Sashe 14
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ango fahad kam abangarensa komai yana tafiya daidai yanzu hakama adaren jiya salim ya rakashi yaje kasuwa suka siyo akwatunan da za azuba lefen aciki, saida yaduba mai tsada ajin farko wanda baza araina ba sannan yabiya kudin danma yasamu ragi kasancewar shagon baffa ne yayan salim,akwatuna guda biyar yasiyo har dan kit na shida kalarshi pink mai haske sosai sai walwali da kyalli yake, dakin mamuh yakai domin acan ake tara kayan wanda kusan yanzu komai yagama haduwa sai dan abinda ba arasa ba, kowa saida ya yaba da wadannan akwatunan domin sunyi mutukar kyau, shifa yanzu wani girma yake jin yazo masa saboda zaiyi aure. Daren ranar baiyi bacci da wuriba sai wurin 2 nadare, washe gari bai fita shagoba sai yamma dan har saida yayanshi Abba yadawo ya iske shi agida,yana dakin yana baje akatifa amma ba bacci yakeyi ba idonshi biyu,
"Kaga ango... Saura wata nawane?"
"Saura yan satittika fa, saura sati nawa zakace ba wata nawa ba?"
Dariya Abba yayi yanemi wuri ya zauna bayan ya cire rigar jikinshi,
"To Allah yanuna mana ashe abin yazo"
"Yazo gaskiya domin saura kiris"
Dariya Abba yayi saboda shi gaba daya kallon abin yake kamar a mafarki wai fahad ne zaiyi aure. Da yamma yana shago yayiwa bilkisu text ya sanar da ita za akawo lefe nanda kwana biyu domin ayiyah tace yakamata akai kayan haka nan tunda yan uwa da abokan arziki sun gama gani, dawo mishi da reply tayi tace Allah yakaimu, wani text din yasake tura mata wai wanne colour din fenti zai yiwa gidan nanma tadawo da reply tace light purple. Bayan faruwar haka da kwana biyu aka shirya kai lefe tun ana igobe za akawo lefen iyallo aka sauka itada yafendo domin akarbi komai dasu, yan uwan ammah kuwa sai ranar da za akawo lefen sukazo da safe, anyi hidima iya hidima sannan annuna bajinta domin anyiwa baki tanadi na musamman, mamuh da anty Fauziyya da Anty asabe ne suka kawo lefen sai maman su salim da matan yayun su fahad guda biyu juwairiyya da kubra,
Acan gidansu bilkisu kuwa gida cike yake da mata ita kam tana daki ita da khulsum bayan sun dawo daga aiki, su maama kuwa ba zama ana can ana raping din soye soyen da za abaiwa baki tun safe suke aiki itada su Hindu ammah bata saka musu ko hannu ba sai dai tazo taga me ake ta komawarta daki wurin baki. Misalin karfe biyar na yamma baki suka karaso hajiya iyallo da guda da shewa ta taresu nan aka soma shiga da akwatina falon ammah inda yan karbar kayan suke, sosai lamarin ya kayatar domin kowa sun girmama kowa, gwaggo badiya kanwar ammah me bimata itace takawo tukwicin dubu talatin ta basu,basu bar gidanba sai jikin magriba dauke da garar arziki nan kowa ya raja'a wurin kallon kayan banda su meenah dake can dakin bilkisu suna tasu shaftar ita kuma Hindu na kwance tunda suka gama wadannan soye soyen kanta ke juyawa,
"Amarya kodai da bayani ne?" Inji khulsum, dariya maama tayi tace,
"Ai ba ita kadai ba har dayar itama dazu tagama amanta yanzune ta warware..."
Caraf meenah tayi tace,
"Kai Anty mama kiji tsoron Allah.... Maine fa yahau min kai"
Ita dai bilkisu na zaune tana jinsu tana bin kowa da ido bata uhm bare um um, tasan da ace hamood ne yakawo mata lefe yau ai da farin cikin da zata tsinci kanta aciki Allah kadai yasani amma bata fitar da ran hakanba agaba tunda idan da rai to da rabo.
Sai dare suka samu zarafin kallon kayan bayan mutane sun baje domin hatta yan uwan ammah adaren suka tafi yanzu sai su iyallo, bilkisu na saman kujera sukuma su khulsum suna gaban akwatunan suna kallon kayan daya bayan daya, saida suka gama tsaf sannan ta raka khulsum tatafi da tadawo dakinta tawuce bata koma wurinsu maama ba domin ita kadai tasan abinda take ji.
