Sashe 38
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Mata? Mata kuma? Tayaya wasila tazama matarsa? Sai dai ko farkarsa...."
Ai tun kafin ya karasa bilkisu take jin jiri yana daukarta abu biyune suka taru suka dagula mata lissafi awannan lokacin nafarko jin wai hamood yanada HIV na biyu kuma jin wai wasila karuwarsa ce, sama sama take jin bayanin likita amma tunda jimawa tadaina fuskantar komai maganin tasa hannu ta karba daga nan tawuce ciki jiri yana cigaba da daukarta ko sallamar da yake yimata bataji.
***
Cikin nasara admission dinsu fahad yafito kuma yasamu inda suka bashi BSC laboratory level 200 saboda result dinshi na diploma yayi masifar kyau dan da distinction yafita kuma SLT ya karanta shiyasa, shi anasa zabin ma pharmacy yaso subashi yadora amma suka bashi laboratory dole babu yadda ya iya hakan zai daure ya karanci lab din,babu bata lokaci yashirya yaje ya karbo admission letter dinshi, har makaranta ya kaiwa husnah tagani tayi congratulating dinshi, suna tare yaya Baffa yayan salim yayi masa waya wai yazo ya sameshi agida, sallama yayiwa husnah yahau Babur dinshi yatafi yana zuwa yaya baffa ke sanar dashi wai wasu turawa ne zasu karbi hayar gidansa idan har zai basu zasuyi aiki na shekara daya agarinne kuma a wannan area din suke son gidan, baba fahad yakira awaya ya sanar masa babu bata lokaci baba ya amince shima fahad baida zabin da yawuce ya amince din, cikin kwanaki biyu aka gama komai aka bawa turawa gida suka hau gyarashi,kudi mai yawan gaske suka biya aka sakawa fahad cikin account dinsa. Da wadannan kudin yadiba yaje yayi registration ya kama hayar dakin da zai zauna anan opposite din makarantar wanda ya kasance private hostel na manyan yara shi dinma a babban yaron yafito bayan yagama registration yakoma gida zaije yashiryo yadawo saboda nanda yan kwanaki za afara lectures.
*_Ummi Shatu_*
*Wannan littafin na siyarwa ne,me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
35***Babu bata lokaci fahad ya kammala shirye shiryensa na tafiya makaranta domin shi aburinsa idan yatafi bazai dawo gidaba sai semester ta kare, duk abubuwan da zai bukata ya tanadi kudinsu domin acewarsa baya so ya debi kaya daga nan kano har zuwa kaduna wai za arainashi yafi son sai yaje can sannan yasiyi komai, anan gida dai ayiyah da mamuh sunyi masa jar miya cikin plastic da dakakken jan yaji mai daukeda tafarnuwa wai dan adan saukaka masa yayinda su anty Fauziyya suka yimasa snacks. Ana igobe zai tafi yaje gidajen yan uwansa duk yayi musu sallama shida salim bayan sallar ishah suka dawo gida bai samu ganin husnah ba a wannan dare domin ka'idar makarantarsu karfe 6 ake rufewa, shiyasa yabari sai washe gari da safe zaije ganinta before yawuce.
Lamo yayi kwance bisa katifarsa yana sake sake acikin ransa wato gaba daya rayuwar nanma jarrabawace acikinta da gaibu saboda duk yadda kakai ga shiryawa kanka rayuwa baka taba sanin abinda zai faru gobe komai iya hasashenka shidai koda wasa bai taba kawowa zai yi soyayyar aure da husnah ba asalima kallon mai dan tabin hankali yake yimata ada amma yanzu duk da bajin sonta yakeyi acikin ransa ba tana da wani muhimmanci agareshi, bilkisu dai insha Allah yamanta da ita koda kuwa hakan zaisa ya dawwama acikin bakin ciki da damuwa. Washe gari kamar yadda ya tsara bayan yagama shiryawa cikin kananan kaya bakin jeans da t shirt din polo yellow, hatta takalmin da yasaka na kamfanin polo ne da p cap, gidansu salim yaje yayiwa mamansu sallama sannan suka wuce wurin husnah tare, kasancewar weekend ne bata da class shiyasa da personal tafito tasha yellow din atamfa mai zanen kwarya, tana karasowa salim yafara tsokanarsu,
"Kaga amarya da ango.... Wato tsabar ma zuciyoyinku anko suke da juna shine harda saka kaya kala daya...."
