke, yaushe kika shigo kuwa"

Zama tayi saman rug dake gaban gadon ammah tana kallon tv din itama,

"Ammah na dan jimafa ai na leko kina bayi"

"Ehh ruwa na dan watsa saboda naji garin adaure yake"

"Gaskiya ana sheka zafi"

Har suka gama hirarsu tatashi tafita ammah bata yimata maganar ansaka ranar bikinta ba har saida Abba yadawo da daddare sannan yakirata yake fada mata, rasa wanne yanayi ta tsinci kanta tayi farin ciki ko bakin ciki? Share fahad din tayi bata nemeshi ba haka shima bai kirata ba. Har akayi kwana biyu basu magantu ba ita gaba daya haushinsa takeji kamar ba itace ta kawoshi ba shikuma barinta yayi ta sarara gashi hidindimu sun fara yimasa yawa saboda tun washe garin ranar da aka sanya ranar auren nan baba yakira yayun fahad din kamar yadda yafada suka tattauna dangane da yadda za ayi akan maganar bikin fahad, shi dai baba yace zai karasa gina masa gidanshi wanda yafara hakama yayunshi maza guda biyu wadanda ke zaune a gombe da zamfara sunce zasu bada kyakkyawar gudun mawa lokacin da baba ke sanar dasu awaya sauran yan uwansa mata kuma sukace zasu taimaka masa wurin yin lefe. Yanzu kam fahad ansamu nayi domin can wurin aikin yake wuni duk da dama ginin yadan deboshi da fadi shiyasa dole sai baba yasaka masa hannu. Kasancewar yau ba ayi aikinba yasashi zama agida domin hutawa, yana kwance adakinshi duk jikinsa ciwo yake kamar shine yake aikin ginin, alamun shigowar text yagani duk tunaninshi husna ce amma da yabude sai yaga sabanin haka domin bilkisu ce taturo masa da,

_Salam idan kasamu time kazo zaku gaisa da kakarmu._

"Tofa.. Wata sabuwa nifa kunyar gaishe gaishen nan nakeji amma ya na iya? Ai idan naki zuwama sai na fuskanci hukunci"

Shi kadai yaketa maganganunshi daga karshe ya yanke shawarar kiran salim domin yarakashi da daddare. A lifan din salim suka tafi bayan sallar isha, kayan marmari suka tsaya suka fara siya mata sannan suka karasa gidan, awaje suka jira har bilkisu ta fito fuskarta dai babu yabo babu fallasa, kasancewar yasan hali shine yafara gaisheta ta amsa sannan suka gaisa da salim wanda take kallonshi ta gefen ido aranta tana jin damuwar wai wadannan zata nuna ranar bikinta amatsayin abokan ango,

"Muje ko" daga haka tawuce gaba suna binta abaya har ciki, iyallo jaraba ana zaune dakin baki ana sharbar tuwon shinkafa miyar taushe wanda tasa aka yimata ga tv ana kallo jin baki zasu shigo yasata yin lullubi ta rufe tuwon,

Cikin barkwanci da tsokana irinta kakanni ta taresu,

"Barka da zuwa angona, ina fata dai nima ka tanadi nawa dakin dan kafarka kafata"

Murmushi fahad yayi yayi shiru bai amsa ba sai salim ne yace,

"Dama ai dakunan mata biyu yayi harda naki wanda yamafi nata kyau"

Ai kuwa nan ta cafke tana cewa bata yarda ba shikuma salim yabiyeta sunata yi, daga fahad har bilkisu basa cewa komai shiru kawai sukayi sai dai murmushi sunfi minti talatin wurin iyallo daga karshe suka ajiye mata tsarabar da suka kawo mata harda na cin goro fahad ya ajiye suka fita, godiya da albarka sun shata wurin iyallo daga nan suka gaida ammah suka fita domin shi Abba yau baya nan, a compound din gidan suka tsaya yayinda salim yafita yabasu wuri, kallonshi tayi yasha coffee din yadin kufta da hula da takalmi sau ciki sannan ta dauke kai, ita kam hijabi ne ajikinta har kasa, shiru sukayi dukkaninsu na dan wani lokaci.

"Mai gadon zinare ya ake ciki? Kinji dai yanda su Abba suka yimana wai aure nanda 2 months nikuma gani mai karamin karfe"

"To ai basai ka takura kanka ba kawai kayi abinda ya sawwaka.... Tunda aurene na wucin gadi" takarasa maganar acikin zuciyarta,

"To Allah yasa bazaki rainaba"

"Babu matsala kayi dai dai karfinka"

"To shikenan, sai gani nagaba,nabarki lafiya, I luv u!!"

Bata amsa masaba yajuya yatafi yana daga mata hannu.

