← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 67

Sashe 13

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yakarashe maganar acikin ranshi, duk da yace fita zaiyi amma dan naci bata tafiba har saida yagama yanka kayan nan ya kullesu yakai cikin shago yana gaba tana biye dashi har shagon su salim, key din Babur dinshi yakarbo domin dagaske bilkisu yake son gani yanzu da yamnacin nan,

"Inhau muje ka saukeni a school"

Girgiza kai yayi,

"Bana daukar mata a machine sai dai inbaki kudin napep"

Zumbura baki tayi tatafi batare da tace masa komai ba ita ala dole tayi fushi shi kam murmushi yayi yabuga babur din yabashi wuta yaje ya wuceta a kofar plaza. Bilkisu tana zaune hindu tana kitse mata kanta wanda yafi sati uku atsefe mai gadi yashigo kiranta danma kitson manya ne baifi saura biyu agama ba,mamakine ya isheta jin wai ana sallama da ita bata san fahad bane domin lokacin da yazo yanata kiran wayarta amma shiru kasancewar tabar wayar adaki, agaggauce Hindu ta karasa mata ta shiga daki domin dauko mayafi, dukansu mikewa sukayi wai zasuje su gano yayansu, ita dai batace musu komai ba ta kama hannun hudah,

Har tafita bai sakko daga kan Babur dinba yana kai yana duba wayarsa yana dariyar tsokanar da yayanshi Abba keyi masa, ita tafara fitowa fuska ba yabo babu fallasa su meenah na biye da ita,

"Yaya fahad sannu da zuwa"

Sai lokacin yasan fitowarsu Babur din yaja zuwa kusa dasu yana kallon gimbiyar tashi da ta wani dauke kai tana shakar iskar dake kadawa,

"Uhmm son girma kamar gyambo" yafada aranshi afili kuma yace,

"Yau amare ne agidan... Yakuke"

"Lafiya lau ya fahad, ai yanzu amarci sai ku kaida adda labour" inji meenah,

"Wai hakama zakuce?"

"Ehh mana ya fahad gashi kuma wallahi kun dace da juna" inji hindu,

"Shine ai, abin nasu kamar shiri ita baka shi fari...." Meenah tafada tana dariya,

"Gaskiya dai wannan hadin yayi daidai..." Inji mama,

Tana jin duk uban surutun da suke zubawa amma batace musu uffan ba har sukayi suka gama ita abinda yakara kular da itama yayan da taji suna cemasa, gashi sunzo sun wani saki baki sai zuba suke kamar kanyar da bata da zaki. Sun jima awurinshi sannan suka shiga cikin gida amma banda hudah wacce ke makale da ita, saida yaga shigarsu gida sannan ya daga ido ya kalleta yana mikawa hudah hannu babu musu kuwa ta taho wurinshi ya dauketa yadora gaban Babur dinshi,

"Ina yini adda..."

Duk da bataso yin dariya ba amma saida tayi saboda yanayin yanda yayi maganar,

"Lafiya lau... Ya kake?"

"Alhamdulillah, ya mutanen gida?"

"Kowa lafiya"

Shiru sukayi yakoma yiwa hudah wasa wacce keta danna horn din jikin Babur din nashi, ji yake inama ace yarshi ce shida bilkisu wai... Da Allah ne kadai yasan irin farin cikin da zai tsinci kansa aciki,

"Lafiya kuwa naganka babu ko waya?"

Kallonta yayi sai kuma ya girgiza kansa yana murmushi,

"Mutum bazai zo yaga matarshi ba saida wani abu?"

Duk da maganar ta ratsata amma saita dake ta sake kallonshi aranta tana cewa, "yaron nan naga yana nema ya zake dayawa fa"

"Uhmm? Ni kawai ji nayi ina son inganki saboda nakwana biyu bamuyi tozali da fuskokin juna ba... That's all"

"To nagode, yanzu dai ai gashi kaganni, inada dan uzuri agida wanda nakeyi sai kuma kafito dani"

"Nifa ko baki koreni ba dama tafiya zanyi amma kafin sannan, zan nemi alfarma"

"Allah yasa zan iya"

"Dan Allah pics dinki nakeso ki turo min, sannan ki daure kifara kulani online murinka chat"

"Pics kuma? Me zakayi da pics dina?"

