← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 67

Sashe 29

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Daga haka yawuce bedroom yayi shirin ball yafito yana sanye da kayan ball ajikinsa jajaye na club din Barcelona harda safa hannunsa rikeda wayarshi da bakaken combos dinshi, wani kulli ne taji ya tokare makoshinta wato ma mahaukaciya ya dauketa ko yaya da har zai tashi yabarta without saying anything, babu bata lokaci ta mike taje gabanshi,

"Malam ji mana... Bakaji abinda nace maka bane?"

Juyowa yayi ya kafeta da ido bayan ya ajiye takalmanshi akasa,

"To mekikeso nace miki baby? Banida abinda zance shiyasa kikaji nayi shiru"

"Fahad wallahi tun muna shaida juna ka sakeni domin bazan iya zaman aure dakai ba, kalleka fa ka kalleni ai kaima kasan ni ba mate din aurenka bace dan haka kawai ka sakeni tun kafin duniya ta jimu..."

"To wai dan Allah laifin me kikayi min da zakice sai na sakeki, ko kuma ni laifin me nayi miki?"

"Babu abinda kayi min kawai bana bukatar auren ne ahalin yanzu"

"Hmmm bilkisu kenan karfa kiga kin girmeni kirinka yimin kallon sakarai ko marar wayo, ashe kecema mijin mutukar zan rinka aiki da umarninki...."

Sunkuyawa yayi zai dauki takalmanshi ta kamo rigarshi yadago yana kallonta,

"Wallahi fahad sai ka sakeni, akan me zaka dage sai kayi rayuwar aure dani..."

"A'a dan Allah basai kin yimin sharri ba,yaushe nataba nemanki? Na taba cewa sai na kusanceki?"

"Ni ba wannan maganar nake yimaka ba, maganar saki nake yimaka, ka sakeni kawai...."

Murmushi yayi sannan yadauki takalminsa yana kallonta,

"Zan tafi....me zan samu? Kiss ko hugging?"

Wani takaicine taji ya lullubeta ga bakin ciki da yake taso mata a makoshinta,

"Wai kai wasa ka dauki maganar nan ne?"

Wani sakaran kallo yayi mata sannan ya maida kallonsa ga wayarshi wadda ke vibrating alamar kira yashigo,

"To idan ba wasa ba menene? Ai wannan maganganun naki basuda maraba da wasan kwaikwayo hajjaju.... Ni natafi sai na dawo"

Tsabar bakin ciki rasa abinda zatai tayi,kasa koda kwakkwaran motsi tayi tana ji tana kallonsa yasaka kai yafice daga cikin falon yana amsa wayar da akayi masa,

"Hello anty fauziyya..."

"Auta yajikin naka?" Tafada daga daya bangaren,

"Anty nasamu sauki ni yanzu hakama filin ball zanje"

"Kai, kar kaje fa kajawa kanka matsala"

"Ahh babu komai Anty wallahi ras nake jina"

Kasa motsawa tayi daga wurin taci gaba da tsaiwa kamar wadda aka dasa har saida kafafuwanta suka fara nuna alamar gajiyawa da tsaiwar da take nan tazame ta zauna kamar abin shiri sai kuma kuka ya balle mata tashiga rusashi kamar wata yarinyar goye domin harta manta rabonta da kuka irin wannan.

Abangaren fahad kuwa sosai abinda yafaru tsakaninsa da bilkisu ya tsaya masa arai,ko kadan hakan baiyi masa dadiba amma haka dai yadaure ya yakice damuwar yashiga sha'aninsa duk da dai abun yana fado masa arai lokaci zuwa lokaci. Saida yabuga ball sosai sannan yafita yaje yanemi wuri ya zauna dan yahuta, shifa yanzu matsalar ma idan yakoma gida bai san ayanayin da zaije ya iske bilkisu ba wannan abu yanzu shine babbar damuwarsa.

Tunda bilkisu tayi wannan zaman yan borin tana rusa kuka bata dainaba saida kiran hamood yashigo cikin wayarta da rarrafe taje ta dauko wayar tadaga muryarta har ta dishe dan tsabar kuka,

"Sweetheart yasakeki...?"

