Sashe 49
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hado mishi tayi cikin plate harda su tumatur da sauran kayan lambu, zama yayi sosai yaci sannan yakoma ya kwanta babu jimawa bacci yayi gaba dashi bai farkaba sai daf da la'asar, yafito tsakar gida domin yin alwala,zama yayi yasa maryam takawo masa ruwan alwala, yana yin alwalar mamuh tazo tana tambayarsa awanne asibitin su Bilkisu suke domin suna son suje dubata yanzu fada mata yayi yakoma falon ayiyah, yana salla yaji tafiyarsu suna yimasa sallama shi kadai aka bari agidan domin harda su maryama aka tafi. Bayan ya idar da salla yasake kwanciya sai lokacin yamika hannu yadauko wayarshi yana dubawa text din husnah na barka da friday yagani sai kuma miss called dinta da nasu bashir, daya bayan daya yarinka bin miss called din yana kira bayan yagama yatashi ya yafita kofar gida yazauna yana jiran dawowarsu ayiyah.
Yafi mintuna talatin zaune awurin sannan suka dawo, maryam na rikeda babban warmer mai kyau,
"Maryam me kika samomin?" Yafada yana kokarin tashi tsaye,
"Surukarka ce tabayar akawo maka wai kaci ka maida jinin jikinka...."
Jin abinda mamuh tafada yasashi yin dariya saboda yazaci wasan da tasaba yimasa yauma tayi, binsu yayi suka shiga cikin gida,ga mamakinsa kuwa sai yaga ashe dagaske ne domin agabansa maryam ta ajiye warmer din tana cewa,
"Ya fahad wai gashi..."
Budewa yayi nan kamshi ya bugeshi mai dadi, farfesun hanta ne cikin warmer din yaji kayan kamshi sai kamshi ne ketashi,
Kallonsu mamuh yayi sannan yakalli maryam yace,
"To kuma ni zaki kawowa ki ajiyewa? Mika musu..."
Dauka tayi takai gabansu mamuh ta ajiye, cikin plate mamuh ta zuba masa ta mika masa,
"Wallahi mamuh wannan yayi yawa... Rage"
"Ba ragewar da za ayi, kaida kabada jini har leda daya da rabi ai dole kaci abubuwan da zasu kara maka jini dannan...."
"Mamuh dazufa da bakya nan wallahi naci zogale dayawa..."
"Saifa ka cinye fahad, dauki maza ina kallonka..."
Dauka yayi yafara ci ita kuma taci gaba da raba nasu, yana ci yana hadawa da ruwa har ya cinye saboda ita hanta akwai cikawa mutum ciki shiyasa yajishi yakoshi over, tashi yayi yafita bayan ya gama yakoma dakinsu, salim yaturawa text yana sanar dashi anjima zai rakashi su dubo Bilkisu, wanka yashiga domin yanzu ya danji karfin jikinsa.
Bayan sallar magrib suka tafi asibitin su uku saboda harda ya abba,dukkaninsu sunsha dogayen kaya, babu kowa adakin sai iya Bilkisu da meenah suna zaune kan gadon Bilkisu na shan tea har lokacin tana sanye da hijabinta, jin sallamarsu yasata sake kasa da kanta bata ko dagoba saboda bata son ganin sun hada ido da fahad saboda tasan yanzu bata da wata martaba a idonsa tunda ashe sadaka aka aura masa ita tasan ba kowane yakitsa wannan abunba sai iyallo saboda dama itace ke cewa zata aurar da ita sadaka, yanzu gashi anja mata reni da wulakanci a idon yaro,
Tana ji su Abba na tambayar yamai jiki suna yimata sannu dakyar ta iya amsawa sakamakon kukan da ke kokarin taho mata, lokacin da taji meenah na gaisawa itada fahad sai taji kamar da biyu yake yin gaisuwar nan ta shareshi bata ko dago ba daga karshe su Abba suka fita suna yimata fatan samun sauki haka itama meenah sai ta tashi tafita yarage su biyu kadai cikin dakin,
"Sannu... Yajikin? Ke daga fada miki gaskiya shine zaki kwanta ciwo...?"
