Sashe 8
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dariya sukayi gaba daya nan suka cigaba da hirarsu kamar abokai dama ko tsaye abban bawani fin fahad yayiba haka suka taso tare kamar twins, wannan hirarce ta daukewa fahad hankali dan kafin su farga har 12 da rabi takusa, tashi Abba yayi yanufi toilet nan fahad yasa pillow yatoshe kunnenshi lokacin da yaji kofar tafara kara kiiiiyyyyyyyy, Abba na fitowa yakashe wutar dakin duk da haka saida fahad yakunna light awayarshi sannan ya iya bacci.
***
Su Bilkisu yau zasu gama biki domin kuwa yau za a mika amare gidansu, tun safe Bilkisu take tattara musu sauran kayayyakinsu da ba akai ba kafin kace me gida yacika da yan kai amare ita kam Bilkisu batayi niyyar zuwaba amma khulsum ta matsa sai sunje domin saurayinta zaizo yakaisu, ana yin sallar isha'i akayi haramar kaisu saida aka gama zagawa dasu wurin iyaye sukayi musu fada sannan aka tafi kaisu gidajensu. Hudah aka fara rakawa unguwar jan bulo sannan aka raka Mina sharada, duk inda sukaje Bilkisu bata shiga domin tasan gidajen asalima kayan ciki sune suka jera. Misalin karfe goma suka dawo daga rakiyar amaren, yanzu kam yan biki saura kadan domin dama yau duk wasu suka tattafi sai najiki irinsu iyallo da yan uwan amma harda mahaifiyarta hajjo, ba karamin dadi tajiba ganin dakinta fayau babu kowa nan ta dauko hudah bayan tayi mata wanka itama tayi tabi lafiyar gado domin maama na can wurinsu amma acan zata kwana. Wani lafiyayyen bacci tayi domin tunda ta kwanta bata motsa ba saida 6 nasafe tayi nan tatashi tayi salla tasake komawa har 9 sama sama tajiyo muryar hajjo kakarta tana fadin,
"Ohh maigado ai sai asaceki dake da katifar da kike kai batare da kin saniba, kowa yatashi banda ke"
"Ai dole tayi bacci hajjo wallahi tagaji dayawa tasha zirga zirga" Inji maama wadanda suka shirya tsaf domin zuwa gidan amare suda su iyallo, sai bayan sun tafi da dadewa sannan bilkisu tatashi ganin babu hudah akusa da ita ya tabbatar mata da tabi tsohuwarta, wanka tayi ta caba kwalliya tasha gown ta atamfa dark blue, wurin ammah ta nufa wacce ke can dakinta ita da baki yan Allah sanya alkhairi, gaisawa dasu kawai sukayi tafito tawuce kitchen koko da kosai ne akayi na karin kumallo sai dankali da kwai wanda aka soyawa abba, dankali da kwan ta diba ta zauna tayi nak sannan tafito sai lokacin wayoyinta suka fado mata dan rabonta dasu tun ranar dinner da daddare, daki takoma ta daukosu gaba daya ta kunna su nan sakonni suka yita shigowa rututu kusan 10 amma aciki guda biyu na hamood ne wanda ke sanar da ita zai dawo Nigeria jiya idan yazo zai kirata dan Allah tazama mai rike masa alkawari domin itace matar aurenshi, dariya tayi tana jin farin ciki yana ratsata, sauran massages din kuwa duk na fahad ne wanda bata da masaniyar cewa shine, daga karshe ajiye wayoyin tayi ta dauko laptop dinta tayi downloading din wani Indian series mai suna Rangarasiya ita kam Allah yadora mata kaunar Indian film tana tsaka da kallo khulsum tayi sallama,
"Au ke baki tafi gidan amaren ba?"
Murmushi tayi,
"Me zanje inyi musu kuma"
"Ai shikenan, bani ruwa insha"
Kawar da laptop din tayi daga gabanta ta mike ta dauko mata ruwan ta miko mata,
"Ya labarin mutumin ne?"