Murmushi fahad yayi itama haka amma batace komai ba sai fahad ne ya mayar masa da martani,
"Kasan aduk lokacin da masoya suka shaku da juna to komai nasu rikidewa yake yakoma iri daya shiyasa sai ka gansu tamkar wasu yan biyu... Ni bakaga har wani kama mukeyi da ita ba.... Ko husnah ta? Ai kamarmu daya ko?"
Dariya tayi tarufe fuska tana fadin,
"A'a ya fahad wallahi kafini kyau..."
Dariya yayi yana kallon wani wuri,
"To ai kinfini haske Asma'u kuma ma dai kamar tamu daya..."
"Kana dai kawai tsokana tane fa..." Tafada cikin shagwaba,
"To kuma meye abun turo min bakin? Ko kina son inbaki goodbye kiss ne...."
Dariya tayi ta juya masa baya,
"Nidai bana so..."
"Nima bance kina so ba kawai tambayace yan matanah...."
Shidai salim ashe yajima da sulalewa yabasu wuri yana can zaune gaban wata bishiya mai dauke da benci a karkashinta,
"Ya fahad dan Allah idan katafi karka manta dani.... Karka maye gurbina da wata... Wallahi idan kayi min haka zan iya rasa raina..."
Saida ya matsa kusa da ita sannan yafara yimata magana kasa kasa cikin alamun rarrashi da tarairaya,
"Haba husnah ai ko amafarki bazan taba mantawa dake ba.... Kina da wani babban bangare acikin zuciyata, kisa aranki akoda yaushe kina cikin zuciyata kuma insha Allah bazan taba zama sanadiyyar rasa rayuwarki ba domin zan baki kulawa zan sadaukar miki da lokutana aduk lokacin da kika bukaci hakan.... Amma kin san me? Karfa nima ina tafiya kiyi min kishiya...."
Murmushi tayi kwalla tana ciko idanuwanta,
"Ya fahad only u, kasa wannan aranka nice dai nake tsoron yanmatan Jami'a kar inje ina nan wata ta kwace min kai...."
"Husnah no need to worry about that....saboda ni wallahi tsoron mata nakeyi yanzu.... Karki dauka da wasafa... Seriously tsoron mata nake ayanzu dai...."
Kallonta yayi yanda take hawaye dagaske tana gogewa,
"To menene wai na kukanne?? Idan bakya son natafi shikenan sai infasa karatun husnah indai hakan zai saki farin ciki..."
Girgiza kai tayi tana share hawaye,
"A'a ya fahad kaje, Allah yabasa sa'a.... Sai munyi waya"
Daga haka tajuya tatafi yasan wani kukan takeyi wanda bata son yagani duk kuma sai yaji wani irin tausayinta yana shigarshi, shida yazo suyi sallama amma gashi tatafi da kuka ko sallamar ma bata bari sunyi ba.
"Allah sarki husnah Allah yabani ikon faranta miki...."
"Amin" salim ya amsa wanda karasowarsa wurin kenan, dafa kafadar fahad yayi yahau bayan Babur din yana cewa,
"Rabuwar masoya tana zafi gashi ku baku sababa....."
"Dallah can... Meye hakan"
"Ahh waka ce mana nake yimuku... Allah sarki husnah..."
Buga Babur din fahad yayi suka fita sai da suka bar kofar makarantar sannan yace da salim,
"Salim wallahi husnah tausayi take bani... Ina tsoron kar zuciyarta tashiga wani hali saboda soyayyata kamar yadda tawa zuciyar ta tsinci kanta sakamakon halin da bilk....."
Sai kuma yayi shiru domin baya son tunata baya kaunar tunawa da ko sunan bilkisu arayuwarsa domin abinda yafaru tsakaninsu shine abu mafi muni da ya taba faruwa dashi wanda baya jin zai iya mantawa,
"To ai indai zaka danne zuciyarka kanuna mata soyayya ka riketa da gaskiya bazata taba shiga halin da kake tsoron shigarta ba...."
"Zan kokarta insha Allah i will try my best to makes her happy,lovely and even special... I will for eva care for her"
Dariya salim yayi,
"Ai nasan zaka iya... Lover boy"
Da hirar husnah a bakunansu sukaje gidansu fahad yayi sallama dasu ayiyah har baba ma yana nan yana jiran tafiyarsa bai fitaba sai lokacin yake jin kamar zaiyi kuka, su maryam kam kukan suke tayi kamar anyi musu mutuwa shiyasa shima saida yaji kwalla na shirin zubo masa da koke koke dai yadau kayanshi yatafi shida salim wanda zaiyi masa rakiya har inda zai hau motar Kaduna.