Jin abinda yace yasata dagowa ta zuba masa harara saboda ta tsani ke dinnan kafin ta dauke idonta yarama,
"Ni ai ka kira da matar sadaka ko?"
"To da matar meye? Sadaka aka bani kuma nakarba..."
"Wallahi karya kake yi..."
Nuna kanshi yayi da yatsa,
"Ni kike cewa ina yimiki karya?"
"Ehh din...."
Kafin yayi magana meenah tashigo rikeda waya nan ta mikawa Bilkisu tana cemata,
"Adda labour gashi su elmustapha ne..."
Karba tayi suka fara gaisawa dasu elameen suna yimata ya jiki, bata saurari fahad ba wanda ahankali yace,
"Yarinya kuma sai kin biyani jinina da na baki dan ba kyauta nabayar ba..."
Shima bai sake bi ta kanta ba yayi waje abinshi yabarta da kunar zuciya domin maganganunshi sosai yanzu suke bata mata rai,wayar nan kawai tanayi ne bawai dan tana fuskantar abinda take cewa ba......
*_Ummi Shatu_*
*Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
46****Daren ranar ma haka ta kwana batayi bacciba saboda tsabar bacin rai da damuwa da zarar ta tuno maganganun da ya yayyaba mata sai taji kwalla ta ciko idonta. Washe gari dasafe aka sallameta suka koma gida, suna zuwa tasamu tashiga wanka tafito domin shiryawa kamar tasaka hannu aka tayi ihu haka takeji idan har tatuno da maganganun fahad, ahaka ta daure tashirya tana cikeda damuwa tana gamawa Hindu takawo mata abin karyawa nan ta zauna tasoma dan kurbar ruwan zafi bawai dan tanaso ba amma sauran kayan karyawar ko tabasu batayi ba ahaka Hindu tadawo ta sameta tana rikeda sultan a hannunta,
"Adda mai gado yabaki ci abincin ba? Saifa kin dan daure..."
Jin abinda Hindu tace yasata dagowa ta kalleta da kodaddun idanuwanta wadanda ko kwalli babu,
"Hindu banida apatite abakina wallahi, sam bana jin dadin komai..."
"Duk da haka ki dan daure mana, sannan dan Allah ki gyara fuskarki kisaka koda powder ne da kwalli... Amma ya fahad yazo yaganki ahakan nan ai akwai matsala..."
Harara ta watsawa hindu sannan tamaida kallonta kan sultan wanda ke miko mata hannu yana yimata gwaranci, mika hannu tayi zata karbeshi amma Hindu taki sakinshi tana cewa,
"Kai bari kar kaje ka karasa mana addarmu kaga dazun nan tadawo daga gadon asibiti..."
Murmushi Bilkisu tayi ta karbeshi sakamakon kukan da yafara yi, ita kuma haka Allah ya dorawa yaran kannenta kaunarta duk sun shaku dasu babu wanda yake yimata kiywa,
"Dan Allah adda labour ki daure kici abincin nan kar yayi sanyi sannan ki gyara fuskarki saboda tsaro..."
"Ke hindu idanma fa akan fahad kiketa wannan damun nawa bazan yiba..."
"A'a wallahi Adda labour ni basaboda shi bane kawai dai ai kinga idan kika saka kwallin fuskarki zatafi fitowa amma yanzu Allah baki ganki ba duk kin canja kin sake fadawa..."
Bata sake yin magana ba ta jawo abincin gabanta ta bude tafara ci tanayi tana bawa sultan, saida tagama tsaf ta zauna gaban mirror tana shafa powder sai tajiyo sallamar khulsum, tana jiyosu sunayi itada hindu atsakar gida hindu nacewa bazasu amshi uzurinta ba tunda bataje asibiti ba saida suka dawo gida. Anan gaban mirrior din khulsum tashigo ta sameta tana zizira kwalli,
"Labour patient har an warke anfara coda ado za atari oga?"
