Sashe 55
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bata kulashiba taja duvet ta rufe har kanta tana sauraron ajiyar zuciyar da yake saukewa ahankali zuwa can kamar bayan mintuna 15 taji yatashi yakashe mata wutar yafita, tofah kamar amafarki sai taji kuka ya subuce mata wanda bata san musabbabinsa ba,ni kaina Ummi A'isha so nake naji dalilin kukan Bilkisu........
_jiya yar dakina asked me wai sis ummy wacce irin kamace da yan Jami'a? I laugh over and over and over again then nace mata, yan gayu masu class kuma wayayyu saboda seriously duk wadda tayi jami'a zaki sameta komai nata is different tun daga mu'amalarta da mutane and so on, hatta a dressing dinta ma wallahi zaki fuskanci mai class ce babu baragada da yawan hayaniya shiyasa kukaji na siffanta husnah da haka, da nace kana ganinta zaka gane yar Jami'a ce what i mean is da zarar ka ganta kaga mace mai class kuma abar burgewa, and da nace tayi hudar kunne guda uku bawai fa ina nufin hakan baida kyau ba a'a kawai inaso innuna irin ta kure kwalliya da gayu mai yawa so dan Allah kar ayi min mummunar fahimta wallahi duk abinda nafada da kyakkyawar niyya nafada, tnx for ur love and support._
*_Ummi Shatu_*
*Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
50***Kuka take yi harda shessheka gaba daya ta jike pillow din da take kai, ga wani matsanancin ciwon kai wanda yafara damunta har tsawon karfe daya da kusan rabi takai tana wannan kukan,
Dai dai wannan lokaci shi kuma fahad na can tare da husna, lokacin da yashiga kishingide ya isketa ta dan fara bacci, tashinta yayi ta hanyar kama yan kafarta wadanda sukasha jan lalle da baki yana jansu ahankali, bude ido tayi tana kallonshi cikeda gajiya da tarin bacci,
"Ya fahad... Sai yanzu kadawo?"
"Wai har kin fara bacci asma'u? Oya tashi kici abinci sai ki kwanta..."
Yafada yana janyo hannunta, kafada ta noke tamaida kanta ta kwantar saman pillow,
"Ni bana jin yunwa, kaci kayanka..."
Murmushi yayi ya matsa jikinta, ahankali yace,
"Ko kema kina jin tsorone?"
"Name?" Tafada tana bata rai,
"Kar kici min kazata kuma nace sai kin biyani......!"
Daga shi har ita dariya ce ta subuce musu ta harareshi sannan ta gyara kwanciyarta izuwa rigingine,
"U kid yourself sweetheart.... Good news da zan baka yanzu shine am off, soo allow me to sleep pls....."
Murmushi yayi yana shafar lallen hannunta,
"To kinga dadinma zagewa kici kaza kenan tunda ba biyana zakiyi ba, wake up pls"
Girgiza kai tayi tana lumshe idanuwanta,
"Na koshi wallahi, sai da safe zanci...."
"Ok, sleep tight my love, good night...."