Murmushi yasake yi yasauke hudah kasa sannan yazaro dubu daya ya danka mata a hannunta,

"Nidai kawai ki taimaka kibani babu ruwanki da abunda zanyi dashi... Shikenan nabarki lafiya, kizama cikin aminci da kwanciyar hankali"

Babur dinshi yabuga yayi gaba yayinda ita kuma tabishi da kallo,

"Jishi kamar wani babba sai zaro magana da iya shiryata"

Daukar hudah tayi tashiga cikin gida, kamar yadda ta tsammata su Hindu anbaje anata zuzuta haduwar da fahad yayi da kuma yaba hankalinsa ita dai batace uffan ba tawuce daki ta ajiye mayafinta tasake fitowa tana zama khulsum na shigowa, har lokacin su maama hirar fahad suke,

"A'a kaga amare"

Dariya sukayi gaba dayansu, meenah tace,

"Anty khulsum ai yanzu kune amare gashi nan sai budada kamshi kuke" takare maganar da yiwa khulsum alama da ido,

Saida Ammah tabar wurin bayan sun gaisa sannan ta maida hankalinta Kansu meenah,

"Wai me kukeso kuce minne? Wacece amaryar? Ni ko wa?"

Dariya mama tayi,

"Kar dai kice kema baki saniba?"

"Wai me kuke magana akaine? Menene ban saniba?"

"Maganar auren adda labour mana, anfa samata rana nanda 2 months bikinta ai ni nazaci ma anko kikazo fitarwa"

Gimtse fuska khulsum tayi ta kalli bilkisu,

"Lallai kawata, abin har yakai haka? Kullum muna tare dake amma shine kika kasa sanar dani maganar bikinki? Nagode"

Daga haka tamike zata tafi, janta daki bilkisu tasoma kokarin yi amma tana turjewa daga karshe dai saida su maama suka saka baki sannan tayarda suka shiga dakin,

"Kawata kiyi hakuri dan wallahi ni auren nan ganinshi nakeyi kamar da wasa..." Nan takwashe komai ta fada mata amma ta boye mata kudurin dake cikin zuciyarta

Dariya khulsum tayi tace,

"Nidama tunda naji yace wai ke zaiyiwa dinki ni bazai yimin ba nasan akwai wata akasa"

Kai mata duka bilkisu tayi tana cewa "bana son sharri malama"

"Allah dagaske guy din yana mutuwar sonki"

Sun dade tareda khulsum suna tsattsara abubuwa da dama domin hatta anko atake anan khulsum ta fitar dashi tace pink din net da blue din head yayinda ita kuma amarya zata saka blue din kaya da pink din head su Hindu murna suka shiga yi suna cewa wallahi yayi sosai ayi hakan ita dai jinsu takeyi bata tankawa domin tunaninta gaba daya yana ga hamood.

Shi dai ango shirinsa yake ba kama hannun yaro domin gidanshi har anyi roofing anyi wearing da komai yanzu fenti da saka kofofi dasu tiles yarage kudine ma ya yanke masa shiyasa aikin yatsaya. Kwana biyu atsakani ya dan kwanta zazzabi saboda baya samun zama yanzu ga dinkuna duk sunyi masa yawa danma yabaiwa hamza wasu yarage masa, har yayi dan zazzabinshi yagama bilkisu bata saniba domin ba waya sukeyi ba shine ma yake kiranta ita kuwa ba kiranshi takeyi ba saida dalili, ranar da yaji dan dama dama bayan sallar magrib yashirya yaje wurinta, yau kam a guest room aka saukeshi ba a compound ba kamar yadda aka saba domin yazo kenan abba kuma yadawo shine yabada umarnin akaishi guest room dinshi, har lokacin kanshi bai gama daina yimasa ciwo ba ga jikinsa babu wani karfi sosai, yana nan zaune Rabi ta kawo masa ruwa da juice da wani dan madaidaicin food flask, bai taba komaiba har gimbiyar tashigo tana sanye da milk colour din doguwar riga da mayafinta wannan fitinannen kamshin nata yana biye da ita, ayanda ya lura tana kaunar dogayen riguna sosai domin tafi sakasu fiyeda riga da skirt ko zani, har ya amsa sallamarta tanemi wuri ta zauna akujerar dake kallon tashi idonshi na kanta,

