Sashe 39
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washe gari yafara fita lectures tun aranar yayi friends guda uku dama su ukune tun level one suke tare haidar da Bashir sai mukhtar shi dai fahad baya son hada kai da kowa a makarantar nan kamar yadda su ayiyah sukayi masa fada akan ya tsaya yayi abinda yakaishi sannan banda kula abokai barkatai domin hakan babu fa'ida acikinsa amma saboda yanda suka manne masa dole saida ya kulasu dukda yana jin tsoro domin yaga kamarsu yaran manyane shikuwa ba dan kowan kowa bane sai dai sam ko kadan su basu nuna masa hakanba domin aranar ma dakinsa suka bishi bayan sun fito daga lecture harda kokawa akan guntun snacks din dake cikin jarida a nannade wanda yarage shiyasa shima ba adauki wani lokaci mai tsawoba yasaki jikinsa dasu saboda yaga basuda wani mummunan hali basa shaye shaye basa iskanci basa komai shi dama dan shaye shaye ya tsana bazai taba iya abota dashiba.Kullum suna tare su hudunnan kamar wasu yan hudu shi mukhtar gidansu a abuja yake sukuma su bashir duk yan cikin Kaduna ne, duk lokacin da suka fito daga lecture sai dai su zauna suyita bacci adakin fahad ko kuma wani lokacin suyita buga games a wayoyinsu ko game din kati shiyasa fahad yafara kokarin nemarwa kansa mafita domin baya son zaman nan na asara shiyasa ya yanke shawarar fara zuwa shagon dinkin da yagani tsallaken gidan da yake zaune su mukhtar nata tsokanarshi suna cewa yana babban yaro amma shine zai je yana dinki? Shi dai cewa yayi ehh babu komai ai Sana'a ce saboda yasan basuda masaniyar irin kudin da yake samu ta hanyar dinkin nan shiyasa kwana biyu da baiyiba duk jinsa yake sai shankali hatta kafarshi kumbura takeyi ita kadai tana sabewa.
***
Tunda bilkisu tazauna acikin falonta bayan tafiyar Dr abrar takasa samun nutsuwa gaba daya jinta take kamar acikin mafarki, takasa zaune takasa tsaye sai kaiwa da komowa takeyi burinta kawai taga dawowar hamood cikin gidan ta zazzage masa abinda ke cikinta,
"Wannan ai cin amanane da mugunta, ni hamood zai yiwa wannan butulcin...? Ohh my God.... What a heartless..... Wannan wacce irin mugunta ce..."
Wasu hawayene ke kwaranya daga cikin idanuwanta mikewa tayi tawuce bedroom dinta tasoma hada kayanta gashi abin haushi akwatunanta ansace balle tazuba kayan aciki duk da hamood yayi mata dadin bakin wai zai siya mata wasu, haka dai taci gaba da zama amma babu hamood babu labarinsa tana ta kiran wayarshi kuma akashe har dare bai dawo gidanba sai wise ce tadawo gidan da misalin karfe 10 nadare ko kallonta bilkisu batayi ba amma itama yau kallo daya zaka yimata kagane ashirye take da ko wanne irin bala'i wanda mutum keji dashi, babu wanda ya tankawa wani wise tawuce bedroom dinta wanda ke falon kasa sam hakan bai damu bilkisu ba ayau domin yanzu ita ba ta wasila takeba ta hamood takeyi so take yazo gidan ta kare masa tanadi amma abin takaici da bacin rai bai dawo gidanba har 12 nadare har lokacin bilkisu bata runtsa ba tana jiran taga ta inda hamood zai bullo anan falon ta kwana har asubah dama tunda tazauna bata tashi sai dai idan salla zatayi.
Safiyar ranar da misalin karfe goma tana zaune tana zaman jiran tsammani domin bata son tatafi gida tasake dawowa tafiso tatafi gaba daya da takardar sakinta ko wani abu mai kamada haka, ga kayanta nan agefe wadanda ta shirya domin tafiya dasu, akan idonta wise tafito tashiga kitchen ta dafo indomie tazo takoma daki, har takosa da zaman tana shirin tafiya inyaso sayita su kare awaya taji dirin shigowar motarsa, mikewa tsaye tayi ta rike kugu tayi tsayuwar ashirye nake da duk abinda mutum yazo dashi tana jijjiga kamar ansaka mata wayar wuta masiface rubuce kan fuskarta ahaka hamood yabude kofa yashigo ya isketa.....
