Sashe 34
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bai kara magana ba yafada saman gadonta yakwanta rub da ciki, ko takalmin kafarsa bai cireba, gaba daya tayi mutuwar tsaye ita kam ganin irin marin da hamood ya zabga mata she can't believe wai yau itace acikin wannan rayuwar itada hamood, tajima tsaye kamar wadda aka kafa kafin tanemi wuri ta zauna tana kallonsa yanata sharar baccinsa cikin maye,
"Ohhh Allah.... Ya Allah kayi min maganin wannan masifa...."
Dakyar da sudin goshi tasamu bacci ya dauketa saboda tajima bata samu bacci ba kai rabonta da bacci isasshe kuma mai dadi tun kafin bikinta. Asubar fari ta tashi tayi salla tsakanin mata da miji sai Allah hakan yasa tasoma tashin hamood akan yatashi yayi salla amma fafur yaki tashi daga karshe ma da ta matsa masa afusace yabude ido yadago ya daka mata tsawa,
"Malama wai sallar nan ubanki zan yiwa? Karki sake ki kara tashina..."
Jin abinda yace yayi mutukar razanata, wai ita hamood ke fadawa haka? Rabuwa dashi tayi saboda taga kamar har lokacin mayen bai gama sakinsa ba, anan ita kam taci gaba da zama har gari yagama wayewa, wanka tayi tashirya ta sauka kasa ta shiga kitchen duk ranta adagule zuciyarta a cunkushe wato dama ance zauna da mutum kaga halinsa wato shi hamood wadannan ne nasa halayen kenan? Ahaka ta kammala hada breakfast dinta tanata zancen zuci bayan ta kammala takai kan dining takoma sama lokacin karfe goma tawuce, sai lokacin hamood yatashi bai ko kalleta ba yashiga bathroom babu jimawa yafito yawuce dakinsa domin shiryawa bin bayansa tayi agabanta yashirya yasake fitowa tana ganinsa baiyi salla ba nan abun yasake daure mata kai, kai tsaye dining yaje tana biye dashi yaja kujera ya zauna itama haka,
Chips yasoma ci da spoon yana kunna wayarsa wadda bilkisu bata san da itaba sai yau,
"Hamood ina kwana....?" Takatse shirun nasu,
"Lafiya lau sweetheart...."
Shiru dukkaninsu sukayi sai zuwa can ta saki ajiyar zuciya dama ita ba abincin take ciba kawai tana jujjuyashi ne,
"Hamood meyasa dan girman Allah ka dauki dabi'ar da ban sanka da itaba ka yabawa kanka....? Hamood dama kana shaye shaye ne? Jiyafa da daddare har marina kayi sannan da asuba ka zagi ubana, gashi yau ko sallar asubah banga kayi ba...."
Saida ya ja wasu seconds sannan yadago ya kalleta,
"Kiyi hakuri sweetheart wallahi duk wadannan abubuwan ban san lokacin da nayisu ba, amma hakan bazai sake faruwa ba, jiyane kin bata min rai dayawa wallahi, duk yanda akayi tsohon mijinki dinnan banzan yaron nan baiso aurenmu dakeba shiyasa yayi min asirin da zan kasa kusantarki..."
Ajiyar zuciya taja ta sauke tana kallonsa,
"Bana tunanin fahad zai aikata abinda kake fada nidai ashawarata kaje asibiti sannan ka binciki wannan matar taka...."
"Matata bata aikata komai ba bilkisu ni nafi danganta matsalar dake tunda ita ko yaushe naje gareta lafiya lau nake gabatar da al'amurana kinga kuwa idan hakane matsalar daga gareki ce..."
Shiru tayi saboda ta fuskanci hamood bazai taba ganewa ba tunda bai san kaidin mataba, har ya kammala babu wanda yasake cewa komai mikewa tsaye yayi,
"Ni nafita.... Zanje office"
Bai jira cewarta ba yafice, tagumi ta rafka bayan tasauke ajiyar zuciya, ranar ma bai dawo gidanba sai 12 amma ba acikin mayeba.
