Sashe 25
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ita dai da yake hankalinta ma baya wurin bata san meyake yiba, wani private hospital ne mai suna al shaddad hospital aka kai meenah acan suka iske maama da mahaifiyar mijin meenah saida suka gaisa da fahad ya tambayi ya mai jiki sannan yatafi gida yaje yaci gaba da baccinsa, wani hukunci na ubangiji itama hindu babu jimawa aka kawota amma ita tana zuwa baifi da mintuna ashirin ba ta haifi yarta katuwa mace nan duk hankali yasake tashi ganin meenah shiru har lokacin tana can dai tanata fama, ammah kuwa da kokari har wannan lokaci bata zo asibitinba tana can gida dai tana tayasu da addu'a sannan tahada komai da ake bukata da abinci tabawa rabi mai aikinta da driver sunkai, su bilkisu kam babu wanda yabi takan abincin da aka kawo domin lokacin ana tunanin yiwa meenah aiki aciro yaron dan har anbaiwa mijinta takarda yasa hannu ba akai ga biyan kudin aikinba Allah ya takaita ta haifo yaronta namiji shima tubarkalla da girmansa.
Sai lokacin kowa yasamu nutsuwa, bayan an kaisu dakin hutu fahad yazo lokacin magriba takusa jariran dai ana ganinsu gasu nan gwanin sha'awa amma iyayen na can ana yimusu karin ruwa sunata baccin gajiya har cikin dakin da jariran suke bilkisu takai fahad ta fara dauko masa macen ta mika masa ya karba yana murmushi, kallon jaririyar yake tayi yakasa bada ita,
"Bazaka dauki dayan bane?" Yaji bilkisu tafada sai lokacin yabata ita yadauki namijin yana mai cigaba da kallon yarinyar, shi dai yana son ahaifa masa yar budurwa ko dan bashida kanwa mace ne oho, bata jaririn yayi yafita yana yimusu Allah yaraya, sai wurin 10 nadare yadawo yadauki bilkisu, washe gari aka sallami masu haihuwar suka tattara sai gidan ammah, dakin bilkisu nada aka sakasu, tunda akayi haihuwar nan bilkisu can take wuni,ana igobe suna suka sha lalle da kitso har masu jegon duk su hudun, da tayi niyyar kwana sai washe garin suna zata koma gidanta amma fahad ya uzzura mata nan Ammah tace tatafi inyaso tadawo da sassafe,
Tanata fushi taje suka tafi shi dai sai santin kunshinta yakeyi da yagani batare da yafito fili ya nuna mata ba har sukaje gida, kasa kasa yake kallonta yana hadiyar yawu, zama tayi bakin gado ta cire mayafinta da dan kwalin kanta hakan yasake saka fahad acikin wani hali, zama yayi agefenta,
"Hajjaju... Dan Allah nidai yau dinnan..."
Kallonshi tayi dama har lokacin bata huceba,
Dan matsawa kusa da ita yasake yi taja baya tana fadin,
"Menene haka??"
"Gaskiya yau yakamata.... Abani.... A..b..a..ni... Ha...kki..na"
Ita saboda yadda ya rarraba maganar ma sai takasa ganewa, nan ta kalleshi yawani matso jikinta sosai yana shafa sumarshi alamun kunya,
"Kace me? Me kace?"
"Cewa nayi yakamata yau abani.... Hakki... Na"
"A ina hakkin naka yake?"
"Ni na nasan a inda yake idan har kin bani dama kuma kin yarje min"
Wata uwar harara ta dalla masa ta mike zata bar wurin da azamarshi yariko hannunta shima yamike tsaye, daga idonta tayi ta kalleshi dayake yafita tsawo kafin tace wani abu jin hannunshi tayi akan waist dinta yamaida ita ta zauna bisa cinyarsa, kokarin yi masa masifa tayi amma ya hanata yin hakan ta hanyar hade bakinsu wuri guda, kokawar kwacewa tafara yi amma takasa saboda yanayin karfin ba daya bane, yana kokarin rabata da rigar jikinta taci nasarar kwatar kanta har ya balle bra din dake jikinta. Hannunta ya riko a masifance take kallonshi da fushi akan fuskarta,
"Dan Allah mai gado yau daya dai ki amince min..."
"Kasan Allah duk ranar da kasake yunkurin tabani ko tam..."
Idanuwanshi dake lumshe yabude ya kalleta,
"Me kike nufine wai? Amma dai ai kin san Shari'a ta bani damar yi ko da karfine ko?"
