Sashe 22
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana nan zaune tana aikinta yafito sanye da jallabiya kalar ruwan kasa har lokacin bai daina kumbura ba, kayan shimfidarshi ya diba ya fita zuwa falo bai sake komawa cikin dakin ba sai asubah daga nan bacci yakoma bayan yayi sallar asubah bai tashiba sai karfe 9, wanka yayi yasa three quarter da t shirt ya tattaro kayan baccinshi da kananan kayanshi yakai tsakar gida, duk sai wani cika yake yana batsewa tana ankare dashi, yajima tsaye kan kayan yana kallonsu kafin yaje ya dauko bucket da sabulun wanki yazo gaban fanfo ya debi ruwa yafara wanke kayan yanayi yana yarfe hannu kamar wanda ake yankar naman hannunshi,
"Hajjaju yanzu idan wani yazo ya iskeni ina wanki bazaki ji kunya ba?"
Karasa ajiye kayan wanke wankenta tayi tana kallonshi,
"Au wai kai da nufinka ni zanyi maka wankin?"
Langabe kai yayi yasake bata fuska,
"To ai mata masu neman aljanna har wanki suke yiwa mazajensu"
Dariya ita abun yabata ma amma ta dake ta wucewarta daki, dakyar ya samu ya wanke kayan Amma fa ji yake kamar yayi wani gagarumin aiki gashi ko breakfast baiyi ba, falo yaje ya fada saman doguwar kujera yanata ajjiye numfashi. Saida yahuta sosai sannan yatashi ya yi breakfast lokacin karfe goma da kusan rabi, yana gamawa yasake kwanciya, wurin 12 na rana yakwaso kayan mashi yazauna domin gogesu, yana yi yana jin wakar breaker awayarshi,
"Gaskiya ni ba dan gata bane..., inyi wanki da kaina kuma gugar ma arasa mai taimako na..."
Tana jinsa bata tanka masa ba zuwa can yafara bin wakar,
"Idan zaki kije dani.... Idan nai fushi ki rarrasheni....!"
Nan dinma dai bata tanka ba har yayi yagama, ganin rana tayi express girki tayi musu bayan yaci abincin rana ya tattaro kayan sawarshi masu datti yace itama ta tattaro nata wanki zai kai musu, bayan yatafi itama ta wanke nata inner wears din masu datti, rasa inda zata shanya kayan tayi domin bata son fahad yagani shiyasa ko pant ta wanke boyeshi take inda bazai ganiba wani lokacin ma sai yafita take shanyawa kafin yadawo yabushe ta dauke kayanta amma bata taba wanke bra ba sai yau, babu yanda ta iya dole akan igiyar da ya daura ta baya ta shanya kayan. Kafin yadawo tayi wanka tashirya tana jiran yazo su tafi ziyarar da yace zasuje gidan yaya asabe da su anty kubra domin itama tana son fitar bata son zaman kadaicin nan musamman ma idan baya nan. Bai jima awurin kai wankin ba yadawo,wanka kawai shima yayi yasaka wani yadi mai laushi kalar ruwan toka amma bai saka hulaba yasha turare suka fita, drop din napep suka dauka yakaisu duk inda zasu je dama anty Kubra da anty juwairiyya makota ne domin katangarsu ma daya anty asabe ce dai awata unguwa ta daban, daga karshe gidansu yakaita wurinsu ayiyah ai kuwa ranar taga soyayya domin ayiyah kamar zata goyata dan kauna. Fita yayi yabarta tareda su ayiya yatafi majalissar su ta shan shayi wadda ke kusa da filin kwallonsu dama sunyi waya da salim yasanar dashi yana can.
Acan gida kuwa itama bilkisu tasake da su ayiyah sosai duk aikin da taga zasuyi sai ta karbe tayishi ahaka harsu Mariya suka dawo daga islamiyya suka sameta,Rungumeta sukayi suna tsalle dan tsananin murnar ganinta, itama murnar takeyi domin tana kaunar yaran duk da ba yan biyu bane amma kamarsu daya sannan a shekaru ma tsiran babu yawa, tana nan tareda su sunata bata labarin makarantarsu sai zuba mata surutu suke yi ita kuma tana cin tuwon da mamuh ta zubo mata tuwon biski miyar taushe wacce taji tantakwashi da man shanu ai kuwa taji dadin tuwon nan domin tazage ta ci babu fulako, tana daf da gama cin tuwon fahad yashigo ai su mariya na jin maganarshi atsakar gida kowacce takama bakinta, dariya abin yabawa bilkisu saboda daga jin motsinshi yara har sun daina kwarafniya,
"Meyasa kuka daina yimin hirar ne mariya?"