"Yataho ai may be ma yanzu ma yasauka"
"Ahh lallai abun yazo amarya"
Shiru bilkisu tayi saboda tasan kawai neman magana ne irin na khulsum.
Dasu iyallo sukaje gidajen amaren kowacce aciki babu wacce batayi cikiyar bilkisu ba amma babu ita sai maama itace ma ke cemusu kila da yamma bilkisun zataje musu nan ta gyaggyara musu abubuwan da yadace sannan suka tarkato suka dawo iyallo dai sai sakawa danta albarka take kan irin rawar daya taka wurin zubawa yayansa kayan daki nagani na fada. Har suka dawo gida bilkisu natare da khulsum suna kallo saida rana tafara yi sannan tatafi domin tanada karanta labaran rana.
Da yamma dukkan baki suka tafi amma banda iyallo ita kam tana nan Allah kadai yasan ranar tafiyarta, haduwa sukayi maama da bilkisu suka gyare gidan tsaf yadawo yanda yake da, suna kammalawa Abba na dawowa daga garko dama duk karshen wata yake zuwa ya duba garin nasa a matsayinsa na hakimin garin manya manyan kaji da zabbi aka shigo dasu sai kwan zabbi cikin bokitin roba dama duk ranar da yaje haka yake dawowa da kaya niki niki domin jama'ar kauye akwai kara banda su yalo, gwaiba da sauransu, nan dai su bilkisu suka shiga aiki baji ba gani ita dai iyallo tana zaune tsakar gida kan tabarma ta kishingida tana ganin mai shiga da mai fita domin mutane sunata zuwama amma Allah yasanya alkhairi. Sai dare maama ta tattara tatafi bayan mijinta yazo daukarta, bilkisu rufe kofarta tayi tai kwanciyarta nan taga text din minah da na Hindu kamar hadin baki duk suna yimata korafin rashin zuwanta murmushi kawai tayi ta ajiye wayar tafada kogin tunani.
Washe gari bata tashi dawuri ba sanin acikin hutu take ba aiki zata fita ba, koda tafito tuni har anhada abin karyawa kowa yaci sai nata kadai dauka tayi takoma dakinta taci tana kammalawa kiran abba yashigo wayarta cikeda ladabi ta daga nan yace taje yana kiranta, hijab ta dauka tafita jikinta na bata lallai akwai abinda ke faruwa bare iyallo trouble maker tana nan.....
*_Ummi Shatu_*
© _HASKE WRITERS ASSO._
*KAMAR DA WASA...!*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*Dan girman Allah na rokeku kudaina fitar min da book, ku kuma wadanda aka turowa kuji tsoron Allah idan baki siyaba karki karanta.*
*9*
***Falon tsit sai fadan iyallo dake tashi duk tabi ta cikashi da hayagaga,
"Haba yarinya tadade da kawowa misali amma kun zuba mata ido sai dai garin Allah idan yawaye tayi wanka ta saba jaka tatafi wani wai aikin gwamnati, to wallahi ya isa haka sam bazan lamunta ba kannenta duk gasu can adaki amma ita tana gida, wannan ai ba dabara bace karatunnan tayi ta dada tayi ta dada wai shin karshen biro da takarda zata gani? To wallahi wata biyu kacal na bata ta fito da miji idan ba hakaba ga dan uwanta nan mudan ai tushensu daya sai a aura mata shi...."