Haka dai aka cigaba da zaman doya da manja domin ta fuskanci salla kwata kwata bata dameshi ba gashi da saurin fushi abu kadan zai hau yafara zagin mutun ko zagin iyayenshi, satinta biyu agidan ranar da yamma daf da magriba sai gashi rikeda babbar trolley wasila na biye dashi tasha attach da wani siririn mayafi, tana zaune afalo suka shigo dama gama girkinta kenan tayi tuwon semo miyar agushi wacce taji busasshen kifi, ganinshi tareda wasila abin yayi mutukar Sosa ranta shiyasa ta dauke kanta. Cikeda rashin damuwa suka karaso ciki hannunsu sarke cikin na juna, wani kallon banza wise kebinta dashi amma ita bata saniba saboda bata ko kalleta ba, gabanta hamood yakarasa yana kallonta,
"Sweetheart dan Allah wasila zata dan zauna damu na tsawon wani lokaci....."
Dagawo tayi ta kalleshi kallo mai kunshe da ma'anoni daban daban batare da ta tanka masa ba tawuce tanufi sama, ajiye trolley din yayi yabi bayanta,
Tana zaune kan stool din dake gaban dressing mirror tayi tagumi tacika tayi famm, tsugunnawa yayi agabanta,
"Haba sweetheart bai kamata fa kiyi hakaba, menene abin damuwa anan? Wasila fa bazata wuce 2 weeks ba zata tafi...."
Harararsa tayi sannan ta kawar da kai gefe,
"To meya hana tazauna anata gidan da zata biyoka nan?"
"Dan Allah kiyi hakuri gidan nata ake dan gyara mata kin san kuma mata da neman fitina musamman wadanda aka yiwa kishiya kiris suke jira suce kayi musu laifi...."
Dakyar dai yasamu ya lallasheta ta sauko,
"To tashi muje kasa..."
"Kaje ina zuwa, sallah zanyi"
Tashi yayi yafita ita kuma tashiga toilet tayi alwala tazo tayi salla tasake gyara fuskarta sannan tasauka kasa, wani karin bakin cikin ta tarar domin hamood ne da wasila kan dining sun gama cin abincin da tasha wahala ta girka kuma ita girkinta batayi da wise ba iya daidai cikinta da na hamood tayi tunda bata san da zuwan wise dinba, fuskarta adaure ta bubbude flasks din nan taga wayam sai ko gutsattsari nanfa tasake hasala ta kalli hamood yayinda ita kuma wise ke kallonta up and down,
"Hamood meye haka dan Allah? Waye yasa ku cinye min abinci?"
"Ayya sweetheart ai nazaci kinci naki wannan nawane shiyasa muka ci...."
"Koda nakane ai kamata yayi kujirani nasauko bawai kawai ku saka agaba ku cinye ba"
"To dai aikin gama yagama just kawai kisake shiga kitchen and find something sharp sharp sai kici ko indomie ne...,bari ni naje nayi salla"
Daga haka yamike yafita ita kuma wise tatashi tawuce bedroom din kasa, kallon wurin da suka ci abincin tayi duk sunyi kaca kaca dashi da miya kamar kajine suka ci kokuma masu bulallen baki, cikeda bacin rai tagyara wurin taje kitchen ta dafa tea taci da snacks takoma daki. Tunda wise tadawo gidan sai abubuwa suka sake kazanta domin ko abinci taci anan zata bar flate din bazata daukeba sai dai bilkisu ta dauke sannan baza tayi girki ba sai wanda bilkisu tadafa zata ci da bilkisu tasamu hamood tayi masa complain sai cewa yayi ita wise bata iya girkiba dan ko shiga kitchen wahala yake mata tayi hakuri har sai ranar da wise din takoya, maganar matsalarsu kuma da ta tuntubeshi akan suje asibiti sai cewa yayi shifa lafiyarsa kalau dan haka babu asibitin da zaije saboda awurinta ne kadai yake fuskantar wannan matsalar amma awurin wise rass yake, ita dai adaddafe tazauna da wise har na tsawon sati biyu kowa harkarsa yakeyi ba ruwan kowa da kowa aikin gidanta kuwa ita keyin kayanta amma wise ko cokali bata dauke mata wani lokacin ma idan tagama cin abinci haka zata yi ball da kwanon komai tsadarsa shiyasa daga ranar da tazo gidan zuwa yanzu ta fasa kwanuka da dishes babu adadi ita dai bilkisu bata taba yimata magana ba saboda badashi tazo ba kayan hamood ne kawai dai ansiyane da sunanta. Satin wasila biyu da yan kwanaki bilkisu tasamu hamood akan maganar tafiyar wise, karkatar da hular kansa yayi ya kalleta,
'Gaskiya kiyi hakuri dan ko zata tafi ba yanzuba saboda amfaninta yafi naki yawa agareni domin awajenta nake samun nutsuwa..."