"Anty ya fahad ya hanamu surutu, duka yake yi sosai yafi ya Abba duka..." Inji Maryam,
"Ga dukanshi zafi..."
Dariya tayi saboda jin abinda mariya tace itama, sake nutsuwa sukayi lokacin da yashigo cikin falon, nan suka fara rige rigen gaisheshi,
"Mariya karbo min abinci awurin ayiyah..."
Tun kafin yarufe bakinshi ta tashi tafita, kallon Maryam yayi ya harareta,
"Ke kuma ina dan kwalinki? Bana hanaku zama babu dan kwali ba?"
Itama tashi tayi dasauri tashige daki domin dauko dan kwalin, sai lokacin ya maida kallonshi kan bilkisu,
"Nikuma akan me za ayi min nawa fadan?"
Dariya yayi ya zauna kusa da ita yana lumshe idanuwa sakamakon kamshinta da ya shaka wato matar nan karshe ce awurin kamshi yarasa wanne turare take shafawa take wannan kamshin shiyasa wani lokacin har kishin fitarta wurin aiki yake saboda baya son wani yaji kamshin nan sai shi kadai,
"Ni na isa hajjaju? Ai ke bakya laifi"
Dan murmushi kawai tayi batace komai ba har maryam ta kawo masa tuwon shima yafara ci ita kuma bilkisu ta dauke kwanikan da tagama ci zata fitar dashi,
"Ke mariya ita zata fitar da kwanikan...?"
Dasauri suka karbeta tana cewa ma subarshi amma suka ki, hannunta taje ta wanke sannan ta dawo tazauna,
"Gaskiya kana takurawa yaran nan"
"Basa jin magana ne..."
"Wallahi bawani rashin ji da sukeyi"
"Bazanyi musu dake ba"
Saida shima yagama cin tuwon sannan suka yiwa su ayiyah sallama suka tafi lokacin har baba yadawo daga kasuwa, yanzun ma kamar dazu a keke napep suka koma gida sun ko yi sa,a akwai wuta dayake side din ana samun wuta sosai, bedroom tawuce shi kuwa afalo yaja birki yacire rigar jikinshi yabar dogon wandonshi da singileti fara yana kallon kwallo, ita kam wanka tayi ta dauki laptop dinta tana kallo daga ita sai towel duk da yanzu tana dan taka tsantsan amma takasa sabawa da zama cikin hijab domin ita agida babu mai shigar mata daki shiyasa take cin karenta babu babbaka dan sai ta kwana da towel ko under wear dama da daddare daga pant har bra babu ruwanta dasu sai idan tana period ne take kwana da pant, bata san kirinkin da yakai fahad baya ba sai ganinshi tayi yafado mata daki dauke da braziers dinta data wanke dazu,
"Ji mana malam, wai meye hakane? Dan Allah karinka knocking before ka shigo"
"Yi hakuri, mantawa nayi"
Tana gyara hijab din datake kokarin sakawa tace,
"Waya saka dauko min shaya?"
Wartar kayan tayi cikeda jin haushi, shi kam yana dariya yawuce drewar domin itace bata saniba amma yafi minti biyar yana kallon braziers din duk saida yayi musu kallon kurulla sannan yakawo mata.
Kayan baccinshi ya dauka yawuce toilet har lokacin harararshi takeyi, sai da taga shigarshi sannan ta tashi taje ta boye kayan acan drewar dinta,dawowa tayi ta zauna taci gaba da aikinta har yafito daga wankan sanye da gajeren wando da riga armless duk farare sol masu santsi, kallonta yatsaya yi yana shafar keya,
"Hajjaju nace yau dinma a falon zan kwana...?"
"A'a akaina zaka kwana..." Tayi masa gatse dama bata gama hucewa daga fushin dauko mata braziers dinta da yayiba, dan tabe baki yayi yai gaba yana kunkuni,
"Da za ayi hakan aini so zanyi..."