Zama bilkisu tayi tana sauraron fadan iyallo har saida tayi shiru sannan Abba yayi magana yabata hakuri yace insha Allah za ayi yadda tace, ita kam amma shiru tayi batace komai ba har akayi aka gama. Juyawa Abba yayi ga bilkisu yace,
"Uwata kinji abinda hajiya tafada lallai lallai kifito da miji cikin wata biyu ayi miki aure"
Daga kai tayi yayinda iyallo ta bude murya,
"Yawwa gaya mata da kyau, wannan yawon karatu ya isa haka"
Sallamarta abba yayi tatashi tatafi takoma dakinta ta zauna, sam bata sa abin aranta ba domin karma ya dameta taci gaba da harkarta. Kwana biyu da faruwar hakan iyallo ta tattara takoma garko kuma aranar maama tazo nan bilkisu take bata labarin abinda yafaru,
"Iyallo jaraba, ai wallahi adda labour da kin wanketa tas kafin tatafi"
"Ke maama kar nakara jin haka, ba mahaifiyar babanku bace? Itama fa tana da iko daku infada muku gaskiya, kedai mai gado kawai kiyi abinda tace ki fidda miji kiyi auren nan kihuta muma mu huta da maganganunsu"
Bilkisu dai batace komai ba domin har yau bata samu hamood ba shima kuma bai kirata ba, sai yanzu hankalinta yasoma tashi ganin ankusa wata daya domin har hutunta yakare takoma aiki, agefe daya kuma iyallo kullum cikin bugowa abba waya take tana kara jaddada masa maganar auren mudan da bilkisu, ita kuwa bilkisu ji take akan ta auri ya mudan gara ta auri koma waye.
Wasa wasa lokaci sai tafiya yake amma shiru babu labarin hamood duk ta inda take tunanin zata sameshi tarasa domin daga Facebook dinshi har Twitter da instagram duk shiru, yanzu kam tashiga mutukar damuwa gashi wanda ke damunta batare da tasan ko wayeba bai fasaba kullum yake kiranta kuma yaturo mata text ganin wankin hula na shirin kaita dare yasata nemarwa kanta mafita. Daren ranar kwana tayi batayi bacciba tanata sakawa da kwancewa daga karshe shawarar khulsum ta fado mata inda take cemata,
"Ni kawai ina ganin ki baiwa bawan Allahn nan dama wallahi yafito ya bayyana miki kansa idan yayi miki kawai ki aureshi ki manta da wani hamood tunda har yanzu babu wani labari game dashi...."
Lumshe idanuwanta tayi bayan ta dafe kanta dake sara mata, tabbas yazama dole ta dauki shawarar khulsum mutukar tana son hakanta ya cimma ruwa,wayarta ta jawo ta duba agogo karfe 2 da yan mintuna na dare, text ta soma rubutawa wannan guy din da har yau bata san ko wayeba, bayan yanuna mata yatafi ne ta kashe wayar gaba daya tana jiran zuwa gobe sai ayita takare.
***
Ga fahad kuwa abun ba sauki domin har gobe bilkisu ce zabinsa duk da yasan tayi masa nisa kokuma tafi karfinshi amma dayake ita zuciya babu ruwanta da duk wadannan abubuwan haka ta nace da soyayyarta, kullum aikin kenan tura mata love massages gashi tun bayan bikin kannenta bai sake ganinta ba dan program dinma da takeyi yanzu shiru sai wata bakuwar murya ce keyi gaba daya yarasa gane abinda ke faruwa. Bayan yadawo daga sallar asubah kamar yadda yasaba yazauna saman katifa yajawo wayarshi da niyyar yakirata ya tadata tayi salla yana kunna wayar yaga massage dinta jikinshi na rawa yabude domin wannan shine karo nafarko da ta taba turo masa sakon karta kwana, da sauri da sauri yafara karanta sakon nata kamar haka;
_Amincin Allah ya tabbata agareka, dan Allah idan har bazaka damuba ina son ganinka gobe agidanmu akwai muhimmiyar maganar da nake so mu tattauna, nagode._
Ajiyar zuciya yasauke yana jin tsoro yana shigarsa, tambayar zuciyarsa yafara yi to yanzu idan taganshi tace baiyi mata ba kokuma tace kar yasake kulata fa? Yajima zaune cikin rashin sanin abinyi daga karshe yabarwa Allah ya kwanta ya tura mata da reply,
_Sarauniyar mata ina fata kin tashi cikin aminci da koshin lafiya, insha Allah yau zan amsa kiranki batare da jinkiri ba amma inaso kibani time da kanki kuma kibani address din saboda ban san gidan nakuba, masoyinki ahar kullum....!_
Daga haka yatura mata ya ajiye wayar yana addu'ar samun nasara acikin wannan al'amari.