Cikin dasasshiyar muryarta ta amsa amsa,

"Wallahi hamood yaki ya sakeni, nayi nayi amma abin ya faskara..."

"Don't tell me this sweetheart, you should insist akan dole sai ya sakeki, ki matsa masa sosai,bana son ki kara koda 1 week agidansa...."

Daga kai tayi tamkar yana kallonta,

"Yanzu baya nan yafita amma da zarar yadawo zan dora daga inda natsaya..."

"Yawwa one love..."

Kit takashe wayar tana jin sabon kuka yana taho mata,ahaka fahad yadawo ya isketa zaune dirsham kan rug tana hawaye,

"Hajjaju..... Wai dan Allah menene matsalar ne? Meke faruwa?"

Yace da ita yana kokarin tsugunnawa agabanta, jajayen idanuwanta wadanda suka kankance ta dago tana zabga masa harara,

"Fahad wallahi idan har baka rabu daniba sai kayi nadama tareda da nasani mai tarin yawa...."

"Ni wallahi bana son inji irin wadannan kalmomin suna fitowa daga bakinki"

Hayayyako masa tayi da masifa da tashin hankali tuni yatashi yawuce bedroom domin har anfara kiran sallar magrib, wanka yayi yafito yashirya yasaka jeans da jallabiya milk colour yafita bayan yasha turare tana zaune inda yabarta tana ta kuka,

"Ni narasa maganin abinda kukan nan zaiyi miki bilkisu.... Dan girman Allah ki barwa Allah lamarinsa ki sanyawa zuciyarki ruwan sanyi..."

Mikewa tayi tana hawaye tana tunkararsa,

"Wallahi fahad ko duniya zata tashi bazan cigaba da zama da kai ba domin ba kaine farin cikina ba, farin cikina yana wurin waninka dan haka yazama tilas ka sawwake min..."

Bai jira takaraso ba yafice da sauri yabar gidan, masallaci yatafi daga can yawuce wurinsu salim wato majalissarsu ta shan shayi, ita kuwa bilkisu tana nan zaune dakyar tatashi tayi salla bayan tayi salla hamood yasake kiranta yana kara jaddada mata maganar neman sakinta awurin fahad.

Gaba daya fahad bashida nutsuwa domin wasa wasa damuwar da bilkisu ke ciki tafara tasiri akansa saboda yau kimanin kwana biyar kenan suna cikin rashin kwanciyar hankali tun ranar da aka sallamoshi daga asibiti rabonshi da cikakkiyar nutsuwa domin bilkisu tasashi agaba da masifa da tijara tun abin baya damunsa har yafara damunsa,

Dama tunda haka tafara faruwa tadaina kwana acikin daki sai falo yanzu sai shine ke kwanciya aciki sannan tadaina girki kwata kwata sai dai tahada tea tasha shiyasa kwana biyar kacal duk tafita hayyacinta fahad yayi lallashin yayi ban bakin amma abin yaci tura. Yau ma kamar kullum yana daki yana shiryawa zai fita yajiyota tana yin waya afalo,saurarawa yayi dakyau nan yaji abinda take fada,

"Hamood ka kara hakuri wallahi ina iya bakin kokarina ganin ya sakeni but he refused... I don't even know what to do..."

Bai bari yakarasa jin wayar tasuba yaje yakarasa shiryawarshi yana niyyar fita tashigo ta watsar da wayoyin kan gado bayan ta watsa masa harara tawuce cikin bathroom, killer smile ya danyi aranshi yace,

"Daidai kenan"

Karamar wayarta yadauka yafita yabar babbar domin yasan tafi amfani da karamar, lifan dinshi yagoge da duster sannan yahau yafita.Saida yayi nisa da unguwar sannan yatsaya yayi packing agefen titi receiving calls dinta yafara bi yana dubawa har yagano abinda yake son yagano babu bata lokaci yayi dialing number hamood, a kasalance yaji yadauki wayar,

"Sweetheart ya sakeki ne?" Abinda kunnuwan fahad suka jiye masa kenan nan yayi kwafa yafara balbalawa hamood masifa kamar zai yashe hanjin cikinsa ya yar,

"Ban saketa ba kai meya hana ka saketan dakiki?, kai wanne irin garane marar tunani da nutsuwa? Dan tsabar jakanta shine zaka rinka kiran matata kana hure mata kunne wai sai takashe aurenta kunyi aure...... To wallahi bari kaji infada maka wani abu...."

