← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 45 OF 67

Sashe 45

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sai lokacin ya daga ido ya kalleta amma baiyi magana ba dolenta tajanye idanuwanta daga gareshi saboda kwarjinin da yayi mata. Cikin fushi taja hijabinta tafita, dakin Ammah taje tana tambayarta me fahad keyi adakinta nan ammah tace shida dakin matarsa sai aje ana tambayar me yakaishi?

Sake komawa dakin nata tayi jiki babu kwari wato shi aka sake aura mata akaro na biyu ashe ashe zamansu bai kareba Allah kadai yasan ranar karewarsa, ita dai tasan bazata yiwa Allah butulciba amma gaskiya bahaka taso ba, ba da fahad take son gudanar da kayan kunyar nanba, bata son yaga girmanta har yakai ga rainata dama gashi yanzu tafara ganin salon rainin nashi tunda ko gaisheta baiyi ba bare tasa ran zata bashi umarni yabi kamar zamansu na baya, afusace tashige cikin bathroom bayan taja towel dinta dake kan kofa, tana wanka tana tunani yanzufa yaron nan dan baida kunya sai yace zai ziyarceta a shimfida ko?

"Subhanallahi... Allah ya sawwake... Ashe kuwa zan mutu da budurcina..." Tafada acikin zuciyarta. Shi dai yana zaune yana sauraron karar ruwan da take wanka dashi acikin bathroom, yasan jira take yagaisheta kamar yadda yakeyi ada amma abinda bata saniba shine yanzu ba da bace idan har tunaninta shine zai gaisheta to zasu shekara basu gaisa ba sannan yanzu itace ma zata rinka gaisheshi ko tana so ko bata so dolenta dan bazai dauki raini ba, jinsa yake yi yanzu a matsayin babba gaba da ita,

Yanata murmushi shi kadai sakamakon abinda yagano a facebook dama post din da akayi magana akan cikakkiyar mace dinnan ta yadda ake gane alamominta yatafi nema wanda yakai kusan shekara da karantawa amma dayake Facebook baya goge abu komai jimawar da yayi sai gashi yasameshi bayan dogon bincike, duk macen dake da kananun ido to jarababbiya ce awurin shimfida,sannan wadda dan yatsanta na kafa nakusa da babba yafi babban tsawo to tanada bukata sosai, mai hips sosai tanada nisa, haka mai manyan mazaunai, sannan mai manyan chest itama tanada yawan bukata,mai dan mitsitsin baki to halittarta ma ta ya mace hakan take, yana tsaka da sake karantawa ta bude kofa tafito daga cikin bathroom din fuskarta babu fara'a shima gimtse tasa fuskar yayi yana sake karanta post din wanda wannan shine karo kusan na biyar da yake ta tisawa yana sake maimaitawa, shi bai damu da yaga wadannan abubuwan da ya karanta atare da husnah ba amma akan Bilkisu kam sai yagane komai.

Tana cika tana batsewa ta nemi wuri ta zauna bayan ta dauki man shafawa ita duk abinda yafi bata mata rai shine rashin gaishetan da baiyiba sannan tana yimasa magana yayi wani banza da ita dan tsabar rainin wayo acikin hijab taketa nuku nukun shafe jikinta da mai saboda yanzu yanayi ya sauya duk da jiya da yau zafi akeyi amma idan kayi wanka baka shafa maiba sai kayi fururu saboda lokacin sanyine, ta gefen ido yake satar kallonta,yatsun kafarta yaketa satar kallo ai kuwa yaga nakusa da babban yafi babban tsayi, daidai lokacin ta mike ta isa gaban wardrobe dinta ta juya mishi baya tana neman kayan da zata saka,kallonta yake tayi ta baya ya kafe hips dinta da ido,

"I will find it out...." Yafada acikin zuciyarshi yana dariyar mugunta,

"Uwar son girma, ashe har yanzu halin nan yana nan ba asauyaba na son girma... Very soon Zamu banbance nidake waye babba...." Yasake fada cikin ranshi, doguwar riga ta ciro ta atamfa tanata yin kunkuni,

"Kawai zaka wani shigo min daki kasani agaba... Ban son takura..."