***
Su Bilkisu yau zasu gama biki domin kuwa yau za a mika amare gidansu, tun safe Bilkisu take tattara musu sauran kayayyakinsu da ba akai ba kafin kace me gida yacika da yan kai amare ita kam Bilkisu batayi niyyar zuwaba amma khulsum ta matsa sai sunje domin saurayinta zaizo yakaisu, ana yin sallar isha'i akayi haramar kaisu saida aka gama zagawa dasu wurin iyaye sukayi musu fada sannan aka tafi kaisu gidajensu. Hudah aka fara rakawa unguwar jan bulo sannan aka raka Mina sharada, duk inda sukaje Bilkisu bata shiga domin tasan gidajen asalima kayan ciki sune suka jera. Misalin karfe goma suka dawo daga rakiyar amaren, yanzu kam yan biki saura kadan domin dama yau duk wasu suka tattafi sai najiki irinsu iyallo da yan uwan amma harda mahaifiyarta hajjo, ba karamin dadi tajiba ganin dakinta fayau babu kowa nan ta dauko hudah bayan tayi mata wanka itama tayi tabi lafiyar gado domin maama na can wurinsu amma acan zata kwana. Wani lafiyayyen bacci tayi domin tunda ta kwanta bata motsa ba saida 6 nasafe tayi nan tatashi tayi salla tasake komawa har 9 sama sama tajiyo muryar hajjo kakarta tana fadin,
"Ohh maigado ai sai asaceki dake da katifar da kike kai batare da kin saniba, kowa yatashi banda ke"
"Ai dole tayi bacci hajjo wallahi tagaji dayawa tasha zirga zirga" Inji maama wadanda suka shirya tsaf domin zuwa gidan amare suda su iyallo, sai bayan sun tafi da dadewa sannan bilkisu tatashi ganin babu hudah akusa da ita ya tabbatar mata da tabi tsohuwarta, wanka tayi ta caba kwalliya tasha gown ta atamfa dark blue, wurin ammah ta nufa wacce ke can dakinta ita da baki yan Allah sanya alkhairi, gaisawa dasu kawai sukayi tafito tawuce kitchen koko da kosai ne akayi na karin kumallo sai dankali da kwai wanda aka soyawa abba, dankali da kwan ta diba ta zauna tayi nak sannan tafito sai lokacin wayoyinta suka fado mata dan rabonta dasu tun ranar dinner da daddare, daki takoma ta daukosu gaba daya ta kunna su nan sakonni suka yita shigowa rututu kusan 10 amma aciki guda biyu na hamood ne wanda ke sanar da ita zai dawo Nigeria jiya idan yazo zai kirata dan Allah tazama mai rike masa alkawari domin itace matar aurenshi, dariya tayi tana jin farin ciki yana ratsata, sauran massages din kuwa duk na fahad ne wanda bata da masaniyar cewa shine, daga karshe ajiye wayoyin tayi ta dauko laptop dinta tayi downloading din wani Indian series mai suna Rangarasiya ita kam Allah yadora mata kaunar Indian film tana tsaka da kallo khulsum tayi sallama,
"Au ke baki tafi gidan amaren ba?"
Murmushi tayi,
"Me zanje inyi musu kuma"
"Ai shikenan, bani ruwa insha"
Kawar da laptop din tayi daga gabanta ta mike ta dauko mata ruwan ta miko mata,
"Ya labarin mutumin ne?"
"Yataho ai may be ma yanzu ma yasauka"
"Ahh lallai abun yazo amarya"
Shiru bilkisu tayi saboda tasan kawai neman magana ne irin na khulsum.