"Ok fyade kenan zakayi min, right?"
Girgiza kai yayi yamaida idonshi yarufe,
"Ni bazan taba yimiki fyade ba, da yardarki da amincewarki zan kusanceki...."
"Lallai yaron nan bakada kunya..."
"Banida kunya...? To bari infito amarar kunyar tunda har anyi min tambarinta"
Ja daya yayi mata sai gata kusa dashi bakin da ya kirashi da marar kunya yayi magani tareda ragewa kansa zafi bayan yayi fatali da sutturarta, sosai fa yau fahad ya jagwalgwalata daga karshe yabarta ba dan wai yakushi da dukan da takeyi yana shigarshi ba kawai dai ya kyaleta ne,rigarta ta jawo tasaka tana faman cika tana batsewa.
Daga haka ta mike tawuce bathroom cikeda fushi, juyi yayi ya baje sosai akan gadon yana maida numfashi ahankali.....
*Idan har kika karanta alhalin baki biyaba keda Allah domin yana ji kuma yana gani.*
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA....!*
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*24*
***Har tafito daga bathroom din bayan tayi wanka bai motsa daga inda yakeba, kayan baccinta ta dauka ta koma bathroom din tasaka sannan tafito fuskarta ahade babu fara'a,
"Malam dan tashi zan kwanta"
Batare da ya bude idonshi ba yace,
"Ki kwanta mana amma ni bazan iya tashiba yanzu jikina babu karfi saboda akwai abinda yashirya yi kekuma kin katse shi"
Batare da ta tanka masa ba dan taga abin nasa harda rainin wayo aciki tawuce can karshen gadon tayi kwanciyarta bata ko cire hijab din jikinta ba,
"Wallahi akwai matsala ajikinki billy, yanzu ke dan tabakin nan danayi bakiji komai ba? Dan Allah kibari ko dan romance mu sake yi...."
Ita mamaki ma fahad ke bata yanzu wato yasan komai kenan dama can ido yazuba mata bai nuna ba amma yana sane da komai, kunya taji tarufeta dan haka tayi gaggawar juya masa baya,
"Kinji..." Yasake yimata magana yana kallon bayanta,
Ganin bazata kulashi ba yayi shiru ya hakura ai ko wanka bai tashi yayiba daga nan inda yake kwance yacire rigarshi da wandonshi ya wurgar yazauna da iya singileti da gajeren wando, dayake yau itama adan tsorace take dashi bata matsa akan sai ankashe wuta ba ahaka suka kwana da haske, shi dai fahad kasancewar abun yana ranshi har mafarkinta yayi da asubah da yatashi kunkuni yayita yi shi kadai,
"Kaida hakkinka amma anhanaka anbarka da yin mafarki idan kayi magana kuma ace kayi rashin kunya..., ni bada yin abuba nida wanka da asubar nan....."
Tana jinsa tayi kamar bata jiba da tajiyo alamun wanka yakeyi bayan yashiga bathroom ficewa tayi tabar dakin tashiga kitchen tana mamakin wannan al'amari wato shi a wannan shekarun nasa har yasan yanda zaiyi da mace lallai, abu mai sauki tahada masa takai dining sannan taje daki zata shiga wanka yana baje saman gado jikinsa sanye da jeans da t shirt da wayarshi ahannu yana chaten da husna yar nacin tasa domin yau kusan kwana uku kenan tanata turo masa sako amma bai budeba sai yau kuma cikin rashin sa,a ashe tana online,
Tana harararshi tashiga wanka harda saka key, bayan tafito sanye da hijab ta kalleshi,
"Malam dan fita zan shirya"
"To ranki yadade"
Yana fita tasawa kofar key tashirya ta dauki duk abinda zata bukata tafita ta sameshi akan kujera yana kwance,
"Bari naje gida sai zuwa dare zan dawo, kayi zamanka basai ka kaini ba zan hau napep"
"To shikenan Allah yatsare"
Fita tayi aranta tana mitar dalilin dayasa bata siyi motaba ma tun wuri, shi fahad murna ma yayi da bashi zai kaita ba domin yasan idan ya dauketa sake famo masa tabon abinda ke damunsa zatayi, haka yawuni agida ranar jikinsa duk babu kwari sai la'asar yafita yaje gidansu acan yaci abinci sannan yatafi dama yasamu su ayiyah suma suna shirin tafiya gidan sunan. Su bilkisu kam yau kansu yasai kayuwa domin suna yayi suna, yara sunci sunan ammah da abba macen yahanazu zasu kirata da Minal namijin kuma lukman zasu kirashi da sultan, gida ya cika dam da dangi da abokan arziki su iyallo da baki baya shiru cewa bilkisu tayi yanzu kuma saura ita itama nanda yan watanni suna so suzo suna, batace komai ba taci gaba da harkarta dama ammah tatura akirata tazo surukanta sunzo iyayen fahad nan taje taji dasu.