Harararta Bilkisu tayi ta taso daga gaban mirror din tadawo gefen gado kusa da khulsum,
"Zaki fara ko? Allah yakawo ki ai kuma..."
"Ah to ai gaskiya ce anwarke mana me kuma yayi saura banda akoma bakin daga..."
"Sai kiyi kuma..."
"Yawwa wai ke yaushe zaki tare ne? Allah kinga labour ki tare tun kafin abinnan ya bayyana dan wallahi ni harga Allah ban yarda da wannan ciwo ciwon nakiba.... Laulayi kika fara ko?"
"Wai ke meyasa ba a abun arziki dake ne? Ni dan Allah kinga karki bata min rai..."
"To yi hakuri, sorry kinga jiya banzo asibiti na dubaki ba ko? Wallahi khalifa ne nima baida lafiya... Amma yaji sauki yau"
"Babu komai ai da kinyi zamanki ma kin kula dashi"
"Ai yaji sauki yana can tare da babanshi"
"Allah yakara masa lafiya..."
"Amin... Yawwa wai mutuniyar kin kuwa taba gwada hadin nan dana turo miki rannan?"
Dariya Bilkisu tayi saboda ita wallahi ma sai yanzu tatuna da sakon da khulsum din ta turo mata,
"Madam kedai kije kiyi tayi amma ni wallahi bazan yiba..."
Kallonta khulsum tayi cikin jin haushi,
"Allah yashiryeki labour maza dai ki tsaya kallon ruwa kwado yayi miki kafa wallahi idan baki kama mijinki a hannunba... Hmmm zaki ganene"
"Toh Anty..."
Dariya khulsum tayi sannan tayi kasa da murya tace,
"Wai dan Allah laulayinne da gaske?"
"Ban saniba..."
Kafin khulsum tasake magana suka jiyo sallamar fahad atsakar gida amma ahankali kamar wani marar gaskiya, mikewa khulsum tayi tana cewa,
"Bari na kwashi yanmatan kafafuwana inbarku kusha morning show dinku, ga wata gumba idan kinaso sharp sharp ce wallahi...."
"Banaso akai gaba..."
"Kedai kika sani wallahi, ni sai anjima"
Mikewa tayi ta kwanta bayan fitar khulsum tana jiyo lokacin da khulsum din suke gaisawa da fahad atsakar gida mintuna kadan tsakani taji shigowarsa ta hanyar bude kofa da yayi bata ko motsa ba ayadda take bare ta dago ta kalleshi, daga dan nesa yatsaya yana kallonta, riga da skirt na leshi tasaka wanda aka yiwa simple style yayi dass ajikinta, dakin gaba dayanshi sanyayyen kamshine ke tashi cikinsa,
"Yajiki......?" Yafada yana murmushin da bazata ganeba,
"Da sauki" ta amsa kamar bataso domin badan shi din mai jin magana ce komai kankantarta ba da bazai jiba,
"Dama nazo dubaki ne, hope kinji dadin jinina dake jikinki?"
Juyowa tayi afusace ta harareshi,
"Dadinta ma dai banice nanemi da kabani jinin ba, badanma lokacin da aka saka min bana cikin hayyacina ba da me zanyi da jininka.... Wa yasani ma ko guntun sikila ne..."
Murmushi yayi yana kallonta yasan dai maganar dayace wannan matar sadakar da yakirata dashi ne yaketa sosa mata zuciya har take neman hanyar mayar masa da martani,
"Kiyi hakuri bani na kar zomon ba rataya aka bani, kuma ratayar ma ban karba ba......"
"Idanma ka karba idanma baka karba ba ruwanka, sannan da kake cewa sadaka aka aura maka ni ai yanzu ma kanada damar da zakace kafasa... Tunda ba adole"
"Akan me zance nafasa? Ai narigada na karba"
"Duk da ka karba ai kasan hanya mafi sauki wacce tadace da zakabi ka mayar da sadakar...."
Tabe baki yayi yasamu kan bedside drewar yazauna yadora kafa daya akan daya,
"Ni yanzu ba wannan ne yakawo ni ba inada abin yi dubiyace ta kawo ni..."