Dasu iyallo sukaje gidajen amaren kowacce aciki babu wacce batayi cikiyar bilkisu ba amma babu ita sai maama itace ma ke cemusu kila da yamma bilkisun zataje musu nan ta gyaggyara musu abubuwan da yadace sannan suka tarkato suka dawo iyallo dai sai sakawa danta albarka take kan irin rawar daya taka wurin zubawa yayansa kayan daki nagani na fada. Har suka dawo gida bilkisu natare da khulsum suna kallo saida rana tafara yi sannan tatafi domin tanada karanta labaran rana.
Da yamma dukkan baki suka tafi amma banda iyallo ita kam tana nan Allah kadai yasan ranar tafiyarta, haduwa sukayi maama da bilkisu suka gyare gidan tsaf yadawo yanda yake da, suna kammalawa Abba na dawowa daga garko dama duk karshen wata yake zuwa ya duba garin nasa a matsayinsa na hakimin garin manya manyan kaji da zabbi aka shigo dasu sai kwan zabbi cikin bokitin roba dama duk ranar da yaje haka yake dawowa da kaya niki niki domin jama'ar kauye akwai kara banda su yalo, gwaiba da sauransu, nan dai su bilkisu suka shiga aiki baji ba gani ita dai iyallo tana zaune tsakar gida kan tabarma ta kishingida tana ganin mai shiga da mai fita domin mutane sunata zuwama amma Allah yasanya alkhairi. Sai dare maama ta tattara tatafi bayan mijinta yazo daukarta, bilkisu rufe kofarta tayi tai kwanciyarta nan taga text din minah da na Hindu kamar hadin baki duk suna yimata korafin rashin zuwanta murmushi kawai tayi ta ajiye wayar tafada kogin tunani.
Washe gari bata tashi dawuri ba sanin acikin hutu take ba aiki zata fita ba, koda tafito tuni har anhada abin karyawa kowa yaci sai nata kadai dauka tayi takoma dakinta taci tana kammalawa kiran abba yashigo wayarta cikeda ladabi ta daga nan yace taje yana kiranta, hijab ta dauka tafita jikinta na bata lallai akwai abinda ke faruwa bare iyallo trouble maker tana nan.....
*_Ummi Shatu_*
© _HASKE WRITERS ASSO._
*KAMAR DA WASA...!*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*Dan girman Allah na rokeku kudaina fitar min da book, ku kuma wadanda aka turowa kuji tsoron Allah idan baki siyaba karki karanta.*
*9*
***Falon tsit sai fadan iyallo dake tashi duk tabi ta cikashi da hayagaga,
"Haba yarinya tadade da kawowa misali amma kun zuba mata ido sai dai garin Allah idan yawaye tayi wanka ta saba jaka tatafi wani wai aikin gwamnati, to wallahi ya isa haka sam bazan lamunta ba kannenta duk gasu can adaki amma ita tana gida, wannan ai ba dabara bace karatunnan tayi ta dada tayi ta dada wai shin karshen biro da takarda zata gani? To wallahi wata biyu kacal na bata ta fito da miji idan ba hakaba ga dan uwanta nan mudan ai tushensu daya sai a aura mata shi...."