Ango dai abangarenshi yagama komai duk da har wata yar rama yayi kadan saboda stress danma yanada mataimaka, ko shago yanzu ba sosai yake zuwa ba, shiyasa lokacin da salim yakai musu labarin wai fahad zaiyi aure abin yabasu mamaki duk sai suka fara zargin to ko husnah zai aura amma sai salim yace musu a'a wannan watace daban basu ma santa ba. Saida biki yarage saura sati daya yana shago yana dinka farar shaddar da zai saka ranar daurin aure saiga husna, daga cefane take tabiyo ta shagon dama arana takan zo shagon nan sau biyu ko sau uku,
Su biyune ashagon daga shi sai kanin hamza dake koyon dinki, sauri yake yagama yatafi gida domin ayiyah na nemansa,
Zama husna tayi gefenshi dayake akan benci yake,
"Prince... Yakake"
"Lafiya husna, ya karatu?"
Kayan dayake dinkawa ta kalla sai kuma ta kalli bakar ledar dake gefen keken da tarin invitation card aciki, babu bata lokaci takai hannu ta dauko kafin ya fauce har ta matsa tana karantawa tiryan tiryan, idanuwanta ne suka cika da kwalla ganin sunanshi baro baro ajiki domin harda saka Prince in bracket, ai cefanen da tashigo dashi shagon nan tatafi tabarshi tana kuka fahad yanata kiranta amma taki ta ko waiwayo, duk kuma yau sai yaji tausayinta ya kamashi ganin akanshi take wannan kukan, duk da yana saurin yaje gida amma hakura yayi yakira Salim dan ya rakashi school of nursing wurin husnah, kayanta da tabari yadaukar mata yatafi mata dashi, yakirata yafi sau biyar amma bata dauka ba tana kwance tanata kuka yan dakinsu kawayenta sai rarrashinta sukeyi amma taki yin shiru fiyeda mintuna talatin kenan take kukan nan, ganin taki daga wayarshi sai yatura mata text akan tayi hakuri tazo yana son ganinta, wannan shine karo nafarko da yazo wurinta har cikin makarantarsu amma ita kullum sai taje wurinshi kaf kawayenta babu wanda bai san prince ba yan dakinsu kuwa da sunanshi suke kiranta saboda kowanne bango dake jikin dakin sunanshi ne rubuce da marker, idanuwanta sunyi jajur tafito tazo wurinshi suna tsaye shida salim amma shi yana kan roba roba din Salim da alama shine ya tukosu yakawosu,
Wani sabon hawayene yazubo mata lokacin da sukayi ido hudu dashi,
"Husnah menene abin kukane? Meye zaki tada hankalinki?"
Harara ta watsa masa batare da tayi magana ba, murmushi Salim yayi yasa baki cikin sigar lallashi yace,
"Kiyi hakuri husnah, kedai prince kikeso to ko yayi aure karki duba aurensa kawai kidubi soyayyar da kike yimasa saboda rayuwa tsarice daga ubangiji tayuyu ke ata biyu zakizo, wannan ba matsala bace, ki kwantar da hankalinki dan Allah..."
Kalaman Salim sunyi nasarar dan rage mata radadin da takejin zuciyarta nayi amma har lokacin taki koda kallon fahad, har Salim yagama tsarata tasauko bata kalli fahad ba, da zai bata ledar ta wacce ta baro ashago bata kalleshi ba ta karba, tura babur din yayi yamatsa kusa da ita kamar zai takata ai kuwa babu shiri takai masa duka duk da idan tayi masa irin wannan hade fuska yake yau murmushi yayi yace,
"To ki dan kalleni mana husnah tah..."
Ai kuwa kalmar tayi mata dadi shiyasa babu bata lokaci ta dan warware harda su kyalkyala dariya ganin haka yadauki Salim suka tafi, shidai yasan baya son husnah amma yau yana tausaya mata domin tanuna masa iyakar soyayya tun ranar da tafara zuwa shagonsu taganshi tafara sonshi duk da fada yafi yawa cikin mu'amular tasu saboda ita bata kunyar tabashi agaban kowaye ko yanzu kafin su baro wurinta saida ta dafashi ta hanyar dora hannunta kan nashi,
"Gaskiya akwai matsala fa, dan wallahi yarinyar nan dagaske take sonka"
"To ya zatayi sai dai tayi hakuri tunda nidai aure zanyi"
"Sai ka kara da ita"
Dariya fahad yayi,
"So kake bilkisu ta korene daga gidan kenan"
"Kaida gidanka taya zata koreka"
"Allah saita koreni ai gida yazama nata, ko kuma daga daki kasa akoroni falo"
Dariya sukayi gaba daya, har gida salim yakaishi sannan yatafi shikuma yashiga wurinsu ayiyah domin jin ba'asin kiran da ake yimasa, gyadar yatarar da mamuh na tacewa akwando ta dahu ligif kanfata yayi a cup yawuce falon ayiyah yana ci,
"Ayiyah wannan gyadar badai dadiba ta dahu wallahi"
"To santi kake kenan, yawwa dama maganar sati dayan da amarya zatayi ananne shine nace ai gara kafara tuntubarta tun yanzu dan tasani ko"
Dan jimm yayi, tabbas yasan kam haka al'adarsu ayiyah take yayinsu ma duk da sukayi aure saida matansu sukayi kwanaki bakwai bakwai agidan,
"Idan kuma kana ganin wani za atura babba to sai atura yaje yasanar dasu..."