Wani kallo tayi masa yana sanye da kananan kaya amma yadora lab coat asama kafarshi rufe cikin bakar safa, takula akwai shi da saka safa akafa sai kace wani marar lafiya,
"Yanda kake da abinyi haka nima nake dashi, nidai kawai ka datse igiyar auren nan kowa ya huta..."
"Ban ganeba.... Wai kina nufin ni fahad na sakeki? Idan hakan kikeso zan yimiki amma abisa sharadi guda daya..."
Yafi mintuna talatin zaune awurin sannan suka dawo, maryam na rikeda babban warmer mai kyau,
"Maryam me kika samomin?" Yafada yana kokarin tashi tsaye,
"Surukarka ce tabayar akawo maka wai kaci ka maida jinin jikinka...."
Jin abinda mamuh tafada yasashi yin dariya saboda yazaci wasan da tasaba yimasa yauma tayi, binsu yayi suka shiga cikin gida,ga mamakinsa kuwa sai yaga ashe dagaske ne domin agabansa maryam ta ajiye warmer din tana cewa,
"Ya fahad wai gashi..."
Budewa yayi nan kamshi ya bugeshi mai dadi, farfesun hanta ne cikin warmer din yaji kayan kamshi sai kamshi ne ketashi,
Kallonsu mamuh yayi sannan yakalli maryam yace,
"To kuma ni zaki kawowa ki ajiyewa? Mika musu..."
Dauka tayi takai gabansu mamuh ta ajiye, cikin plate mamuh ta zuba masa ta mika masa,
"Wallahi mamuh wannan yayi yawa... Rage"
"Ba ragewar da za ayi, kaida kabada jini har leda daya da rabi ai dole kaci abubuwan da zasu kara maka jini dannan...."
"Mamuh dazufa da bakya nan wallahi naci zogale dayawa..."
"Saifa ka cinye fahad, dauki maza ina kallonka..."
Dauka yayi yafara ci ita kuma taci gaba da raba nasu, yana ci yana hadawa da ruwa har ya cinye saboda ita hanta akwai cikawa mutum ciki shiyasa yajishi yakoshi over, tashi yayi yafita bayan ya gama yakoma dakinsu, salim yaturawa text yana sanar dashi anjima zai rakashi su dubo Bilkisu, wanka yashiga domin yanzu ya danji karfin jikinsa.
Bayan sallar magrib suka tafi asibitin su uku saboda harda ya abba,dukkaninsu sunsha dogayen kaya, babu kowa adakin sai iya Bilkisu da meenah suna zaune kan gadon Bilkisu na shan tea har lokacin tana sanye da hijabinta, jin sallamarsu yasata sake kasa da kanta bata ko dagoba saboda bata son ganin sun hada ido da fahad saboda tasan yanzu bata da wata martaba a idonsa tunda ashe sadaka aka aura masa ita tasan ba kowane yakitsa wannan abunba sai iyallo saboda dama itace ke cewa zata aurar da ita sadaka, yanzu gashi anja mata reni da wulakanci a idon yaro,
Tana ji su Abba na tambayar yamai jiki suna yimata sannu dakyar ta iya amsawa sakamakon kukan da ke kokarin taho mata, lokacin da taji meenah na gaisawa itada fahad sai taji kamar da biyu yake yin gaisuwar nan ta shareshi bata ko dago ba daga karshe su Abba suka fita suna yimata fatan samun sauki haka itama meenah sai ta tashi tafita yarage su biyu kadai cikin dakin,
"Sannu... Yajikin? Ke daga fada miki gaskiya shine zaki kwanta ciwo...?"
Jin abinda yace yasata dagowa ta zuba masa harara saboda ta tsani ke dinnan kafin ta dauke idonta yarama,
"Ni ai ka kira da matar sadaka ko?"
"To da matar meye? Sadaka aka bani kuma nakarba..."
"Wallahi karya kake yi..."
Nuna kanshi yayi da yatsa,
"Ni kike cewa ina yimiki karya?"
"Ehh din...."