*_Ummi Shatu_*
36***Tunda hamood yashigo ta dauke kai tamayar dashi gefe daya ganin haka yasashi shima hade rai yadaure fuska kamar bai taba dariya ba,
"Macuci.... Azzalumi..... Mugu to Allah ya toni asirinka....yanzu dama hamood kasan kana dauke da kwayar cutar HIV amma shine ka aureni ahaka har kake burin hada shimfida dani?"
Wani mugun kallo ya watsa mata sannan yazare farin tabaran dake sanye cikin idonsa, zama yayi kan kujera ya dora daya kan daya yana watsa mata kallon dake kara tafarfasa ranta,
"To sai me dan na aureki ina dauke da HIV? Bake kika manne min kika like min akan dole sai na aureki ba? Karfa ki manta har aurenki kika kashe dan kawai in aureki in zauna dake...."
"Ya isa haka malam.... Ai duk wadannan abhbuwan dakake ikararin cewar na aikata na aikatane acikin rashin sani... Kuma ina nadamar hakan ahalin yanzu, wallahi hamood kaci amanata kuma ka zalunceni wanda bazan taba yafe maka ba har abada.... Sannan ka gaggauta sallamata domin gidan ubana zan tafi insha Allah nagama zama dakai...."
Wata shakiyiyar dariya yasaki irin wacce ke dauke da mugunta tsantsa aciki sannan yayi mata kallon uku ahu,
"U are such an idiot mai gado, sai yanzu nasan bakida tunani sam.... Hmmmm to idan ke shashasha ce ni mai hankaline... Bazan taba sakinki ba koda kuwa za amaimaita yakin duniya akaro na uku.... And lastly abinda zan fada miki shine u should mind ur tongue kisan irin maganar da zaki rinka fada min idan bahaka ba jikinki zai rinka gaya miki....."
Yana kokarin mikewa taje tasha gabansa cikeda masifa da tashin hankali,
"Wallahi hamood koda baka sakeni ta dadin rai ba to yazama wajibi ka sakeni ta dolen dole koda kuwa agaban kotu ne domin nagama zama da macuci,mayaudari, mashayi kuma mazinaci... Ko kana tsammanin har yanzu ban san irin kazamar rayuwar da kuke yi kaida waccan karuwar ba? To Allah yagama tonar asirinku dan haka kasakeni kuma kabani kudina naira dubu dari biyar wanda abbana yabani kai kuma ka lallabani ka kwace....."
Tafa hannaye wasila tashiga yi wacce fitowarta kenan daga cikin daki,
"My dear yanzu kana tsaye kanajin abinda wannan mahaukaciyar take fada maka amma shine bazaka dauki mataki ba?"
Tun kafin wise tarufe baki hamood ya dauke bilkisu da wani gigitaccen mari wanda yayi barazanar makantar da ita, zafin marin yasa bilkisu sake daga murya tana furta,
"Allah ya isana macuci azzalumi kuma wlhi sai ka bani kudina sannan dolenka ka sakeni...."
"Banza yar gidan matsiyata ni zaki yiwa sharrin na karbar miki kudinki? Uban me uban naki yake dashi da har zan karba? Saki kuma bazan yiba ko kin zaci nima irin wannan sakaran yaronne da zan sakeki aduk lokacin da kikaso? Koda zan sake ki yazama dole inmore sadakina dan haka sai kishirya daukar kwayar cutar HIV...."
Tun kafin yakarasa bilkisu ta dadimeshi tana kuka,
"Ni ba yar matsiyata bace sai dai idan kaine dan matsiyata kuma wallahi daga yau nagama zama dakai...."
Wani marin yasake bata sannan yashiga dukanta babu ji ba gani har saida takai kasa lokacin ne yafara ball da ita yana nausa mata kafa aciki, kuka bilkisu takeyi tana ihun neman dauki ganin yana kokarin kasheta yasa wise zuwa tana kokarin hanashi amma yahaukace kwata kwata bayaji bare gani,
"Nashiga uku hamood ka kusa kasheta... Kar kayi kisan kai kaga yanda takeyi fa... Kabarta haka"
Shine abinda wise keta fada amma hamood yaki saurararta ganin haka yasata sulalewa daga gidan tagudu tun kafin hamood yakashe bilkisu azo tafiya dashi ahada harda ita.