"A'a ayiyah bari zanje anjima infada mata"
"Yawwa ka kokarta dama shine kiran da nake yimaka"
Saida ya cinye gyadar nan tsaf sannan yatashi yafita, yaci sa'a salim na gida dan haka Babur dinsa yaje yakarba yanufi gidansu bilkisu duk da baida tabbacin ko tana nan, dawowarsu kenan daga kasuwa sun siyo furnitures tana kokarin rage kayan jikinta yakirata yace yana waje, ita wallahi bataso wannan zuwan nashi ba haka dai ta daure ta zura doguwar riga da hijabi tafita....
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA...!*
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*16*
*Littafin kamar da wasa na kudi ne yar uwa idan kinada bukata kibiya ki karanta.*
***Ba dan tanasoba haka ta fito ta sameshi yana compound din gidan tsaye jikin wata bishiya,
"Baby..."
Batare da ta kalleshi tace,
"Yakake?"
"Lafiya lau ranki yadade, ya mutanen gida?"
Atakaice ta amsa da,
"Lafiya"
"Am dama namanta ne ban fada miki wani abuba shine yanzu nazo sanar dake, mu a family dinmu idan anyi aure sai ankai amarya gidansu ango acan za aware mata daki har sai tayi tsawon kwanki bakwai ko wani abu mai kamada haka..."
"Wannan al'adar wanne garine kenan?" Ta tambaya batare data kalleshi ba,
"Fulanin kura..."
"So yanzu dai kana nufin gidanku za akaini acan zan zauna har na tsawon 1 week?"
"Ba lallai yakai hakaba dama kawai al'adace amma yana yuyuwa ma bazaifi 3 days ba ko 2"
Jijjiga kai tayi ta jingina jikin bishiyar flower tana kallon gefe,
"Babu damuwa..., ya maganar dinkuna ne wai? Naji shiru kuma tun ranar fa nayi maka maganar"
"Bani intafi dasu adaren nan zan yanka, abubuwane suka yimin yawa wallahi baby ko bakiga har nayi baki ba na fada...?"
"Bafa na son sunan nan nafada maka, so kadaina"
"Kaga ango... Saura wata nawane?"
"Saura yan satittika fa, saura sati nawa zakace ba wata nawa ba?"
Dariya Abba yayi yanemi wuri ya zauna bayan ya cire rigar jikinshi,
"To Allah yanuna mana ashe abin yazo"
"Yazo gaskiya domin saura kiris"
Dariya Abba yayi saboda shi gaba daya kallon abin yake kamar a mafarki wai fahad ne zaiyi aure. Da yamma yana shago yayiwa bilkisu text ya sanar da ita za akawo lefe nanda kwana biyu domin ayiyah tace yakamata akai kayan haka nan tunda yan uwa da abokan arziki sun gama gani, dawo mishi da reply tayi tace Allah yakaimu, wani text din yasake tura mata wai wanne colour din fenti zai yiwa gidan nanma tadawo da reply tace light purple. Bayan faruwar haka da kwana biyu aka shirya kai lefe tun ana igobe za akawo lefen iyallo aka sauka itada yafendo domin akarbi komai dasu, yan uwan ammah kuwa sai ranar da za akawo lefen sukazo da safe, anyi hidima iya hidima sannan annuna bajinta domin anyiwa baki tanadi na musamman, mamuh da anty Fauziyya da Anty asabe ne suka kawo lefen sai maman su salim da matan yayun su fahad guda biyu juwairiyya da kubra,
Acan gidansu bilkisu kuwa gida cike yake da mata ita kam tana daki ita da khulsum bayan sun dawo daga aiki, su maama kuwa ba zama ana can ana raping din soye soyen da za abaiwa baki tun safe suke aiki itada su Hindu ammah bata saka musu ko hannu ba sai dai tazo taga me ake ta komawarta daki wurin baki. Misalin karfe biyar na yamma baki suka karaso hajiya iyallo da guda da shewa ta taresu nan aka soma shiga da akwatina falon ammah inda yan karbar kayan suke, sosai lamarin ya kayatar domin kowa sun girmama kowa, gwaggo badiya kanwar ammah me bimata itace takawo tukwicin dubu talatin ta basu,basu bar gidanba sai jikin magriba dauke da garar arziki nan kowa ya raja'a wurin kallon kayan banda su meenah dake can dakin bilkisu suna tasu shaftar ita kuma Hindu na kwance tunda suka gama wadannan soye soyen kanta ke juyawa,
"Amarya kodai da bayani ne?" Inji khulsum, dariya maama tayi tace,
"Ai ba ita kadai ba har dayar itama dazu tagama amanta yanzune ta warware..."