Kafin yayi magana meenah tashigo rikeda waya nan ta mikawa Bilkisu tana cemata,
"Adda labour gashi su elmustapha ne..."
Karba tayi suka fara gaisawa dasu elameen suna yimata ya jiki, bata saurari fahad ba wanda ahankali yace,
"Yarinya kuma sai kin biyani jinina da na baki dan ba kyauta nabayar ba..."
Shima bai sake bi ta kanta ba yayi waje abinshi yabarta da kunar zuciya domin maganganunshi sosai yanzu suke bata mata rai,wayar nan kawai tanayi ne bawai dan tana fuskantar abinda take cewa ba......
*_Ummi Shatu_*
*Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
46****Daren ranar ma haka ta kwana batayi bacciba saboda tsabar bacin rai da damuwa da zarar ta tuno maganganun da ya yayyaba mata sai taji kwalla ta ciko idonta. Washe gari dasafe aka sallameta suka koma gida, suna zuwa tasamu tashiga wanka tafito domin shiryawa kamar tasaka hannu aka tayi ihu haka takeji idan har tatuno da maganganun fahad, ahaka ta daure tashirya tana cikeda damuwa tana gamawa Hindu takawo mata abin karyawa nan ta zauna tasoma dan kurbar ruwan zafi bawai dan tanaso ba amma sauran kayan karyawar ko tabasu batayi ba ahaka Hindu tadawo ta sameta tana rikeda sultan a hannunta,
"Adda mai gado yabaki ci abincin ba? Saifa kin dan daure..."
Jin abinda Hindu tace yasata dagowa ta kalleta da kodaddun idanuwanta wadanda ko kwalli babu,
"Hindu banida apatite abakina wallahi, sam bana jin dadin komai..."
"Duk da haka ki dan daure mana, sannan dan Allah ki gyara fuskarki kisaka koda powder ne da kwalli... Amma ya fahad yazo yaganki ahakan nan ai akwai matsala..."
Harara ta watsawa hindu sannan tamaida kallonta kan sultan wanda ke miko mata hannu yana yimata gwaranci, mika hannu tayi zata karbeshi amma Hindu taki sakinshi tana cewa,
"Kai bari kar kaje ka karasa mana addarmu kaga dazun nan tadawo daga gadon asibiti..."
Murmushi Bilkisu tayi ta karbeshi sakamakon kukan da yafara yi, ita kuma haka Allah ya dorawa yaran kannenta kaunarta duk sun shaku dasu babu wanda yake yimata kiywa,
"Dan Allah adda labour ki daure kici abincin nan kar yayi sanyi sannan ki gyara fuskarki saboda tsaro..."
"Ke hindu idanma fa akan fahad kiketa wannan damun nawa bazan yiba..."
"A'a wallahi Adda labour ni basaboda shi bane kawai dai ai kinga idan kika saka kwallin fuskarki zatafi fitowa amma yanzu Allah baki ganki ba duk kin canja kin sake fadawa..."
Bata sake yin magana ba ta jawo abincin gabanta ta bude tafara ci tanayi tana bawa sultan, saida tagama tsaf ta zauna gaban mirror tana shafa powder sai tajiyo sallamar khulsum, tana jiyosu sunayi itada hindu atsakar gida hindu nacewa bazasu amshi uzurinta ba tunda bataje asibiti ba saida suka dawo gida. Anan gaban mirrior din khulsum tashigo ta sameta tana zizira kwalli,
"Labour patient har an warke anfara coda ado za atari oga?"
Harararta Bilkisu tayi ta taso daga gaban mirror din tadawo gefen gado kusa da khulsum,
"Zaki fara ko? Allah yakawo ki ai kuma..."
"Ah to ai gaskiya ce anwarke mana me kuma yayi saura banda akoma bakin daga..."
"Sai kiyi kuma..."
"Yawwa wai ke yaushe zaki tare ne? Allah kinga labour ki tare tun kafin abinnan ya bayyana dan wallahi ni harga Allah ban yarda da wannan ciwo ciwon nakiba.... Laulayi kika fara ko?"