Yasan muddin idan bashine ya gaisheta ba to sai dai idan bazasu gaisa dinba shiyasa yakatse shirun da gaisheta, ta amsa kuwa fuskarta babu yabo babu fallasa,

Shagwabe murya yayi ya langabar da kai yana kallonta,

"Bawan Allahnnan har yayi zazzabinshi yagama baki saniba bare kiyi masa sannu.... Dama haka akeyi?"

"Ayya to aini ban saniba, baka fada minba"

"To ai baki nemeni ba, har yanzu ban gama warkewa ba, tabani kiji..."

Murmushi tayi ta dauke kai,

"Kai yarone, kuruciya na damunka wallahi akan me zan tabaka?"

Murmushin shima yayi,

"Au hakane yarintar? Shikenan"

"Kasan me? Maganar biki a ina zaka zauna ne?"

"A ina zamu zauna dai, can ne transformer uku sabuwar unguwar nan amma gidan bawani babba bane dai"

"Ba matsala indai dakunan sunkai biyu zuwa uku"

Gyara zamansa yayi yana kallonta,

"Daki dayane kwal..."

"Daki daya fa?"

"Ehh mana"

"Hmm lallai, to kai a ina zaka rinka kwana"

Dariya tambayar tabashi da kunya lokaci guda shiyasa ma baice komai ba, itama share maganar tayi kamar yadda yashare amma aranta cewa take,

"Ai kuwa yaro garama tun wuri kanemi wurin kwana amma banda inda nake"

Ganin lokacin sallar ishah yayi yasashi yi mata sallama domin tafiya, abubuwan da takawo masa baici ba tayi masa packaging dinsu tabishi dasu, bai musaba yakarba yatafi, yana zuwa gida dakinsu kawai yabude yasaka kayan aciki yayi alwala yawuce masallaci, bayan an idar tare da baba suka shigo gidan baba na tambayarshi abubuwan da yanzu ginin nashi ke bukata, kamar koda yaushe nan suka baje atsakar gida suka sha hirarsu har 9 nadare sannan yashiga daki bayan yarufe kofar gida. Wanka yafara yi sannan ya dauki sakon da bilkisu tabiyoshi dashi, farfesun kayan cikine yasha kayan kamshi da lemon kankana mai dankaren sanyi sai ruwa, duk da yasan zaiyi wuya ace itace ta girka amma yana fatan hakan shiyasa ma yazage ya cinye tas, saida ya dan zazzage cikinsa sannan ya kwanta, wayarshi yadauka yakunna recording din da yayi na programs dinta nan muryarta radau ta bayyana, haka yarinka bi daya bayan daya yana saurara.....

*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO.*

*KAMAR DA WASA...!*

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

*15*

*Kamar da wasa na siyarwa ne duk mai ra'ayin karantawa ta biya saita karanta, masu fitar min da book kuma kusani Allah yana ji kuma yana gani sannan yana jiran kowa a madakata*

****Akwana atashi alamari sai kara matsowa yake bilkisu ji take kamar tayi hauka domin har yau bata samu hamood ba amma tasawa ranta ko ranar dauren aure ne hamood yadawo mata tilas tafasa auren fahad ya aureshi, duk wasu shirye shirye tuni anfara su domin fita kunyar jama'a musamman ma bakin da za agayyata, su Hindu kuwa kusan kullum suna hanyar gidan abin nema yasamu, amaryar dai kawai tana binsu ne amma har cikin zuciyarta bata son wannan auren kawai dan dai ta gujewa jarabar iyallo da auren ya mudan ne.
Chapter 13 · 0% Book details