Bilkisu kam tajima da fita daga cikin hayyacinta sakamakon na jakin da hamood ya lakada mata abu na karshe da zata iya tunawa shine taji hamood ya gwarata da kujera ta fadi akan hannunta na hagu wanda take awurin wani azababben zafi ya ziyarceta, cikin azababben ciwon kai take bude idanuwanta ahankali wadanda suka kumbura suntum sakamakon uban bugun da suka sha,
Ammah ce da meenah zaune acikin dakin wanda ko ba afada mata ba tasan asibitine domin ga alamu nan sun nuna hakan, ga ruwa nan ana kara mata a hannunta na dama sannan hannun hagun ta kuma an daddaureshi dasu bandeji alamun dori,
Wasu hawayen nadama ne suka zubo daga cikin idanuwanta, ganin ta dan motsa yasa ammah da meenah azamar tasowa dukkaninsu Wanda har bakinsu na haduwa wurin yimata sannu,
"Sannu mai gado..." Inji ammah,
Kai ta dan daga cikin azabar ciwo ta rinka binsu ammah daya bayan daya da kallo kamar yau tafara ganinsu. Bata iya cewa komai ba sai ciccije baki da takeyi sakamakon ciwon da dukkanin jikinta keyi mata musamman ma hannunta na hagu,
"Sannu adda labour.... Allah yatashi kafadunki"
Dagawa meenah kai tayi tana cije baki hawaye na kwaranya daga cikin idanuwanta ahaka su maama suka shigo itada Hindu,maama na dauke da sultan ita kuma Hindu tana goye da meenal abayanta sai hudah wadda hannunta ke rike da nata, cikin zuciyarta take wani irin kuka mai tsuma rai saboda ganinsu mama da 'yayayensu yasake fama mata raunin da take fama dashi, su gasu da yaransu agidan mazajensu cikin walwala da kwanciyar hankali amma ita tanata shiga cikin runtsin rayuwa,
"Allah ka gafarta min... Allah natuba... Astagfirullah..." Shine abinda taketa fada cikin zuciyarta, jinta take ta tsani hamood ta tsani duk wani namiji mai irin halinsa ahalin yanzu,
"Allah ya isa..." Shine abinda lebanta suka furta amma babu wanda yaji, cikin tausayawa da jimami maama da hindu suka karaso gaban gadon su dinma kamar zasuyi kuka,
"Sannu Adda.... Sannu... Sai Allah yasaka miki insha Allah" inji mamaa,
"Kuma inbanda zurfin ciki irin na Adda labour bata fa taba fadar irin zaman da sukeyi ba bare tafadi cewar yana dukanta..." Hindu tafada tana kokarin zama agefen gadon,
"Ni dama tun jimawa wallahi na fuskanci akwai matsala kugafa irin ramar da tayi har iyallo ke cewa ciki ne..." Meenah itama dake tsaye kusa da amma ta tofa nata,
***
Tunda bilkisu tazauna acikin falonta bayan tafiyar Dr abrar takasa samun nutsuwa gaba daya jinta take kamar acikin mafarki, takasa zaune takasa tsaye sai kaiwa da komowa takeyi burinta kawai taga dawowar hamood cikin gidan ta zazzage masa abinda ke cikinta,
"Wannan ai cin amanane da mugunta, ni hamood zai yiwa wannan butulcin...? Ohh my God.... What a heartless..... Wannan wacce irin mugunta ce..."
Wasu hawayene ke kwaranya daga cikin idanuwanta mikewa tayi tawuce bedroom dinta tasoma hada kayanta gashi abin haushi akwatunanta ansace balle tazuba kayan aciki duk da hamood yayi mata dadin bakin wai zai siya mata wasu, haka dai taci gaba da zama amma babu hamood babu labarinsa tana ta kiran wayarshi kuma akashe har dare bai dawo gidanba sai wise ce tadawo gidan da misalin karfe 10 nadare ko kallonta bilkisu batayi ba amma itama yau kallo daya zaka yimata kagane ashirye take da ko wanne irin bala'i wanda mutum keji dashi, babu wanda ya tankawa wani wise tawuce bedroom dinta wanda ke falon kasa sam hakan bai damu bilkisu ba ayau domin yanzu ita ba ta wasila takeba ta hamood takeyi so take yazo gidan ta kare masa tanadi amma abin takaici da bacin rai bai dawo gidanba har 12 nadare har lokacin bilkisu bata runtsa ba tana jiran taga ta inda hamood zai bullo anan falon ta kwana har asubah dama tunda tazauna bata tashi sai dai idan salla zatayi.