Bayan sallar azahar yashiga kaduna, dakinsa wanda yakama yaje ya shirya kayansa yaci snacks ya kwanta domin hutawa duk da yana son shiga kasuwa yasiyo abubuwan da yake bukata na amfainin yau da kullum da kayan abinci. Zuwa dare ya kammala komai yagyare dakinsa tsaf ya siyo duk abubuwan da yake bukata, kwanciya yayi kan katuwar katifarsa ya bararraje ya kira gida saida suka gaisa da kowa na gidan sannan yakira ya abba shima suka dan taba hira sannan yakira husnah daga karshe ita kam hira suka sha sosai domin har 10 da wani abun domin shagwabar da yasaba yaketa zuba mata,
"Ko inje infadawa baba adaura mana aure akawoki nan mu zauna.... Ni kin san bana son harkar yunwa gashi bana son yin girki da kaina...."
"Ka rinka zuwa captaria kana ci mana..."
"Yanmatanah abincin saidawa farin maggi suke sakawa nikuma bana so idan naci sai nayi amai...." Yakarashe maganar cikin shagwaba, dariya husnah tayi,
"Ya fahad kaifa dadina dakai shagwaba...."
"Kin manta ni dan auta ne? Komai ayiyah tasamu ni take baiwa fa...."
"Su Mariya fa? Basune auta ba?"
"Ke wadannan fa "yayana ne, yaran sister nane..."
"Badai 'yayanka ba,'yayan Anty dai.... Kai ai tukunnah..."
Dariya yayi ya lumshe idanuwanshi,
"To me kike ci na baka na zuba..., nima din kwana nawane muna yin aure zaki haifo yan biyu kafin shekara ta zagayo...."
"Wai wai... Lallai ya fahad, yauwa dama inaso in tambayeka wai dan Allah...."
Jin tayi shiru yasashi bude idanuwansa,
"Menene? Go on ina jinki..."
"Wai meya rabaku da matarka"
"Husnah dan Allah kar muyi wannan maganar saboda ciwona zai iya tashi kinga nasamu kwana biyun nan yasauka...."
"Shikenan ya fahad insha Allah bazan sake yimaka magana kwatankwacin irin wannan ba,Allah yakara maka lafiya..."
"Thank you husnah"
Sun jima suna hira daga bisani sukayi sallama kowa zuciyarsa fari tass saboda dadadan kalaman da suka fadawa juna.
Ai tun kafin ya karasa bilkisu take jin jiri yana daukarta abu biyune suka taru suka dagula mata lissafi awannan lokacin nafarko jin wai hamood yanada HIV na biyu kuma jin wai wasila karuwarsa ce, sama sama take jin bayanin likita amma tunda jimawa tadaina fuskantar komai maganin tasa hannu ta karba daga nan tawuce ciki jiri yana cigaba da daukarta ko sallamar da yake yimata bataji.
***
Cikin nasara admission dinsu fahad yafito kuma yasamu inda suka bashi BSC laboratory level 200 saboda result dinshi na diploma yayi masifar kyau dan da distinction yafita kuma SLT ya karanta shiyasa, shi anasa zabin ma pharmacy yaso subashi yadora amma suka bashi laboratory dole babu yadda ya iya hakan zai daure ya karanci lab din,babu bata lokaci yashirya yaje ya karbo admission letter dinshi, har makaranta ya kaiwa husnah tagani tayi congratulating dinshi, suna tare yaya Baffa yayan salim yayi masa waya wai yazo ya sameshi agida, sallama yayiwa husnah yahau Babur dinshi yatafi yana zuwa yaya baffa ke sanar dashi wai wasu turawa ne zasu karbi hayar gidansa idan har zai basu zasuyi aiki na shekara daya agarinne kuma a wannan area din suke son gidan, baba fahad yakira awaya ya sanar masa babu bata lokaci baba ya amince shima fahad baida zabin da yawuce ya amince din, cikin kwanaki biyu aka gama komai aka bawa turawa gida suka hau gyarashi,kudi mai yawan gaske suka biya aka sakawa fahad cikin account dinsa. Da wadannan kudin yadiba yaje yayi registration ya kama hayar dakin da zai zauna anan opposite din makarantar wanda ya kasance private hostel na manyan yara shi dinma a babban yaron yafito bayan yagama registration yakoma gida zaije yashiryo yadawo saboda nanda yan kwanaki za afara lectures.