Kayan shimfidarshi ya dauka yakara gaba domin yau bacci yake ji, tsabar takaici ko wutar yau bai kashe mata ba yaje yayi kwanciyarsa, itama bata kara bi ta kansa ba saida ta kammala aikinta sannan tafito zataje kitchen lokacin misalin karfe 12 saura nadare, awani baje ta ganshi ya harde hannuwa yadora kafa daya kan daya, murmushi tayi tace aranta,
"Lallai kuwa Prince... Irin wannan zuba mulki haka, baccin ma sai anyi masa sarauta"
Fridge tawuce ta dauko ruwa mai sanyi sannan tadawo takashe masa wutar falon tashige daki abinta. Da safe tanata kici kicin hada abin karyawa saboda tana so tafita office dawuri shi kuwa yanata baccinsa saman katifarsa domin tunda sukayi sallar asubah yasake komawa bacci, har tagama hada breakfast tayi wanka bai tashiba, bayan tagama shiryawa ne tazo tana karyawa yatashi, daga kwancen da yake ya daga ido yana kallonta, leshi ne ajikinta c green colour dinkin riga da skirt, batayi wata doguwar kwalliya ba amma fa akwai kamshi kamar anyi barin turare maida idonsa yayi ya lumshe yana turo baki shi bawai aikin da take fitane damuwarsa ba, damuwarshi shine yanzu duk namijin da ta gifta ta kusa dashi shima dole sai yaji irin wannan kamshin da yake jin tanayi? Kai impossible,
"Allah bazai yuyuba..." Yafada afili tare da tashi zaune,
"Hajjaju har kin shirya ne? Ina kwana?"
Daga kan dining tajuyo ta kalleshi,
"Lafiya lau"
Murmushi yayi domin dama yasan gaisuwar bata wuce haka,
Bathroom yayi sauri yaje yayi brush yadawo ya isketa saman dining din amman takusa kammalawa, kujera yaja ya zauna wacce ke kallon tata,lumshe ido yayi,
"Hajjaju wannan kamshin fa.... Gaskiya...... Hmmm.....gaskiya"
Mikewa tayi tawuce abinta tana cewa,
"Kaga ni malam sauri nake aiki ne dani da sanyin safiyar nan"
"Adawo lafiya, Allah yatsare min ke hajjaju na"
Murmushi kadai tayi tawuce daki ta nado laffaya dinta bayan ta saka safar kafa baka ta dauko komai da take bukata tazo tawuceshi tafita, duk sai yaji gidan kuma babu dadi da baiyi niyyar fitaba amma dole tasa yayi wanka yazo yashirya ganin bata nan da komanta yayi amfani har turare nata yafesa, tsayawa yayi yana kallon turaren,
"Arabian night...uhmm su hajjaju manya"
Duka saida yashafa daga body spray din har performed spray sannan yadauko kayansa yasaka yafita shago. Wurin karfe biyu saura yana shago yagama yiwa wasu yan mata dinki husna na zaune gaban kekenshi sai ga kiran bilkisu yashigo wayarshi, zuba masa ido husna tayi lokacin da yadauki wayar,
"Ranki yadade ya akayi?"
"Kaga dama cewa nayi zan biya ta gidanmu da daddare sai na taho"
"A'a hajjaju ki bari ranar juma'a ko cikin weekend sai kije"
"Shikenan..."
"Adawo lafiya"
"Hajjaju yanzu idan wani yazo ya iskeni ina wanki bazaki ji kunya ba?"
Karasa ajiye kayan wanke wankenta tayi tana kallonshi,
"Au wai kai da nufinka ni zanyi maka wankin?"
Langabe kai yayi yasake bata fuska,
"To ai mata masu neman aljanna har wanki suke yiwa mazajensu"
Dariya ita abun yabata ma amma ta dake ta wucewarta daki, dakyar ya samu ya wanke kayan Amma fa ji yake kamar yayi wani gagarumin aiki gashi ko breakfast baiyi ba, falo yaje ya fada saman doguwar kujera yanata ajjiye numfashi. Saida yahuta sosai sannan yatashi ya yi breakfast lokacin karfe goma da kusan rabi, yana gamawa yasake kwanciya, wurin 12 na rana yakwaso kayan mashi yazauna domin gogesu, yana yi yana jin wakar breaker awayarshi,
"Gaskiya ni ba dan gata bane..., inyi wanki da kaina kuma gugar ma arasa mai taimako na..."
Tana jinsa bata tanka masa ba zuwa can yafara bin wakar,
"Idan zaki kije dani.... Idan nai fushi ki rarrasheni....!"