Safiyar ranar da misalin karfe goma tana zaune tana zaman jiran tsammani domin bata son tatafi gida tasake dawowa tafiso tatafi gaba daya da takardar sakinta ko wani abu mai kamada haka, ga kayanta nan agefe wadanda ta shirya domin tafiya dasu, akan idonta wise tafito tashiga kitchen ta dafo indomie tazo takoma daki, har takosa da zaman tana shirin tafiya inyaso sayita su kare awaya taji dirin shigowar motarsa, mikewa tsaye tayi ta rike kugu tayi tsayuwar ashirye nake da duk abinda mutum yazo dashi tana jijjiga kamar ansaka mata wayar wuta masiface rubuce kan fuskarta ahaka hamood yabude kofa yashigo ya isketa.....
*_Ummi Shatu_*
36***Tunda hamood yashigo ta dauke kai tamayar dashi gefe daya ganin haka yasashi shima hade rai yadaure fuska kamar bai taba dariya ba,
"Macuci.... Azzalumi..... Mugu to Allah ya toni asirinka....yanzu dama hamood kasan kana dauke da kwayar cutar HIV amma shine ka aureni ahaka har kake burin hada shimfida dani?"
Wani mugun kallo ya watsa mata sannan yazare farin tabaran dake sanye cikin idonsa, zama yayi kan kujera ya dora daya kan daya yana watsa mata kallon dake kara tafarfasa ranta,
"To sai me dan na aureki ina dauke da HIV? Bake kika manne min kika like min akan dole sai na aureki ba? Karfa ki manta har aurenki kika kashe dan kawai in aureki in zauna dake...."
"Ya isa haka malam.... Ai duk wadannan abhbuwan dakake ikararin cewar na aikata na aikatane acikin rashin sani... Kuma ina nadamar hakan ahalin yanzu, wallahi hamood kaci amanata kuma ka zalunceni wanda bazan taba yafe maka ba har abada.... Sannan ka gaggauta sallamata domin gidan ubana zan tafi insha Allah nagama zama dakai...."
Wata shakiyiyar dariya yasaki irin wacce ke dauke da mugunta tsantsa aciki sannan yayi mata kallon uku ahu,
"U are such an idiot mai gado, sai yanzu nasan bakida tunani sam.... Hmmmm to idan ke shashasha ce ni mai hankaline... Bazan taba sakinki ba koda kuwa za amaimaita yakin duniya akaro na uku.... And lastly abinda zan fada miki shine u should mind ur tongue kisan irin maganar da zaki rinka fada min idan bahaka ba jikinki zai rinka gaya miki....."
Yana kokarin mikewa taje tasha gabansa cikeda masifa da tashin hankali,
"Wallahi hamood koda baka sakeni ta dadin rai ba to yazama wajibi ka sakeni ta dolen dole koda kuwa agaban kotu ne domin nagama zama da macuci,mayaudari, mashayi kuma mazinaci... Ko kana tsammanin har yanzu ban san irin kazamar rayuwar da kuke yi kaida waccan karuwar ba? To Allah yagama tonar asirinku dan haka kasakeni kuma kabani kudina naira dubu dari biyar wanda abbana yabani kai kuma ka lallabani ka kwace....."
Tafa hannaye wasila tashiga yi wacce fitowarta kenan daga cikin daki,
"My dear yanzu kana tsaye kanajin abinda wannan mahaukaciyar take fada maka amma shine bazaka dauki mataki ba?"
Tun kafin wise tarufe baki hamood ya dauke bilkisu da wani gigitaccen mari wanda yayi barazanar makantar da ita, zafin marin yasa bilkisu sake daga murya tana furta,
"Allah ya isana macuci azzalumi kuma wlhi sai ka bani kudina sannan dolenka ka sakeni...."