Daga haka yasa kai yafita dama lokacin ficewa zaiyi, wannan maganar ba karamin ciwo tayi mata ba dan har kuka tasata daga karshe ta rarrashi zuciyarta aranar da yamma sukayi waya dasu elmustapha suke fada mata saura kwana biyu su koma Sudan shiyasa ta daura aniyar zuwa gida gobe domin suyi sallama,tun adaren ranar ta sanarwa hamood shiyasa washe gari tayi asubancin zuwa gida domin 9 acan tayi mata koba komai zata samu sassaucin zaman kuncin da take ciki, kowa nagidan yazaci laulayi ne yamaida ita yanda take ayanzu ita kuma bata sanarwa da kowa ba, acan duk su hindu suka sameta shiyasa tasake cikinsu sunata cafta sai daf da magrib takoma gida tana shiga bedroom dinta tayi turus saboda gaba daya aburkice yake akwatunan lefenta babu ko daya sannan laptop dinta dake kan bedside drewar itama wayam gashi da alama komai nata mai daraja dake cikin dakin anyi gaba dashi......
*littafin Kamar da wasa na siyar© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA....!*
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*32*
*Littafin kamar da wasa na saidawa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
***A mutukar razane tafita daga dakinta ta nufi na hamood shi dai bata ga wata alama dake nuna cewar anshigar masa dakinba sai dai bata da tabbas, sake fitowa tayi tanufi wurin mai gadi hankalinta atashe nan ta fara tambayarsa suwaye da waye suka shigo gidan amma yace mata babu kowa yau kwata kwata ma basuyi baki ba wasila ma tun safe itama tabar gidan har yanzu kuma bata dawoba haka shima hamood,
Cike da damuwa takoma cikin gida ta nemi wuri ta zauna afalo tana jimami duk kuwa da kiraye kirayen sallar da ta jiyo anayi a masallatai daban daban, to kenan barawon ko kuma barayin ta katangar baya suka shigo? Ta tambayi zuciyarta asirrance, bata samu ta motsa daga inda take zauneba su hamood suka shigo shida wise kamar kullum hannunsu sakale cikin na juna, mikewa tsaye tayi,
"Hamood yau gidan nan babu lafiya... Barayine suka shigo, gaba daya sun kwashe min kayana na lefe da laptop dina harda agogona na gold...."
"What....?" Yafurta da karfi, ai tun kafin tasake magana yanufi upstair da sauri gudu gudu, yana zuwa yashiga bedroom dinshi mintuna kadan yasauko hankalinsa amutukar tashe,
"Kai... To ai nima harda dakina suka shiga, kudin wata mota da na siyar shekaran jiya nazo dashi gidan nan sun dauke.... 7 hundred thousands cash..... Ohh my God"
Wani wulakantaccen kallo wise ta watsa musu su duka biyun kafin ta yi gyaran murya,
"Hmmmm haba dear... Wai kai baka gano game dinba har yanzu? Tab..."
Kallon wise yayi idanuwanshi sun fara yin jaa,
"Me kike nufi?"