Caraf meenah tayi tace,
"Kai Anty mama kiji tsoron Allah.... Maine fa yahau min kai"
Ita dai bilkisu na zaune tana jinsu tana bin kowa da ido bata uhm bare um um, tasan da ace hamood ne yakawo mata lefe yau ai da farin cikin da zata tsinci kanta aciki Allah kadai yasani amma bata fitar da ran hakanba agaba tunda idan da rai to da rabo.
Sai dare suka samu zarafin kallon kayan bayan mutane sun baje domin hatta yan uwan ammah adaren suka tafi yanzu sai su iyallo, bilkisu na saman kujera sukuma su khulsum suna gaban akwatunan suna kallon kayan daya bayan daya, saida suka gama tsaf sannan ta raka khulsum tatafi da tadawo dakinta tawuce bata koma wurinsu maama ba domin ita kadai tasan abinda take ji.
Ango dai abangarenshi yagama komai duk da har wata yar rama yayi kadan saboda stress danma yanada mataimaka, ko shago yanzu ba sosai yake zuwa ba, shiyasa lokacin da salim yakai musu labarin wai fahad zaiyi aure abin yabasu mamaki duk sai suka fara zargin to ko husnah zai aura amma sai salim yace musu a'a wannan watace daban basu ma santa ba. Saida biki yarage saura sati daya yana shago yana dinka farar shaddar da zai saka ranar daurin aure saiga husna, daga cefane take tabiyo ta shagon dama arana takan zo shagon nan sau biyu ko sau uku,
Su biyune ashagon daga shi sai kanin hamza dake koyon dinki, sauri yake yagama yatafi gida domin ayiyah na nemansa,
Zama husna tayi gefenshi dayake akan benci yake,
"Prince... Yakake"
"Lafiya husna, ya karatu?"
Kayan dayake dinkawa ta kalla sai kuma ta kalli bakar ledar dake gefen keken da tarin invitation card aciki, babu bata lokaci takai hannu ta dauko kafin ya fauce har ta matsa tana karantawa tiryan tiryan, idanuwanta ne suka cika da kwalla ganin sunanshi baro baro ajiki domin harda saka Prince in bracket, ai cefanen da tashigo dashi shagon nan tatafi tabarshi tana kuka fahad yanata kiranta amma taki ta ko waiwayo, duk kuma yau sai yaji tausayinta ya kamashi ganin akanshi take wannan kukan, duk da yana saurin yaje gida amma hakura yayi yakira Salim dan ya rakashi school of nursing wurin husnah, kayanta da tabari yadaukar mata yatafi mata dashi, yakirata yafi sau biyar amma bata dauka ba tana kwance tanata kuka yan dakinsu kawayenta sai rarrashinta sukeyi amma taki yin shiru fiyeda mintuna talatin kenan take kukan nan, ganin taki daga wayarshi sai yatura mata text akan tayi hakuri tazo yana son ganinta, wannan shine karo nafarko da yazo wurinta har cikin makarantarsu amma ita kullum sai taje wurinshi kaf kawayenta babu wanda bai san prince ba yan dakinsu kuwa da sunanshi suke kiranta saboda kowanne bango dake jikin dakin sunanshi ne rubuce da marker, idanuwanta sunyi jajur tafito tazo wurinshi suna tsaye shida salim amma shi yana kan roba roba din Salim da alama shine ya tukosu yakawosu,
Wani sabon hawayene yazubo mata lokacin da sukayi ido hudu dashi,
"Husnah menene abin kukane? Meye zaki tada hankalinki?"
Harara ta watsa masa batare da tayi magana ba, murmushi Salim yayi yasa baki cikin sigar lallashi yace,
"Kiyi hakuri husnah, kedai prince kikeso to ko yayi aure karki duba aurensa kawai kidubi soyayyar da kike yimasa saboda rayuwa tsarice daga ubangiji tayuyu ke ata biyu zakizo, wannan ba matsala bace, ki kwantar da hankalinki dan Allah..."