Har bayan suna da kwana biyu kullum sai taje gida amma a napep domin shi fahad bai kara daukarta a babur dinsa ba acewarsa saiya warke. Bayan sati uku da sunansu meenah zasu koma gidajen mazajensu ranar bilkisu taje gidan zasuyi sallama da masu jego dama tun yamma hadari yake haduwa amma taki tafiya saida duk suka tafi suka barta bayan sallar isha fahad yazo ya dauketa, ai tun ahanya yayyafi yafara jikasu kafin suje gida sunyi jalaf da ruwa ga hanyar babu haske ga uban gudun da fahad ke shekawa ganin idan tayi wasa tana iya fadowa yasata kankameshi, bayan sunje gida inbanda sanyi babu abinda suke ji daga shi har ita,kayan bacci tasaka yau babu maganar wanka ta kwanta, shigowa dakin shima yayi yana digar da ruwa ya kwashi kayan da zai saka yaje falo ya canja yaje yakwanta kusa da ita, tashi tayi kafin tayi magana ya rigata,
"Ki taimaka min wallahi yau sanyi nakeji kuma duvet dinnan naki yafi wancan blanket din nawa dumi... Zazzabi ma nake ji fa"
"Malam wallahi bazai yuyuba...."
Yabude baki zai sake magana kenan sukaji wata tsawa mai mutukar karfi dan hatta dakin da suke ciki saida ya girgiza, bata san lokacin da kankameshi ba shima haka, jikinta gaba daya rawa yake ga ruwa da ake kwararawa kamar da bakin kwarya, ahaka suka yi bacci suna kwakume da juna har asuba, shine yafara farkawa har lokacin ruwa akeyi, kallonta yayi tana bacci cikin kwanciyar hankali rungume akirjinsa tayi matashin kai da kirjin nasa,
"Su hajjaju iyayen son girma amma kuma ana tsoron tsawa...."
Pillow yajawo zai kwantar da ita akai domin ya fahimci tana fashin salla duk da boye masan da take tayi domin idan bata salla bata son yasani idan asubah tayi saita tashi taje tayi alwala sai tazo ta zauna kamar irin ta idar da salla dinnan tana tasbihi bayan kuma tun lokacin da ya fara kwana adakin ya fuskanta saboda duk lokacin da zata tashi sai yafarka domin abu kadanne ke farkar dashi abacci,
Sai lokacin kowa yasamu nutsuwa, bayan an kaisu dakin hutu fahad yazo lokacin magriba takusa jariran dai ana ganinsu gasu nan gwanin sha'awa amma iyayen na can ana yimusu karin ruwa sunata baccin gajiya har cikin dakin da jariran suke bilkisu takai fahad ta fara dauko masa macen ta mika masa ya karba yana murmushi, kallon jaririyar yake tayi yakasa bada ita,
"Bazaka dauki dayan bane?" Yaji bilkisu tafada sai lokacin yabata ita yadauki namijin yana mai cigaba da kallon yarinyar, shi dai yana son ahaifa masa yar budurwa ko dan bashida kanwa mace ne oho, bata jaririn yayi yafita yana yimusu Allah yaraya, sai wurin 10 nadare yadawo yadauki bilkisu, washe gari aka sallami masu haihuwar suka tattara sai gidan ammah, dakin bilkisu nada aka sakasu, tunda akayi haihuwar nan bilkisu can take wuni,ana igobe suna suka sha lalle da kitso har masu jegon duk su hudun, da tayi niyyar kwana sai washe garin suna zata koma gidanta amma fahad ya uzzura mata nan Ammah tace tatafi inyaso tadawo da sassafe,
Tanata fushi taje suka tafi shi dai sai santin kunshinta yakeyi da yagani batare da yafito fili ya nuna mata ba har sukaje gida, kasa kasa yake kallonta yana hadiyar yawu, zama tayi bakin gado ta cire mayafinta da dan kwalin kanta hakan yasake saka fahad acikin wani hali, zama yayi agefenta,
"Hajjaju... Dan Allah nidai yau dinnan..."