Daga haka tawuce bathroom tana cigaba da kunkuninta, duk abinda take fada yana jinta saboda shi jinsa akusa yake komai kankantar motsi sai yajishi shiyasa suke yawan fada da abba yayanshi domin idan yana bacci ko tari abba yayi sai yaji, jine dashi sosai kamar maciji ko kana dan nesa dashi kayi gulmarshi sai yaji sai dai kawai yarabu dakai yayi kamar baiji ba. Mintuna kadan sai gata tafito rikeda hijabinta a hannu, akofar bathroom din ta tsaya ta shanya towel dinta sannan takaraso cikin dakin daidai lokacin da wayarta tafara kara cikin sauri ta dauka tana cewa,

"Gani nanfa... Fito kofar gidanki zanzo da mai napep inyaso kawai sai mu wuce..."

Daga haka ta ajiye wayar tawuce gaban mirrior ta bulbula turare halinsu daya dashi wurin son kamshi kwata kwata bata gajiya da siyan turare ko tanada kwalba ishirin a ajiye kan mirror dinta, maroon din mayafi taciro kasancewar atamfar jikinta akwai ratsin maroon ajiki ta dauki hand bag milk ta dauki wayarta sannan tanufi wurin shoe rack tadauko flat din takalminta tasaka tayi hanyar kofa, sai da takusa zuwa kofar cikin isa da kasaita taji yace,

"Ina zakije?...."

Bata ko kulashiba tayi niyyar fita nan taji yasake maimaita ina zakije?

Kanta tsaye tabude kofar zata fita amma kawai sai ji tayi ya danko waist dinta yadawo da ita baya, sam bataji lokacin da yataso ba bare taji tafiyarsa, mayar da kofar yayi ya rufe, yanda ta sha kunu haka shima yasha kunu, kawar da kanta tayi gefe daya tana huci yayinda shikuma yake kallonta ko kiftawa baya yi,

"Wai meye haka? Wannan wanne irin wulakanci n...."

Bata kai ga karasawa ba taji ya fincikota wanda har saida kirjinsu suka manne wuri daya, numfashinsu ke haduwa kowa yana shakar na kowa, ido ta daga dakyar ta kalleshi shima yana kallonta,

"Wa kika tambaya da zaki fita?....... Ehye?.... Tambayarki nake.... Nace wa kika tambaya?" Yakarasa magana cikin tsawa,

Yana kallon yadda idanuwanta ke kadawa tamkar zata fashe da kuka, cikin bakin ciki da rawar murya tace,

"Ba asaniba..... Dallah ni ka sakeni...."

Sake matseta yayi har lokacin yana rikeda damtsenta daya tana manne kirjinshi,

"Ni kike cewa baki saniba?.... Idan kikayi wasa wallahi daga yau bazaki sake ko taka daidai da kofar gidaba.... Zakiyita zama cikin gidan nan babu fita har sai ranar da na gadamar daukarki na kaiki duk inda nakeso...."

Sake matsota yayi cikin huci yace,

"Sannan kisan irin maganar da zaki rinka fada min idan bahaka ba sai kinyi nadama...."

Fincikarta yayi wanda har kayan hannunta suna zubewa yaje ya jefata kan gado nan ta zabura ta mike wanda hakan yaso bashi dariya amma yadake,

Tsayawa tayi ta rike kugu tana haki tamkar dambe zasuyi,

Matsawo yafara yi ahankali yana cewa,

"Ko dambe zakiyi dani ne? Nace dambe kika tashi yi dani....?"

Kafin tabashi amsa wakar ali jita tafara tashi daga cikin wayarshi, _"Rana da wata suna da haske gimbiyata sai ke soyayyarmu har abada...ko rana da wata sun daina haske gimbiyata sai ke soyayyarmu har abada..... I love u baby.....Sarauniya baby...."_

Komawa yayi da baya yadauki wayar domin yasan husnah ce saboda ita kadai yasawa wannan tune din,

Zama yayi kan bedside drewar dinta yadauki wayar,

"Sweet ma'u ya akayi.... Ko har yanzu fushin akeyi dani?" Yafada yana murmushi kasancewar tun lokacin da yafada mata anmayar da aurensu da Bilkisu bata daukar wayarshi sai yau da ta kirashi,

"Ya fahad Allah kai dinne kana bani headache dayawa...."