Nan dinma dai bata tanka ba har yayi yagama, ganin rana tayi express girki tayi musu bayan yaci abincin rana ya tattaro kayan sawarshi masu datti yace itama ta tattaro nata wanki zai kai musu, bayan yatafi itama ta wanke nata inner wears din masu datti, rasa inda zata shanya kayan tayi domin bata son fahad yagani shiyasa ko pant ta wanke boyeshi take inda bazai ganiba wani lokacin ma sai yafita take shanyawa kafin yadawo yabushe ta dauke kayanta amma bata taba wanke bra ba sai yau, babu yanda ta iya dole akan igiyar da ya daura ta baya ta shanya kayan. Kafin yadawo tayi wanka tashirya tana jiran yazo su tafi ziyarar da yace zasuje gidan yaya asabe da su anty kubra domin itama tana son fitar bata son zaman kadaicin nan musamman ma idan baya nan. Bai jima awurin kai wankin ba yadawo,wanka kawai shima yayi yasaka wani yadi mai laushi kalar ruwan toka amma bai saka hulaba yasha turare suka fita, drop din napep suka dauka yakaisu duk inda zasu je dama anty Kubra da anty juwairiyya makota ne domin katangarsu ma daya anty asabe ce dai awata unguwa ta daban, daga karshe gidansu yakaita wurinsu ayiyah ai kuwa ranar taga soyayya domin ayiyah kamar zata goyata dan kauna. Fita yayi yabarta tareda su ayiya yatafi majalissar su ta shan shayi wadda ke kusa da filin kwallonsu dama sunyi waya da salim yasanar dashi yana can.
Acan gida kuwa itama bilkisu tasake da su ayiyah sosai duk aikin da taga zasuyi sai ta karbe tayishi ahaka harsu Mariya suka dawo daga islamiyya suka sameta,Rungumeta sukayi suna tsalle dan tsananin murnar ganinta, itama murnar takeyi domin tana kaunar yaran duk da ba yan biyu bane amma kamarsu daya sannan a shekaru ma tsiran babu yawa, tana nan tareda su sunata bata labarin makarantarsu sai zuba mata surutu suke yi ita kuma tana cin tuwon da mamuh ta zubo mata tuwon biski miyar taushe wacce taji tantakwashi da man shanu ai kuwa taji dadin tuwon nan domin tazage ta ci babu fulako, tana daf da gama cin tuwon fahad yashigo ai su mariya na jin maganarshi atsakar gida kowacce takama bakinta, dariya abin yabawa bilkisu saboda daga jin motsinshi yara har sun daina kwarafniya,
"Meyasa kuka daina yimin hirar ne mariya?"
"Anty ya fahad ya hanamu surutu, duka yake yi sosai yafi ya Abba duka..." Inji Maryam,
"Ga dukanshi zafi..."
Dariya tayi saboda jin abinda mariya tace itama, sake nutsuwa sukayi lokacin da yashigo cikin falon, nan suka fara rige rigen gaisheshi,
"Mariya karbo min abinci awurin ayiyah..."
Tun kafin yarufe bakinshi ta tashi tafita, kallon Maryam yayi ya harareta,
"Ke kuma ina dan kwalinki? Bana hanaku zama babu dan kwali ba?"
Itama tashi tayi dasauri tashige daki domin dauko dan kwalin, sai lokacin ya maida kallonshi kan bilkisu,
"Nikuma akan me za ayi min nawa fadan?"
Dariya yayi ya zauna kusa da ita yana lumshe idanuwa sakamakon kamshinta da ya shaka wato matar nan karshe ce awurin kamshi yarasa wanne turare take shafawa take wannan kamshin shiyasa wani lokacin har kishin fitarta wurin aiki yake saboda baya son wani yaji kamshin nan sai shi kadai,
"Ni na isa hajjaju? Ai ke bakya laifi"
Dan murmushi kawai tayi batace komai ba har maryam ta kawo masa tuwon shima yafara ci ita kuma bilkisu ta dauke kwanikan da tagama ci zata fitar dashi,
"Ke mariya ita zata fitar da kwanikan...?"
Dasauri suka karbeta tana cewa ma subarshi amma suka ki, hannunta taje ta wanke sannan ta dawo tazauna,
"Gaskiya kana takurawa yaran nan"
"Basa jin magana ne..."
"Wallahi bawani rashin ji da sukeyi"
"Bazanyi musu dake ba"
Saida shima yagama cin tuwon sannan suka yiwa su ayiyah sallama suka tafi lokacin har baba yadawo daga kasuwa, yanzun ma kamar dazu a keke napep suka koma gida sun ko yi sa,a akwai wuta dayake side din ana samun wuta sosai, bedroom tawuce shi kuwa afalo yaja birki yacire rigar jikinshi yabar dogon wandonshi da singileti fara yana kallon kwallo, ita kam wanka tayi ta dauki laptop dinta tana kallo daga ita sai towel duk da yanzu tana dan taka tsantsan amma takasa sabawa da zama cikin hijab domin ita agida babu mai shigar mata daki shiyasa take cin karenta babu babbaka dan sai ta kwana da towel ko under wear dama da daddare daga pant har bra babu ruwanta dasu sai idan tana period ne take kwana da pant, bata san kirinkin da yakai fahad baya ba sai ganinshi tayi yafado mata daki dauke da braziers dinta data wanke dazu,
"Ji mana malam, wai meye hakane? Dan Allah karinka knocking before ka shigo"
"Yi hakuri, mantawa nayi"
Tana gyara hijab din datake kokarin sakawa tace,
"Waya saka dauko min shaya?"