"Banza yar gidan matsiyata ni zaki yiwa sharrin na karbar miki kudinki? Uban me uban naki yake dashi da har zan karba? Saki kuma bazan yiba ko kin zaci nima irin wannan sakaran yaronne da zan sakeki aduk lokacin da kikaso? Koda zan sake ki yazama dole inmore sadakina dan haka sai kishirya daukar kwayar cutar HIV...."
Tun kafin yakarasa bilkisu ta dadimeshi tana kuka,
"Ni ba yar matsiyata bace sai dai idan kaine dan matsiyata kuma wallahi daga yau nagama zama dakai...."
Wani marin yasake bata sannan yashiga dukanta babu ji ba gani har saida takai kasa lokacin ne yafara ball da ita yana nausa mata kafa aciki, kuka bilkisu takeyi tana ihun neman dauki ganin yana kokarin kasheta yasa wise zuwa tana kokarin hanashi amma yahaukace kwata kwata bayaji bare gani,
"Nashiga uku hamood ka kusa kasheta... Kar kayi kisan kai kaga yanda takeyi fa... Kabarta haka"
Shine abinda wise keta fada amma hamood yaki saurararta ganin haka yasata sulalewa daga gidan tagudu tun kafin hamood yakashe bilkisu azo tafiya dashi ahada harda ita.
Bilkisu kam tajima da fita daga cikin hayyacinta sakamakon na jakin da hamood ya lakada mata abu na karshe da zata iya tunawa shine taji hamood ya gwarata da kujera ta fadi akan hannunta na hagu wanda take awurin wani azababben zafi ya ziyarceta, cikin azababben ciwon kai take bude idanuwanta ahankali wadanda suka kumbura suntum sakamakon uban bugun da suka sha,
Ammah ce da meenah zaune acikin dakin wanda ko ba afada mata ba tasan asibitine domin ga alamu nan sun nuna hakan, ga ruwa nan ana kara mata a hannunta na dama sannan hannun hagun ta kuma an daddaureshi dasu bandeji alamun dori,
Wasu hawayen nadama ne suka zubo daga cikin idanuwanta, ganin ta dan motsa yasa ammah da meenah azamar tasowa dukkaninsu Wanda har bakinsu na haduwa wurin yimata sannu,
"Sannu mai gado..." Inji ammah,
Kai ta dan daga cikin azabar ciwo ta rinka binsu ammah daya bayan daya da kallo kamar yau tafara ganinsu. Bata iya cewa komai ba sai ciccije baki da takeyi sakamakon ciwon da dukkanin jikinta keyi mata musamman ma hannunta na hagu,
"Sannu adda labour.... Allah yatashi kafadunki"
Dagawa meenah kai tayi tana cije baki hawaye na kwaranya daga cikin idanuwanta ahaka su maama suka shigo itada Hindu,maama na dauke da sultan ita kuma Hindu tana goye da meenal abayanta sai hudah wadda hannunta ke rike da nata, cikin zuciyarta take wani irin kuka mai tsuma rai saboda ganinsu mama da 'yayayensu yasake fama mata raunin da take fama dashi, su gasu da yaransu agidan mazajensu cikin walwala da kwanciyar hankali amma ita tanata shiga cikin runtsin rayuwa,
"Allah ka gafarta min... Allah natuba... Astagfirullah..." Shine abinda taketa fada cikin zuciyarta, jinta take ta tsani hamood ta tsani duk wani namiji mai irin halinsa ahalin yanzu,
"Allah ya isa..." Shine abinda lebanta suka furta amma babu wanda yaji, cikin tausayawa da jimami maama da hindu suka karaso gaban gadon su dinma kamar zasuyi kuka,
"Sannu Adda.... Sannu... Sai Allah yasaka miki insha Allah" inji mamaa,
"Kuma inbanda zurfin ciki irin na Adda labour bata fa taba fadar irin zaman da sukeyi ba bare tafadi cewar yana dukanta..." Hindu tafada tana kokarin zama agefen gadon,
"Ni dama tun jimawa wallahi na fuskanci akwai matsala kugafa irin ramar da tayi har iyallo ke cewa ciki ne..." Meenah itama dake tsaye kusa da amma ta tofa nata,