*_Ummi Shatu_*
*Wannan littafin na siyarwa ne,me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
35***Babu bata lokaci fahad ya kammala shirye shiryensa na tafiya makaranta domin shi aburinsa idan yatafi bazai dawo gidaba sai semester ta kare, duk abubuwan da zai bukata ya tanadi kudinsu domin acewarsa baya so ya debi kaya daga nan kano har zuwa kaduna wai za arainashi yafi son sai yaje can sannan yasiyi komai, anan gida dai ayiyah da mamuh sunyi masa jar miya cikin plastic da dakakken jan yaji mai daukeda tafarnuwa wai dan adan saukaka masa yayinda su anty Fauziyya suka yimasa snacks. Ana igobe zai tafi yaje gidajen yan uwansa duk yayi musu sallama shida salim bayan sallar ishah suka dawo gida bai samu ganin husnah ba a wannan dare domin ka'idar makarantarsu karfe 6 ake rufewa, shiyasa yabari sai washe gari da safe zaije ganinta before yawuce.
Lamo yayi kwance bisa katifarsa yana sake sake acikin ransa wato gaba daya rayuwar nanma jarrabawace acikinta da gaibu saboda duk yadda kakai ga shiryawa kanka rayuwa baka taba sanin abinda zai faru gobe komai iya hasashenka shidai koda wasa bai taba kawowa zai yi soyayyar aure da husnah ba asalima kallon mai dan tabin hankali yake yimata ada amma yanzu duk da bajin sonta yakeyi acikin ransa ba tana da wani muhimmanci agareshi, bilkisu dai insha Allah yamanta da ita koda kuwa hakan zaisa ya dawwama acikin bakin ciki da damuwa. Washe gari kamar yadda ya tsara bayan yagama shiryawa cikin kananan kaya bakin jeans da t shirt din polo yellow, hatta takalmin da yasaka na kamfanin polo ne da p cap, gidansu salim yaje yayiwa mamansu sallama sannan suka wuce wurin husnah tare, kasancewar weekend ne bata da class shiyasa da personal tafito tasha yellow din atamfa mai zanen kwarya, tana karasowa salim yafara tsokanarsu,
"Kaga amarya da ango.... Wato tsabar ma zuciyoyinku anko suke da juna shine harda saka kaya kala daya...."
Murmushi fahad yayi itama haka amma batace komai ba sai fahad ne ya mayar masa da martani,
"Kasan aduk lokacin da masoya suka shaku da juna to komai nasu rikidewa yake yakoma iri daya shiyasa sai ka gansu tamkar wasu yan biyu... Ni bakaga har wani kama mukeyi da ita ba.... Ko husnah ta? Ai kamarmu daya ko?"
Dariya tayi tarufe fuska tana fadin,
"A'a ya fahad wallahi kafini kyau..."
Dariya yayi yana kallon wani wuri,
"To ai kinfini haske Asma'u kuma ma dai kamar tamu daya..."
"Kana dai kawai tsokana tane fa..." Tafada cikin shagwaba,
"To kuma meye abun turo min bakin? Ko kina son inbaki goodbye kiss ne...."
Dariya tayi ta juya masa baya,
"Nidai bana so..."
"Nima bance kina so ba kawai tambayace yan matanah...."
Shidai salim ashe yajima da sulalewa yabasu wuri yana can zaune gaban wata bishiya mai dauke da benci a karkashinta,
"Ya fahad dan Allah idan katafi karka manta dani.... Karka maye gurbina da wata... Wallahi idan kayi min haka zan iya rasa raina..."
Saida ya matsa kusa da ita sannan yafara yimata magana kasa kasa cikin alamun rarrashi da tarairaya,
"Haba husnah ai ko amafarki bazan taba mantawa dake ba.... Kina da wani babban bangare acikin zuciyata, kisa aranki akoda yaushe kina cikin zuciyata kuma insha Allah bazan taba zama sanadiyyar rasa rayuwarki ba domin zan baki kulawa zan sadaukar miki da lokutana aduk lokacin da kika bukaci hakan.... Amma kin san me? Karfa nima ina tafiya kiyi min kishiya...."
Murmushi tayi kwalla tana ciko idanuwanta,
"Ya fahad only u, kasa wannan aranka nice dai nake tsoron yanmatan Jami'a kar inje ina nan wata ta kwace min kai...."
"Husnah no need to worry about that....saboda ni wallahi tsoron mata nakeyi yanzu.... Karki dauka da wasafa... Seriously tsoron mata nake ayanzu dai...."
Kallonta yayi yanda take hawaye dagaske tana gogewa,
"To menene wai na kukanne?? Idan bakya son natafi shikenan sai infasa karatun husnah indai hakan zai saki farin ciki..."