Katseshi hamood yayi cikin bala'i,

"Shut up..... Karka kawo min raini anan domin ni ba sa'anka bane, bilkisu kuma dolenka ka rabu da ita na aureta saboda ita ba matar karamin yaro bace irinka....."

"To ai karamin yaron yayi abinda Kai babban banza ka kasa yi, kawai kazo kana yaudarar matar mutum dan tsabar jahilci da dakikanci,da kasan kana son nata meyasa baka tsaya ka aureta ba sai yanzu da tayi aure zaka dawo kana bibiyarta.... To wallahi am warning u daga yau karka kuskura ka kara kirar min matata idan kuma ka ki ji bazaka ki ganiba..."

"Uban me zakayi idan ansake kiran matar taka? Me kake dashi? Waya san dakai a kasar nan, matsiyaci kawai irinka malam...."

"Zaka san koni waye duk ranar da ka sake gangancin kiranta, banza dan akuya kawai...."

Katse wayar yayi sannan ya kasheta gaba daya ya jefa acikin aljihunsa yabuga Babur dinshi yayi gaba, gidansu yaje amma sam bai nunawa su ayiyah yana tareda matsala ba mamuh sai tsokanarsa takeyi wai yayan barunsa yau su zasu yanke suyi farfesu suci a matsayin abincin rana, shi dai sai dariya yake yajima agidan kafin yatafi da niyyar zuwa kasuwa wurin baba domin bai iskeshi agida ba yasamu yafita kasuwa acan ya shantake wurinsu baba wanda gaba daya shagunan dake layin duk na dattijai ne kamar baba shiyasa suke zamansu zama na mutunci ga yar majalissarsu nan gaban shagunansu karkashin wata bishiyar darbejiya, gefe fahad yakoma yayi zamansa yana sauraren hirar su baba irin tasu ta manya, rabonshi da yazo shagon baba yayi zama irin wannan har yamanta amma yau acan yayi sallar azahar ma nan aka kawowa su baba damammiyar fura cikin katuwar kwarya tasha sugar da gasasshen nama, cups aka fito dasu daga wani shago kowa yana diba sosai abin ya kayatar da fahad wato zama irin na iyayenmu da kakanni abin burgewa ne domin kowa yasan yanda zai zauna da kowa.

Abangaren bilkisu kuwa neman duniya tayiwa wayarta amma tarasa sai babbar amma sama ko kasa tarasa karamar, babu inda batayi checking ba agidan amma bata ganiba daga karshe dai tagane cewa fahad ne yadauka nan ta sake hawa ta cika tayi famm tana jiran dawowarsa amma shiru har hamood yakirata a daya layin nata dake kan babbar wayar yana fada mata irin zagin da fahad yayi masa hakan yasake tunzurata,shi kuwa fahad sai yamma yabar wurinsu baba yanufi shagonsu bayan magriba yakoma gida taso masa bilkisu tayi tamkar zata dokeshi,

"Bani wayata fahad, waye yace ka daukar min waya? Wai menene amfanin zama da mutumin da shi baya son zama dakai? Wacce riba zaka samu?"

Zama yayi saman kujera yana kallonta duk tabi ta hargitse,

"Bilkisu yakamata ki nutsu ki gane mai sonki da gaskiya, wallahi mutumin can yaudararki yakeyi, kiyi hakuri ki karbeni a matsayin miji nikuma nayi miki alkawari bazan baki kunya ba amma wallahi shi ba sonki yakeba dagaske nine nan masoyinki na gaskiya..."

"Ni ba dogon jawabi na tambayeka ba cewa nayi kawai ka sakeni babu ruwanka da rayuwar da zan shiga, babu ruwanka da yana sona ko sabanin haka sannan kabani wayata...."

"Anhanaki wayar kizo ki kwata ai kinada karfi......"

Yafada yana mikewa tsaye babu shiri taja da baya tana kallonsa, nunata yayi da dan yatsa,
Chapter 29 · 0% Book details