Zama bilkisu tayi tana sauraron fadan iyallo har saida tayi shiru sannan Abba yayi magana yabata hakuri yace insha Allah za ayi yadda tace, ita kam amma shiru tayi batace komai ba har akayi aka gama. Juyawa Abba yayi ga bilkisu yace,
"Uwata kinji abinda hajiya tafada lallai lallai kifito da miji cikin wata biyu ayi miki aure"
Daga kai tayi yayinda iyallo ta bude murya,
"Yawwa gaya mata da kyau, wannan yawon karatu ya isa haka"
Sallamarta abba yayi tatashi tatafi takoma dakinta ta zauna, sam bata sa abin aranta ba domin karma ya dameta taci gaba da harkarta. Kwana biyu da faruwar hakan iyallo ta tattara takoma garko kuma aranar maama tazo nan bilkisu take bata labarin abinda yafaru,
"Iyallo jaraba, ai wallahi adda labour da kin wanketa tas kafin tatafi"
"Ke maama kar nakara jin haka, ba mahaifiyar babanku bace? Itama fa tana da iko daku infada muku gaskiya, kedai mai gado kawai kiyi abinda tace ki fidda miji kiyi auren nan kihuta muma mu huta da maganganunsu"
Bilkisu dai batace komai ba domin har yau bata samu hamood ba shima kuma bai kirata ba, sai yanzu hankalinta yasoma tashi ganin ankusa wata daya domin har hutunta yakare takoma aiki, agefe daya kuma iyallo kullum cikin bugowa abba waya take tana kara jaddada masa maganar auren mudan da bilkisu, ita kuwa bilkisu ji take akan ta auri ya mudan gara ta auri koma waye.
Wasa wasa lokaci sai tafiya yake amma shiru babu labarin hamood duk ta inda take tunanin zata sameshi tarasa domin daga Facebook dinshi har Twitter da instagram duk shiru, yanzu kam tashiga mutukar damuwa gashi wanda ke damunta batare da tasan ko wayeba bai fasaba kullum yake kiranta kuma yaturo mata text ganin wankin hula na shirin kaita dare yasata nemarwa kanta mafita. Daren ranar kwana tayi batayi bacciba tanata sakawa da kwancewa daga karshe shawarar khulsum ta fado mata inda take cemata,
"Ni kawai ina ganin ki baiwa bawan Allahn nan dama wallahi yafito ya bayyana miki kansa idan yayi miki kawai ki aureshi ki manta da wani hamood tunda har yanzu babu wani labari game dashi...."
Lumshe idanuwanta tayi bayan ta dafe kanta dake sara mata, tabbas yazama dole ta dauki shawarar khulsum mutukar tana son hakanta ya cimma ruwa,wayarta ta jawo ta duba agogo karfe 2 da yan mintuna na dare, text ta soma rubutawa wannan guy din da har yau bata san ko wayeba, bayan yanuna mata yatafi ne ta kashe wayar gaba daya tana jiran zuwa gobe sai ayita takare.
***
Ga fahad kuwa abun ba sauki domin har gobe bilkisu ce zabinsa duk da yasan tayi masa nisa kokuma tafi karfinshi amma dayake ita zuciya babu ruwanta da duk wadannan abubuwan haka ta nace da soyayyarta, kullum aikin kenan tura mata love massages gashi tun bayan bikin kannenta bai sake ganinta ba dan program dinma da takeyi yanzu shiru sai wata bakuwar murya ce keyi gaba daya yarasa gane abinda ke faruwa. Bayan yadawo daga sallar asubah kamar yadda yasaba yazauna saman katifa yajawo wayarshi da niyyar yakirata ya tadata tayi salla yana kunna wayar yaga massage dinta jikinshi na rawa yabude domin wannan shine karo nafarko da ta taba turo masa sakon karta kwana, da sauri da sauri yafara karanta sakon nata kamar haka;
_Amincin Allah ya tabbata agareka, dan Allah idan har bazaka damuba ina son ganinka gobe agidanmu akwai muhimmiyar maganar da nake so mu tattauna, nagode._
Ajiyar zuciya yasauke yana jin tsoro yana shigarsa, tambayar zuciyarsa yafara yi to yanzu idan taganshi tace baiyi mata ba kokuma tace kar yasake kulata fa? Yajima zaune cikin rashin sanin abinyi daga karshe yabarwa Allah ya kwanta ya tura mata da reply,
_Sarauniyar mata ina fata kin tashi cikin aminci da koshin lafiya, insha Allah yau zan amsa kiranki batare da jinkiri ba amma inaso kibani time da kanki kuma kibani address din saboda ban san gidan nakuba, masoyinki ahar kullum....!_
Daga haka yatura mata ya ajiye wayar yana addu'ar samun nasara acikin wannan al'amari.