Kallonshi tayi dama har lokacin bata huceba,
Dan matsawa kusa da ita yasake yi taja baya tana fadin,
"Menene haka??"
"Gaskiya yau yakamata.... Abani.... A..b..a..ni... Ha...kki..na"
Ita saboda yadda ya rarraba maganar ma sai takasa ganewa, nan ta kalleshi yawani matso jikinta sosai yana shafa sumarshi alamun kunya,
"Kace me? Me kace?"
"Cewa nayi yakamata yau abani.... Hakki... Na"
"A ina hakkin naka yake?"
"Ni na nasan a inda yake idan har kin bani dama kuma kin yarje min"
Wata uwar harara ta dalla masa ta mike zata bar wurin da azamarshi yariko hannunta shima yamike tsaye, daga idonta tayi ta kalleshi dayake yafita tsawo kafin tace wani abu jin hannunshi tayi akan waist dinta yamaida ita ta zauna bisa cinyarsa, kokarin yi masa masifa tayi amma ya hanata yin hakan ta hanyar hade bakinsu wuri guda, kokawar kwacewa tafara yi amma takasa saboda yanayin karfin ba daya bane, yana kokarin rabata da rigar jikinta taci nasarar kwatar kanta har ya balle bra din dake jikinta. Hannunta ya riko a masifance take kallonshi da fushi akan fuskarta,
"Dan Allah mai gado yau daya dai ki amince min..."
"Kasan Allah duk ranar da kasake yunkurin tabani ko tam..."
Idanuwanshi dake lumshe yabude ya kalleta,
"Me kike nufine wai? Amma dai ai kin san Shari'a ta bani damar yi ko da karfine ko?"
"Ok fyade kenan zakayi min, right?"
Girgiza kai yayi yamaida idonshi yarufe,
"Ni bazan taba yimiki fyade ba, da yardarki da amincewarki zan kusanceki...."
"Lallai yaron nan bakada kunya..."
"Banida kunya...? To bari infito amarar kunyar tunda har anyi min tambarinta"
Ja daya yayi mata sai gata kusa dashi bakin da ya kirashi da marar kunya yayi magani tareda ragewa kansa zafi bayan yayi fatali da sutturarta, sosai fa yau fahad ya jagwalgwalata daga karshe yabarta ba dan wai yakushi da dukan da takeyi yana shigarshi ba kawai dai ya kyaleta ne,rigarta ta jawo tasaka tana faman cika tana batsewa.
Daga haka ta mike tawuce bathroom cikeda fushi, juyi yayi ya baje sosai akan gadon yana maida numfashi ahankali.....
*Idan har kika karanta alhalin baki biyaba keda Allah domin yana ji kuma yana gani.*
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA....!*
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*24*
***Har tafito daga bathroom din bayan tayi wanka bai motsa daga inda yakeba, kayan baccinta ta dauka ta koma bathroom din tasaka sannan tafito fuskarta ahade babu fara'a,
"Malam dan tashi zan kwanta"
Batare da ya bude idonshi ba yace,
"Ki kwanta mana amma ni bazan iya tashiba yanzu jikina babu karfi saboda akwai abinda yashirya yi kekuma kin katse shi"
Batare da ta tanka masa ba dan taga abin nasa harda rainin wayo aciki tawuce can karshen gadon tayi kwanciyarta bata ko cire hijab din jikinta ba,
"Wallahi akwai matsala ajikinki billy, yanzu ke dan tabakin nan danayi bakiji komai ba? Dan Allah kibari ko dan romance mu sake yi...."
Ita mamaki ma fahad ke bata yanzu wato yasan komai kenan dama can ido yazuba mata bai nuna ba amma yana sane da komai, kunya taji tarufeta dan haka tayi gaggawar juya masa baya,
"Kinji..." Yasake yimata magana yana kallon bayanta,
Ganin bazata kulashi ba yayi shiru ya hakura ai ko wanka bai tashi yayiba daga nan inda yake kwance yacire rigarshi da wandonshi ya wurgar yazauna da iya singileti da gajeren wando, dayake yau itama adan tsorace take dashi bata matsa akan sai ankashe wuta ba ahaka suka kwana da haske, shi dai fahad kasancewar abun yana ranshi har mafarkinta yayi da asubah da yatashi kunkuni yayita yi shi kadai,
"Kaida hakkinka amma anhanaka anbarka da yin mafarki idan kayi magana kuma ace kayi rashin kunya..., ni bada yin abuba nida wanka da asubar nan....."