Hands free yasaka wayar tayadda Bilkisu zataji komai wacce har lokacin ke tsaye tana rikeda waist dinta,

"Am very sorry one love... Ki yafewa Prince dinki idan bahaka ba ciwon zuciyata yatashi dama kuma kin san ata sanadiyar sonki ya kamani...."

Ajiyar zuciya husnah ta sauke sannan cikin sanyin murya tafurta,

"No ya fahad dan Allah kabari bana son inrasaka.... Na hakura, bazan sake bata maka rai ba.... Ranar ma ban san meya sameni ba har nayi fushi dakai... Am so sorry..."

"Kishi...." Yafada yana murmushi yana satar kallon Bilkisu wacce tacika tayi famm sai huci takeyi kamar bijimin sa,

"U are right.... Ni nasan inada kishi akanka bana son nayi shearing dinka da kowa amma babu yadda zanyi i will accept koma meye...."

"That's why am loving u.... I love u yanmatanah..."

Ai Bilkisu bata jira tagama jin wadannan mugayen kalmomin nashiba ta shige cikin bathroom ta bugo kofar da karfi garammm wadda hatta husnah dake kan waya saida taji, har suka gama waya da husnah Bilkisu bata fitoba, hularshi yadauka yasaka yasan acike take dashi na ya hanata fita unguwa gashi kuma yazo yana waya da wata agabanta duk da baida tabbacin ko tana kishi ko sabanin haka amma yadauki alwashin gano hakan, itace bata saniba duk maganganun da yake fadawa husnah ita yake fadawa indirectly amma yasan bazata ganeba, gaban bathroom din yaje yatsaya yakara kunnensa amma baiji motsin komai ba yasan ba komai takeyi ba,

"Kin dai ji abinda nafada miki ko? Karki sake inji labarin kin fita... Sannan ki kira ita kawar taki kifada mata nahana wannan fitar..."

Cikin jin haushi da masifa yaji tace,

"Sai anfitan... Kayi abinda zakayi... Kuma baza akiratan afada mata dinba kai ka kirata mana da kanka... Aikin ban..."

"Idan kika kuskura kika karasa ko...idan ba tsoro ba kibude kofar mana....", kwafa yayi da karfi sannan yace,

"Ni ai bana kiran matan mutane iya inda Allah ya tsayar dani na tsaya... Gobe aiki kadai nayarda kifita baya ga nan duk inda kikaje keda Allah..."

Bai jira abinda zatace ba yawuce yafita yana jin wayarta nata ringing duk da bai dubaba yasan abokiyar tafiyar tatace taji shiru shine kila take kira, duk da bai fada directly ba tagane da hamood yake da yace wai shi baya kiran matan mutane, jin yafita yasa wasu hawayen bakin ciki zubo mata, wai ita fahad kanin kanin bayanta ke yiwa haka wannan wacce irin kaddara ce? Wai meyasa zaman nan yasake kulluwa?....

*Littafin nan na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*

*_Ummi Shatu_*

JIYA IYAU...

*Wannan littafin na kudine me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*

43***Tafi mintuna goma cikin bathroom din bata ko motsa ba kawai hawayen bakin ciki da takaicine ke fita daga idanuwanta ba abinda yafi tsaya mata arai irin iko da isar da yake neman fara nuna mata, danme zai sakata agaba yana yi mata tsawa? Bude kofar bathroom din tayi tafito ko zama bata yiba ta nufi falon ammah wacce ke zaune suna gaisawa da Abba amma kafin Bilkisu takarasa har sunyi sallama kasancewar su lokacin salla yayi acan,

Zama tayi idanuwanta duk sun sauya cikin bacin rai tafara magana,
Chapter 45 · 0% Book details