Girgiza kai tayi tana share hawaye,
"A'a ya fahad kaje, Allah yabasa sa'a.... Sai munyi waya"
Daga haka tajuya tatafi yasan wani kukan takeyi wanda bata son yagani duk kuma sai yaji wani irin tausayinta yana shigarshi, shida yazo suyi sallama amma gashi tatafi da kuka ko sallamar ma bata bari sunyi ba.
"Allah sarki husnah Allah yabani ikon faranta miki...."
"Amin" salim ya amsa wanda karasowarsa wurin kenan, dafa kafadar fahad yayi yahau bayan Babur din yana cewa,
"Rabuwar masoya tana zafi gashi ku baku sababa....."
"Dallah can... Meye hakan"
"Ahh waka ce mana nake yimuku... Allah sarki husnah..."
Buga Babur din fahad yayi suka fita sai da suka bar kofar makarantar sannan yace da salim,
"Salim wallahi husnah tausayi take bani... Ina tsoron kar zuciyarta tashiga wani hali saboda soyayyata kamar yadda tawa zuciyar ta tsinci kanta sakamakon halin da bilk....."
Sai kuma yayi shiru domin baya son tunata baya kaunar tunawa da ko sunan bilkisu arayuwarsa domin abinda yafaru tsakaninsu shine abu mafi muni da ya taba faruwa dashi wanda baya jin zai iya mantawa,
"To ai indai zaka danne zuciyarka kanuna mata soyayya ka riketa da gaskiya bazata taba shiga halin da kake tsoron shigarta ba...."
"Zan kokarta insha Allah i will try my best to makes her happy,lovely and even special... I will for eva care for her"
Dariya salim yayi,
"Ai nasan zaka iya... Lover boy"
Da hirar husnah a bakunansu sukaje gidansu fahad yayi sallama dasu ayiyah har baba ma yana nan yana jiran tafiyarsa bai fitaba sai lokacin yake jin kamar zaiyi kuka, su maryam kam kukan suke tayi kamar anyi musu mutuwa shiyasa shima saida yaji kwalla na shirin zubo masa da koke koke dai yadau kayanshi yatafi shida salim wanda zaiyi masa rakiya har inda zai hau motar Kaduna.
Bayan sallar azahar yashiga kaduna, dakinsa wanda yakama yaje ya shirya kayansa yaci snacks ya kwanta domin hutawa duk da yana son shiga kasuwa yasiyo abubuwan da yake bukata na amfainin yau da kullum da kayan abinci. Zuwa dare ya kammala komai yagyare dakinsa tsaf ya siyo duk abubuwan da yake bukata, kwanciya yayi kan katuwar katifarsa ya bararraje ya kira gida saida suka gaisa da kowa na gidan sannan yakira ya abba shima suka dan taba hira sannan yakira husnah daga karshe ita kam hira suka sha sosai domin har 10 da wani abun domin shagwabar da yasaba yaketa zuba mata,
"Ko inje infadawa baba adaura mana aure akawoki nan mu zauna.... Ni kin san bana son harkar yunwa gashi bana son yin girki da kaina...."
"Ka rinka zuwa captaria kana ci mana..."
"Yanmatanah abincin saidawa farin maggi suke sakawa nikuma bana so idan naci sai nayi amai...." Yakarashe maganar cikin shagwaba, dariya husnah tayi,
"Ya fahad kaifa dadina dakai shagwaba...."
"Kin manta ni dan auta ne? Komai ayiyah tasamu ni take baiwa fa...."
"Su Mariya fa? Basune auta ba?"
"Ke wadannan fa "yayana ne, yaran sister nane..."
"Badai 'yayanka ba,'yayan Anty dai.... Kai ai tukunnah..."
Dariya yayi ya lumshe idanuwanshi,
"To me kike ci na baka na zuba..., nima din kwana nawane muna yin aure zaki haifo yan biyu kafin shekara ta zagayo...."
"Wai wai... Lallai ya fahad, yauwa dama inaso in tambayeka wai dan Allah...."
Jin tayi shiru yasashi bude idanuwansa,
"Menene? Go on ina jinki..."
"Wai meya rabaku da matarka"
"Husnah dan Allah kar muyi wannan maganar saboda ciwona zai iya tashi kinga nasamu kwana biyun nan yasauka...."
"Shikenan ya fahad insha Allah bazan sake yimaka magana kwatankwacin irin wannan ba,Allah yakara maka lafiya..."
"Thank you husnah"
Sun jima suna hira daga bisani sukayi sallama kowa zuciyarsa fari tass saboda dadadan kalaman da suka fadawa juna.