Kalaman Salim sunyi nasarar dan rage mata radadin da takejin zuciyarta nayi amma har lokacin taki koda kallon fahad, har Salim yagama tsarata tasauko bata kalli fahad ba, da zai bata ledar ta wacce ta baro ashago bata kalleshi ba ta karba, tura babur din yayi yamatsa kusa da ita kamar zai takata ai kuwa babu shiri takai masa duka duk da idan tayi masa irin wannan hade fuska yake yau murmushi yayi yace,
"To ki dan kalleni mana husnah tah..."
Ai kuwa kalmar tayi mata dadi shiyasa babu bata lokaci ta dan warware harda su kyalkyala dariya ganin haka yadauki Salim suka tafi, shidai yasan baya son husnah amma yau yana tausaya mata domin tanuna masa iyakar soyayya tun ranar da tafara zuwa shagonsu taganshi tafara sonshi duk da fada yafi yawa cikin mu'amular tasu saboda ita bata kunyar tabashi agaban kowaye ko yanzu kafin su baro wurinta saida ta dafashi ta hanyar dora hannunta kan nashi,
"Gaskiya akwai matsala fa, dan wallahi yarinyar nan dagaske take sonka"
"To ya zatayi sai dai tayi hakuri tunda nidai aure zanyi"
"Sai ka kara da ita"
Dariya fahad yayi,
"So kake bilkisu ta korene daga gidan kenan"
"Kaida gidanka taya zata koreka"
"Allah saita koreni ai gida yazama nata, ko kuma daga daki kasa akoroni falo"
Dariya sukayi gaba daya, har gida salim yakaishi sannan yatafi shikuma yashiga wurinsu ayiyah domin jin ba'asin kiran da ake yimasa, gyadar yatarar da mamuh na tacewa akwando ta dahu ligif kanfata yayi a cup yawuce falon ayiyah yana ci,
"Ayiyah wannan gyadar badai dadiba ta dahu wallahi"
"To santi kake kenan, yawwa dama maganar sati dayan da amarya zatayi ananne shine nace ai gara kafara tuntubarta tun yanzu dan tasani ko"
Dan jimm yayi, tabbas yasan kam haka al'adarsu ayiyah take yayinsu ma duk da sukayi aure saida matansu sukayi kwanaki bakwai bakwai agidan,
"Idan kuma kana ganin wani za atura babba to sai atura yaje yasanar dasu..."
"A'a ayiyah bari zanje anjima infada mata"
"Yawwa ka kokarta dama shine kiran da nake yimaka"
Saida ya cinye gyadar nan tsaf sannan yatashi yafita, yaci sa'a salim na gida dan haka Babur dinsa yaje yakarba yanufi gidansu bilkisu duk da baida tabbacin ko tana nan, dawowarsu kenan daga kasuwa sun siyo furnitures tana kokarin rage kayan jikinta yakirata yace yana waje, ita wallahi bataso wannan zuwan nashi ba haka dai ta daure ta zura doguwar riga da hijabi tafita....
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA...!*
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*16*
*Littafin kamar da wasa na kudi ne yar uwa idan kinada bukata kibiya ki karanta.*
***Ba dan tanasoba haka ta fito ta sameshi yana compound din gidan tsaye jikin wata bishiya,
"Baby..."
Batare da ta kalleshi tace,
"Yakake?"
"Lafiya lau ranki yadade, ya mutanen gida?"
Atakaice ta amsa da,
"Lafiya"
"Am dama namanta ne ban fada miki wani abuba shine yanzu nazo sanar dake, mu a family dinmu idan anyi aure sai ankai amarya gidansu ango acan za aware mata daki har sai tayi tsawon kwanki bakwai ko wani abu mai kamada haka..."
"Wannan al'adar wanne garine kenan?" Ta tambaya batare data kalleshi ba,
"Fulanin kura..."
"So yanzu dai kana nufin gidanku za akaini acan zan zauna har na tsawon 1 week?"
"Ba lallai yakai hakaba dama kawai al'adace amma yana yuyuwa ma bazaifi 3 days ba ko 2"
Jijjiga kai tayi ta jingina jikin bishiyar flower tana kallon gefe,
"Babu damuwa..., ya maganar dinkuna ne wai? Naji shiru kuma tun ranar fa nayi maka maganar"
"Bani intafi dasu adaren nan zan yanka, abubuwane suka yimin yawa wallahi baby ko bakiga har nayi baki ba na fada...?"
"Bafa na son sunan nan nafada maka, so kadaina"