*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*

*KAMAR DA WASA....!*

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

*14*

*Littafin kamar Dawasa na siyarwa ne,yar uwa idan kinada bukata ki siya saiki karanta, ku kuma masu fitar min da book dan Allah ku hakura haka tunda ai kunyi na zumunci.*

***Wasa wasa lamari sai kara girmama yake domin biki yanata matsowa, a bangaren fahad komai yana tafiya daidai domin hatta lefenshi yakusa kammala danma yana baiwa su yaya asabe matsala saboda komai idan suka siyo suka saka idan baiyi masaba sai ya canja idan anyi magana yace shi matarshi babbar yarinya ce yar gayu ba karamar yarinya bace, tun abin yana yimusu ciwo musamman Anty Fauzy mai zuciyar tsiya amma da ta fahimci inda ya dosa saita daina damuwa daga karshe ma duk abinda zasu siya sai sunyi snapping dinshi sun tura masa ta whatsapp yagani, baba kuwa duk atamfofin da aka zuba cikin lefen shine yabada domin cewa fahad yayi yaje shagonsa yadubo duk atamfofin da suka yimasa dama sana'ar baba kenan shago gareshi a kwari na atamfofi zalla kala kala, duk da kayan sauran kadan su gama haduwa har yau bai siyo akwatuna ba saboda yace da kanshi zai siyo kuma da kudinsa, kowa agidan lamarin auren nan na fahad dariya yake bashi har baba ganin abin suke yi tamkar wasa wai fahad ne zaiyi aure, shi dai yanzu ta ginin gidanshi yake domin burinshi kawai yanzu yaga gidan ya kammala.

Bilkisu kam ta cika famm haka kawai lamarin auren nan ke bata haushi gashi kullum saita gwada number hamood amma shiru kamar koda yaushe bata shiga, yau kam amare duk sunzo gida harda maama dama hudah na gidan wurin bilkisu tun ranar da ta raka iyallo gidajensu hudah ta dankafe mata dole sai tare suka taho,

"Adda muma fa mun kwadaitu da son muga big Broz domin anty maama tace yahadu karshe ga class..." Inji meenah,

"Ehh wlhi meenah anty maama cemin tayi wai duk yafi mazajenmu kyau.... Gaskiya Adda labour kina bada kala..." Hindu tafada tana dariya,

"Yara kudai kubari zaku ganshi, wallahi big guy ne har wani suna fa ake fada masa amma ba zakuji abakina ba...."

Ai maama tana rufe baki bilkisu tatashi tabar musu wurin ta shige kitchen domin idan tazauna suka cigaba da haka tana iya make wata aciki.

Yammacin yau yammacine da jama'ar cikin garin kano da kewaye ke mararinsa domin yazo da sauyin weather, sabanin zafi da ake fama dashi kwana biyu yau garin a lullube yake da ni'imar ubangiji sansayyar iska ce ke kadawa ko ina ga sararin samaniya yayi luf luf gwanin sha'awa tamkar hadari domin da alamarsa kadan kadan, kowanne mahaluki yau yanayin yayi masa dadi ciki kuwa hadda fahad wanda fitowarsa kenan zuwa shagonsu bayan yataso daga wurin aikin gina gidansa da akeyi sai yanzu yasan lallai magidanta na kokari domin shi duk da ana taimaka masa agida amma yanzu haka account dinshi duk ya kusan yasheshi sai dan abinda ba arasa ba, yana tsaye yana yanka kayan wasu dalibai wadanda zasuyi bikin gamawa wato anko, yana yi yana cewa aransa,

"Danma dai Allah baya hana bawansa hanyar samu amma da ba haka ba sunana sorry..."

Maganar su hamza da yajiyo daga cikin shago itace ta dakatar dashi daga zancen zucin da yakeyi,

"Kayan Prince.... Kayan prince"

Ko bai waiwaya ba yasan husnah suke nufin ta taho, shi sunan nan takaici yake bashi wallahi yarasa yanda zaiyi da husnah, kamar yanda ya tsammata abayanshi ta tsaya tana murmushi murmushi dariya dariya,

"My prince... Sannu da aiki"

Aciki ciki ya amsa kamar koda yaushe,

"Yauwa"

Kallonshi tayi daga sama har kasa,p cap ce akanshi dark blue agaban p cap din anrubuta harrafin p da bakin rubutu,sai bakar t shirt mai dogon hannu wadda aka rubuta prince agaban rigar sannan ga bakin trouser yasaka da bakin takalmi na kamfanin Nike,

"Yau kayi kyau my Prince.."

"Nagode"

"Gobe me zaka ci in dafo maka?"

"Ai kawai ma kibarshi saboda ba lallai infito shago ba"

"Haba ya fahad... Meyasa?"

"Ina zuwa wani wurine, yanzu ma fita zanyi....ina so inje inga half soul"
Chapter 12 · 0% Book details