"To ai wannan abune abayyane kuma afili... Kawai dai matarka sun hada baki da barayi sun shigo gidanka sun yasheka idan bahaka ba tayaya akan san kashigo da kudi? Sannan tayaya zasu iya haurowa gidannan har su shigo batare da anyi guiding dinsu ba.....?"
"Ohhh Allah.... Ya Allah kayi min maganin wannan masifa...."
Dakyar da sudin goshi tasamu bacci ya dauketa saboda tajima bata samu bacci ba kai rabonta da bacci isasshe kuma mai dadi tun kafin bikinta. Asubar fari ta tashi tayi salla tsakanin mata da miji sai Allah hakan yasa tasoma tashin hamood akan yatashi yayi salla amma fafur yaki tashi daga karshe ma da ta matsa masa afusace yabude ido yadago ya daka mata tsawa,
"Malama wai sallar nan ubanki zan yiwa? Karki sake ki kara tashina..."
Jin abinda yace yayi mutukar razanata, wai ita hamood ke fadawa haka? Rabuwa dashi tayi saboda taga kamar har lokacin mayen bai gama sakinsa ba, anan ita kam taci gaba da zama har gari yagama wayewa, wanka tayi tashirya ta sauka kasa ta shiga kitchen duk ranta adagule zuciyarta a cunkushe wato dama ance zauna da mutum kaga halinsa wato shi hamood wadannan ne nasa halayen kenan? Ahaka ta kammala hada breakfast dinta tanata zancen zuci bayan ta kammala takai kan dining takoma sama lokacin karfe goma tawuce, sai lokacin hamood yatashi bai ko kalleta ba yashiga bathroom babu jimawa yafito yawuce dakinsa domin shiryawa bin bayansa tayi agabanta yashirya yasake fitowa tana ganinsa baiyi salla ba nan abun yasake daure mata kai, kai tsaye dining yaje tana biye dashi yaja kujera ya zauna itama haka,
Chips yasoma ci da spoon yana kunna wayarsa wadda bilkisu bata san da itaba sai yau,
"Hamood ina kwana....?" Takatse shirun nasu,
"Lafiya lau sweetheart...."
Shiru dukkaninsu sukayi sai zuwa can ta saki ajiyar zuciya dama ita ba abincin take ciba kawai tana jujjuyashi ne,
"Hamood meyasa dan girman Allah ka dauki dabi'ar da ban sanka da itaba ka yabawa kanka....? Hamood dama kana shaye shaye ne? Jiyafa da daddare har marina kayi sannan da asuba ka zagi ubana, gashi yau ko sallar asubah banga kayi ba...."
Saida ya ja wasu seconds sannan yadago ya kalleta,
"Kiyi hakuri sweetheart wallahi duk wadannan abubuwan ban san lokacin da nayisu ba, amma hakan bazai sake faruwa ba, jiyane kin bata min rai dayawa wallahi, duk yanda akayi tsohon mijinki dinnan banzan yaron nan baiso aurenmu dakeba shiyasa yayi min asirin da zan kasa kusantarki..."
Ajiyar zuciya taja ta sauke tana kallonsa,
"Bana tunanin fahad zai aikata abinda kake fada nidai ashawarata kaje asibiti sannan ka binciki wannan matar taka...."
"Matata bata aikata komai ba bilkisu ni nafi danganta matsalar dake tunda ita ko yaushe naje gareta lafiya lau nake gabatar da al'amurana kinga kuwa idan hakane matsalar daga gareki ce..."
Shiru tayi saboda ta fuskanci hamood bazai taba ganewa ba tunda bai san kaidin mataba, har ya kammala babu wanda yasake cewa komai mikewa tsaye yayi,
"Ni nafita.... Zanje office"
Bai jira cewarta ba yafice, tagumi ta rafka bayan tasauke ajiyar zuciya, ranar ma bai dawo gidanba sai 12 amma ba acikin mayeba.