"Wai ke meyasa ba a abun arziki dake ne? Ni dan Allah kinga karki bata min rai..."
"To yi hakuri, sorry kinga jiya banzo asibiti na dubaki ba ko? Wallahi khalifa ne nima baida lafiya... Amma yaji sauki yau"
"Babu komai ai da kinyi zamanki ma kin kula dashi"
"Ai yaji sauki yana can tare da babanshi"
"Allah yakara masa lafiya..."
"Amin... Yawwa wai mutuniyar kin kuwa taba gwada hadin nan dana turo miki rannan?"
Dariya Bilkisu tayi saboda ita wallahi ma sai yanzu tatuna da sakon da khulsum din ta turo mata,
"Madam kedai kije kiyi tayi amma ni wallahi bazan yiba..."
Kallonta khulsum tayi cikin jin haushi,
"Allah yashiryeki labour maza dai ki tsaya kallon ruwa kwado yayi miki kafa wallahi idan baki kama mijinki a hannunba... Hmmm zaki ganene"
"Toh Anty..."
Dariya khulsum tayi sannan tayi kasa da murya tace,
"Wai dan Allah laulayinne da gaske?"
"Ban saniba..."
Kafin khulsum tasake magana suka jiyo sallamar fahad atsakar gida amma ahankali kamar wani marar gaskiya, mikewa khulsum tayi tana cewa,
"Bari na kwashi yanmatan kafafuwana inbarku kusha morning show dinku, ga wata gumba idan kinaso sharp sharp ce wallahi...."
"Banaso akai gaba..."
"Kedai kika sani wallahi, ni sai anjima"
Mikewa tayi ta kwanta bayan fitar khulsum tana jiyo lokacin da khulsum din suke gaisawa da fahad atsakar gida mintuna kadan tsakani taji shigowarsa ta hanyar bude kofa da yayi bata ko motsa ba ayadda take bare ta dago ta kalleshi, daga dan nesa yatsaya yana kallonta, riga da skirt na leshi tasaka wanda aka yiwa simple style yayi dass ajikinta, dakin gaba dayanshi sanyayyen kamshine ke tashi cikinsa,
"Yajiki......?" Yafada yana murmushin da bazata ganeba,
"Da sauki" ta amsa kamar bataso domin badan shi din mai jin magana ce komai kankantarta ba da bazai jiba,
"Dama nazo dubaki ne, hope kinji dadin jinina dake jikinki?"
Juyowa tayi afusace ta harareshi,
"Dadinta ma dai banice nanemi da kabani jinin ba, badanma lokacin da aka saka min bana cikin hayyacina ba da me zanyi da jininka.... Wa yasani ma ko guntun sikila ne..."
Murmushi yayi yana kallonta yasan dai maganar dayace wannan matar sadakar da yakirata dashi ne yaketa sosa mata zuciya har take neman hanyar mayar masa da martani,
"Kiyi hakuri bani na kar zomon ba rataya aka bani, kuma ratayar ma ban karba ba......"
"Idanma ka karba idanma baka karba ba ruwanka, sannan da kake cewa sadaka aka aura maka ni ai yanzu ma kanada damar da zakace kafasa... Tunda ba adole"
"Akan me zance nafasa? Ai narigada na karba"
"Duk da ka karba ai kasan hanya mafi sauki wacce tadace da zakabi ka mayar da sadakar...."
Tabe baki yayi yasamu kan bedside drewar yazauna yadora kafa daya akan daya,
"Ni yanzu ba wannan ne yakawo ni ba inada abin yi dubiyace ta kawo ni..."
Wani kallo tayi masa yana sanye da kananan kaya amma yadora lab coat asama kafarshi rufe cikin bakar safa, takula akwai shi da saka safa akafa sai kace wani marar lafiya,
"Yanda kake da abinyi haka nima nake dashi, nidai kawai ka datse igiyar auren nan kowa ya huta..."
"Ban ganeba.... Wai kina nufin ni fahad na sakeki? Idan hakan kikeso zan yimiki amma abisa sharadi guda daya..."