Wartar kayan tayi cikeda jin haushi, shi kam yana dariya yawuce drewar domin itace bata saniba amma yafi minti biyar yana kallon braziers din duk saida yayi musu kallon kurulla sannan yakawo mata.
Kayan baccinshi ya dauka yawuce toilet har lokacin harararshi takeyi, sai da taga shigarshi sannan ta tashi taje ta boye kayan acan drewar dinta,dawowa tayi ta zauna taci gaba da aikinta har yafito daga wankan sanye da gajeren wando da riga armless duk farare sol masu santsi, kallonta yatsaya yi yana shafar keya,
"Hajjaju nace yau dinma a falon zan kwana...?"
"A'a akaina zaka kwana..." Tayi masa gatse dama bata gama hucewa daga fushin dauko mata braziers dinta da yayiba, dan tabe baki yayi yai gaba yana kunkuni,
"Da za ayi hakan aini so zanyi..."
Kayan shimfidarshi ya dauka yakara gaba domin yau bacci yake ji, tsabar takaici ko wutar yau bai kashe mata ba yaje yayi kwanciyarsa, itama bata kara bi ta kansa ba saida ta kammala aikinta sannan tafito zataje kitchen lokacin misalin karfe 12 saura nadare, awani baje ta ganshi ya harde hannuwa yadora kafa daya kan daya, murmushi tayi tace aranta,
"Lallai kuwa Prince... Irin wannan zuba mulki haka, baccin ma sai anyi masa sarauta"
Fridge tawuce ta dauko ruwa mai sanyi sannan tadawo takashe masa wutar falon tashige daki abinta. Da safe tanata kici kicin hada abin karyawa saboda tana so tafita office dawuri shi kuwa yanata baccinsa saman katifarsa domin tunda sukayi sallar asubah yasake komawa bacci, har tagama hada breakfast tayi wanka bai tashiba, bayan tagama shiryawa ne tazo tana karyawa yatashi, daga kwancen da yake ya daga ido yana kallonta, leshi ne ajikinta c green colour dinkin riga da skirt, batayi wata doguwar kwalliya ba amma fa akwai kamshi kamar anyi barin turare maida idonsa yayi ya lumshe yana turo baki shi bawai aikin da take fitane damuwarsa ba, damuwarshi shine yanzu duk namijin da ta gifta ta kusa dashi shima dole sai yaji irin wannan kamshin da yake jin tanayi? Kai impossible,
"Allah bazai yuyuba..." Yafada afili tare da tashi zaune,
"Hajjaju har kin shirya ne? Ina kwana?"
Daga kan dining tajuyo ta kalleshi,
"Lafiya lau"
Murmushi yayi domin dama yasan gaisuwar bata wuce haka,
Bathroom yayi sauri yaje yayi brush yadawo ya isketa saman dining din amman takusa kammalawa, kujera yaja ya zauna wacce ke kallon tata,lumshe ido yayi,
"Hajjaju wannan kamshin fa.... Gaskiya...... Hmmm.....gaskiya"
Mikewa tayi tawuce abinta tana cewa,
"Kaga ni malam sauri nake aiki ne dani da sanyin safiyar nan"
"Adawo lafiya, Allah yatsare min ke hajjaju na"
Murmushi kadai tayi tawuce daki ta nado laffaya dinta bayan ta saka safar kafa baka ta dauko komai da take bukata tazo tawuceshi tafita, duk sai yaji gidan kuma babu dadi da baiyi niyyar fitaba amma dole tasa yayi wanka yazo yashirya ganin bata nan da komanta yayi amfani har turare nata yafesa, tsayawa yayi yana kallon turaren,
"Arabian night...uhmm su hajjaju manya"
Duka saida yashafa daga body spray din har performed spray sannan yadauko kayansa yasaka yafita shago. Wurin karfe biyu saura yana shago yagama yiwa wasu yan mata dinki husna na zaune gaban kekenshi sai ga kiran bilkisu yashigo wayarshi, zuba masa ido husna tayi lokacin da yadauki wayar,
"Ranki yadade ya akayi?"
"Kaga dama cewa nayi zan biya ta gidanmu da daddare sai na taho"
"A'a hajjaju ki bari ranar juma'a ko cikin weekend sai kije"
"Shikenan..."
"Adawo lafiya"