Haka dai aka cigaba da zaman doya da manja domin ta fuskanci salla kwata kwata bata dameshi ba gashi da saurin fushi abu kadan zai hau yafara zagin mutun ko zagin iyayenshi, satinta biyu agidan ranar da yamma daf da magriba sai gashi rikeda babbar trolley wasila na biye dashi tasha attach da wani siririn mayafi, tana zaune afalo suka shigo dama gama girkinta kenan tayi tuwon semo miyar agushi wacce taji busasshen kifi, ganinshi tareda wasila abin yayi mutukar Sosa ranta shiyasa ta dauke kanta. Cikeda rashin damuwa suka karaso ciki hannunsu sarke cikin na juna, wani kallon banza wise kebinta dashi amma ita bata saniba saboda bata ko kalleta ba, gabanta hamood yakarasa yana kallonta,
"Sweetheart dan Allah wasila zata dan zauna damu na tsawon wani lokaci....."
Dagawo tayi ta kalleshi kallo mai kunshe da ma'anoni daban daban batare da ta tanka masa ba tawuce tanufi sama, ajiye trolley din yayi yabi bayanta,
Tana zaune kan stool din dake gaban dressing mirror tayi tagumi tacika tayi famm, tsugunnawa yayi agabanta,
"Haba sweetheart bai kamata fa kiyi hakaba, menene abin damuwa anan? Wasila fa bazata wuce 2 weeks ba zata tafi...."
Harararsa tayi sannan ta kawar da kai gefe,
"To meya hana tazauna anata gidan da zata biyoka nan?"
"Dan Allah kiyi hakuri gidan nata ake dan gyara mata kin san kuma mata da neman fitina musamman wadanda aka yiwa kishiya kiris suke jira suce kayi musu laifi...."
Dakyar dai yasamu ya lallasheta ta sauko,
"To tashi muje kasa..."
"Kaje ina zuwa, sallah zanyi"
Tashi yayi yafita ita kuma tashiga toilet tayi alwala tazo tayi salla tasake gyara fuskarta sannan tasauka kasa, wani karin bakin cikin ta tarar domin hamood ne da wasila kan dining sun gama cin abincin da tasha wahala ta girka kuma ita girkinta batayi da wise ba iya daidai cikinta da na hamood tayi tunda bata san da zuwan wise dinba, fuskarta adaure ta bubbude flasks din nan taga wayam sai ko gutsattsari nanfa tasake hasala ta kalli hamood yayinda ita kuma wise ke kallonta up and down,
"Hamood meye haka dan Allah? Waye yasa ku cinye min abinci?"
"Ayya sweetheart ai nazaci kinci naki wannan nawane shiyasa muka ci...."
"Koda nakane ai kamata yayi kujirani nasauko bawai kawai ku saka agaba ku cinye ba"
"To dai aikin gama yagama just kawai kisake shiga kitchen and find something sharp sharp sai kici ko indomie ne...,bari ni naje nayi salla"
Daga haka yamike yafita ita kuma wise tatashi tawuce bedroom din kasa, kallon wurin da suka ci abincin tayi duk sunyi kaca kaca dashi da miya kamar kajine suka ci kokuma masu bulallen baki, cikeda bacin rai tagyara wurin taje kitchen ta dafa tea taci da snacks takoma daki. Tunda wise tadawo gidan sai abubuwa suka sake kazanta domin ko abinci taci anan zata bar flate din bazata daukeba sai dai bilkisu ta dauke sannan baza tayi girki ba sai wanda bilkisu tadafa zata ci da bilkisu tasamu hamood tayi masa complain sai cewa yayi ita wise bata iya girkiba dan ko shiga kitchen wahala yake mata tayi hakuri har sai ranar da wise din takoya, maganar matsalarsu kuma da ta tuntubeshi akan suje asibiti sai cewa yayi shifa lafiyarsa kalau dan haka babu asibitin da zaije saboda awurinta ne kadai yake fuskantar wannan matsalar amma awurin wise rass yake, ita dai adaddafe tazauna da wise har na tsawon sati biyu kowa harkarsa yakeyi ba ruwan kowa da kowa aikin gidanta kuwa ita keyin kayanta amma wise ko cokali bata dauke mata wani lokacin ma idan tagama cin abinci haka zata yi ball da kwanon komai tsadarsa shiyasa daga ranar da tazo gidan zuwa yanzu ta fasa kwanuka da dishes babu adadi ita dai bilkisu bata taba yimata magana ba saboda badashi tazo ba kayan hamood ne kawai dai ansiyane da sunanta. Satin wasila biyu da yan kwanaki bilkisu tasamu hamood akan maganar tafiyar wise, karkatar da hular kansa yayi ya kalleta,
'Gaskiya kiyi hakuri dan ko zata tafi ba yanzuba saboda amfaninta yafi naki yawa agareni domin awajenta nake samun nutsuwa..."