Tana jinsa tayi kamar bata jiba da tajiyo alamun wanka yakeyi bayan yashiga bathroom ficewa tayi tabar dakin tashiga kitchen tana mamakin wannan al'amari wato shi a wannan shekarun nasa har yasan yanda zaiyi da mace lallai, abu mai sauki tahada masa takai dining sannan taje daki zata shiga wanka yana baje saman gado jikinsa sanye da jeans da t shirt da wayarshi ahannu yana chaten da husna yar nacin tasa domin yau kusan kwana uku kenan tanata turo masa sako amma bai budeba sai yau kuma cikin rashin sa,a ashe tana online,
Tana harararshi tashiga wanka harda saka key, bayan tafito sanye da hijab ta kalleshi,
"Malam dan fita zan shirya"
"To ranki yadade"
Yana fita tasawa kofar key tashirya ta dauki duk abinda zata bukata tafita ta sameshi akan kujera yana kwance,
"Bari naje gida sai zuwa dare zan dawo, kayi zamanka basai ka kaini ba zan hau napep"
"To shikenan Allah yatsare"
Fita tayi aranta tana mitar dalilin dayasa bata siyi motaba ma tun wuri, shi fahad murna ma yayi da bashi zai kaita ba domin yasan idan ya dauketa sake famo masa tabon abinda ke damunsa zatayi, haka yawuni agida ranar jikinsa duk babu kwari sai la'asar yafita yaje gidansu acan yaci abinci sannan yatafi dama yasamu su ayiyah suma suna shirin tafiya gidan sunan. Su bilkisu kam yau kansu yasai kayuwa domin suna yayi suna, yara sunci sunan ammah da abba macen yahanazu zasu kirata da Minal namijin kuma lukman zasu kirashi da sultan, gida ya cika dam da dangi da abokan arziki su iyallo da baki baya shiru cewa bilkisu tayi yanzu kuma saura ita itama nanda yan watanni suna so suzo suna, batace komai ba taci gaba da harkarta dama ammah tatura akirata tazo surukanta sunzo iyayen fahad nan taje taji dasu.
Har bayan suna da kwana biyu kullum sai taje gida amma a napep domin shi fahad bai kara daukarta a babur dinsa ba acewarsa saiya warke. Bayan sati uku da sunansu meenah zasu koma gidajen mazajensu ranar bilkisu taje gidan zasuyi sallama da masu jego dama tun yamma hadari yake haduwa amma taki tafiya saida duk suka tafi suka barta bayan sallar isha fahad yazo ya dauketa, ai tun ahanya yayyafi yafara jikasu kafin suje gida sunyi jalaf da ruwa ga hanyar babu haske ga uban gudun da fahad ke shekawa ganin idan tayi wasa tana iya fadowa yasata kankameshi, bayan sunje gida inbanda sanyi babu abinda suke ji daga shi har ita,kayan bacci tasaka yau babu maganar wanka ta kwanta, shigowa dakin shima yayi yana digar da ruwa ya kwashi kayan da zai saka yaje falo ya canja yaje yakwanta kusa da ita, tashi tayi kafin tayi magana ya rigata,
"Ki taimaka min wallahi yau sanyi nakeji kuma duvet dinnan naki yafi wancan blanket din nawa dumi... Zazzabi ma nake ji fa"
"Malam wallahi bazai yuyuba...."
Yabude baki zai sake magana kenan sukaji wata tsawa mai mutukar karfi dan hatta dakin da suke ciki saida ya girgiza, bata san lokacin da kankameshi ba shima haka, jikinta gaba daya rawa yake ga ruwa da ake kwararawa kamar da bakin kwarya, ahaka suka yi bacci suna kwakume da juna har asuba, shine yafara farkawa har lokacin ruwa akeyi, kallonta yayi tana bacci cikin kwanciyar hankali rungume akirjinsa tayi matashin kai da kirjin nasa,
"Su hajjaju iyayen son girma amma kuma ana tsoron tsawa...."
Pillow yajawo zai kwantar da ita akai domin ya fahimci tana fashin salla duk da boye masan da take tayi domin idan bata salla bata son yasani idan asubah tayi saita tashi taje tayi alwala sai tazo ta zauna kamar irin ta idar da salla dinnan tana tasbihi bayan kuma tun lokacin da ya fara kwana adakin ya fuskanta saboda duk lokacin da zata tashi sai yafarka domin abu kadanne ke farkar dashi abacci,