Daga haka yasa kai yafita dama lokacin ficewa zaiyi, wannan maganar ba karamin ciwo tayi mata ba dan har kuka tasata daga karshe ta rarrashi zuciyarta aranar da yamma sukayi waya dasu elmustapha suke fada mata saura kwana biyu su koma Sudan shiyasa ta daura aniyar zuwa gida gobe domin suyi sallama,tun adaren ranar ta sanarwa hamood shiyasa washe gari tayi asubancin zuwa gida domin 9 acan tayi mata koba komai zata samu sassaucin zaman kuncin da take ciki, kowa nagidan yazaci laulayi ne yamaida ita yanda take ayanzu ita kuma bata sanarwa da kowa ba, acan duk su hindu suka sameta shiyasa tasake cikinsu sunata cafta sai daf da magrib takoma gida tana shiga bedroom dinta tayi turus saboda gaba daya aburkice yake akwatunan lefenta babu ko daya sannan laptop dinta dake kan bedside drewar itama wayam gashi da alama komai nata mai daraja dake cikin dakin anyi gaba dashi......
*littafin Kamar da wasa na siyar© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA....!*
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*32*
*Littafin kamar da wasa na saidawa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
***A mutukar razane tafita daga dakinta ta nufi na hamood shi dai bata ga wata alama dake nuna cewar anshigar masa dakinba sai dai bata da tabbas, sake fitowa tayi tanufi wurin mai gadi hankalinta atashe nan ta fara tambayarsa suwaye da waye suka shigo gidan amma yace mata babu kowa yau kwata kwata ma basuyi baki ba wasila ma tun safe itama tabar gidan har yanzu kuma bata dawoba haka shima hamood,
Cike da damuwa takoma cikin gida ta nemi wuri ta zauna afalo tana jimami duk kuwa da kiraye kirayen sallar da ta jiyo anayi a masallatai daban daban, to kenan barawon ko kuma barayin ta katangar baya suka shigo? Ta tambayi zuciyarta asirrance, bata samu ta motsa daga inda take zauneba su hamood suka shigo shida wise kamar kullum hannunsu sakale cikin na juna, mikewa tsaye tayi,
"Hamood yau gidan nan babu lafiya... Barayine suka shigo, gaba daya sun kwashe min kayana na lefe da laptop dina harda agogona na gold...."
"What....?" Yafurta da karfi, ai tun kafin tasake magana yanufi upstair da sauri gudu gudu, yana zuwa yashiga bedroom dinshi mintuna kadan yasauko hankalinsa amutukar tashe,
"Kai... To ai nima harda dakina suka shiga, kudin wata mota da na siyar shekaran jiya nazo dashi gidan nan sun dauke.... 7 hundred thousands cash..... Ohh my God"
Wani wulakantaccen kallo wise ta watsa musu su duka biyun kafin ta yi gyaran murya,
"Hmmmm haba dear... Wai kai baka gano game dinba har yanzu? Tab..."
Kallon wise yayi idanuwanshi sun fara yin jaa,
"Me kike nufi?"
"To ai wannan abune abayyane kuma afili... Kawai dai matarka sun hada baki da barayi sun shigo gidanka sun yasheka idan bahaka ba tayaya akan san kashigo da kudi? Sannan tayaya zasu iya haurowa gidannan har su shigo batare da anyi guiding dinsu ba.....?"