Bata amsaba ta gyara kwanciyarta ta hanyar juyawa daya bangaren, shikam yunwa yakeji sosai saboda yau da yunwa yawuni throughout shiyasa ya zauna yaci rabin kaza yasha madara, tashi yayi yashiga bathroom yayi wanka yafito ita dai husnah ko kayan jikinta dakyar ta iya canjawa saboda tsabar bacci da gajiya,shiryawa yayi cikin kayan baccinsa maroon colour masu santsi sannan yatashi yafita, dakin Bilkisu yanufa saboda haka kawai yake jin zuciyarshi bata nutsu da yanayin da Bilkisu ke cikiba shiyasa yasake niyyar komawa dakinta yaganta,
Kamar amafarki taji bude kofa babu shiri ta hadiye kukanta ta toshe bakinta da hannunta guda daya, fitila ya kunna sannan cikin sassarfa yakarasa gaban gadon da take lullube ta wani tukunkune wuri daya,
"Billy....." Taji yafada cikin son jan magana amma sai tayi shiru kamar mai bacci,
"Billy tashi kiji.....kinji"
Nan dinma shiru tayi masa tana shasshekar kuka azuciyarta,
"Wai kina nufin kema kinyi bacci? Ok shikenan good night.....have a nice sweet dream"
Daga haka yajuya yaje ya kashe mata wutar yafita bayan yarufe mata kofa. Yana fita ta cigaba da shasshekar kukanta,kusan daren gaba daya bata samu runtsawa ba har saida asubah takawo jiki lokacinne bacci yasamu nasarar yin gaba da ita, su fahad kuwa tunda yabar dakin Bilkisu yana zuwa ya kwanta kusa da husnah babu jimawa yabi sahunta wurin yin bacci saboda tsabar gajiyar dake tattare dashi sallar asubah makara yayi dan sai wurin 6 sannan ya tashi, yana yin salla yasake kwanciya daidai lokacin ita kuma husnah ta tashi, wanka tayi ta caba ado ta sake kwanciya gefen fahad tana kallonsa yana ta sharar bacci hannunsa kan cikinsa, hamdala ta shiga yi ga ubangijin rahma dan ko yanzu ta mutu tasan Allah ya cika mata burinta, kasancewar jiya da yunwa ta kwana yasata jin cikinta yafara kiran ciroma babu shiri ta tashi tajanyo ledar da fahad yazo da ita adaren jiya, kaji guda biyune aciki amma yaci rabin guda daya sai fresh milk kwali biyu, fresh milk din tafara sha sannan taci rabin kazar da ya ajiye, rasa abinda zatayi tayi gashi takasa komawa bacci kuma lokacin karfe bakwai da wasu mintuna wadanda bazasu gaza biyar ba, tana nan kwance tana kallonsa har shima yafarka hada ido sukayi tayi masa gwalo, hannu ya mika mata amma sai ta gagara kama nashi saboda yau jinta take awani takure duk da ba yau tafara kama hannunshi ba amma dai na yau ya banbanta da na kullum, jikinsa ya matso da ita yana tsokanarta da idanuwanshi,
"Kin ci abinci?" Ya tambayeta ahankali, daga kai tayi sannan tace "ehh"
"Husnah kenan wai duk kinyi laushi why? Dan Allah kidaina tsorona,bari ma ki gani wanka zanyi infita..." Daga haka yatashi yawuce toilet kafin yafito ta dan gyaggyara dakin duk da babu wani datti da yayi sai dai dan abinda ba arasaba. Falo ta dan leka tana sa ran ko zata ga matar gidan amma shiru babu motsin kowa, kafin takoma daki fahad yashirya saima da ta daidaci cewar ya shirya sannan tashiga dakin, yana tsaye gaban mirror dinta yana karya hularshi da zai saka,
"Ya fahad ina kwana?" Tafada tana murmushi sannan tana kallonsa,
"Lafiya lau husnatah, ya bakunta?"
Dariya tayi tazauna agefen gadon tana kallonsa ta cikin mirror shima kallonta yayi yasakar mata murmushi sannan yajiyo,
"Bari induba hajjaju ko ta tashi..." Kai ta daga masa hakan yabashi damar wucewa yafita, dakin Bilkisu yabude yashiga da sallama akan labbansa, tana zaune gefen gado tana shafa mai da alama daga wanka tafito sai dai fuskarta duk a dan kumbure,
"Ashe kin tashi? Yakike?", dan tsuke fuskarta tayi saboda tasan rainin wayon nashi yazo yimata inbanda haka menene nashi na wani cemata yatake, jin bata tanka masa ba kuma taki kallonshi yasashi dan matsawa gab da ita,
"Billy yakika tashi...?"
Sam kin yarda ta kalleshi tayi saboda bata son yaga yanayin da idanuwanta ke ciki, har yagama neman maganarshi yafita bata tanka ba kuma bata kalleshi ba, wurin husnah yakoma yayi mata sallama yafita. Fitarshi babu jimawa su Anty Fauziyya sukazo da sauran yan uwan husnah wadanda suka kwana agidansu fahad, food flask din da aka zubowa kowa breakfast dinshi daban, anty asabe ce tashiga wurin Bilkisu takai mata nata, basu dade agidanba suka tafi sai lokacin da zasu tafi sannan Bilkisu tafito ta rakasu bakin kofa sannan takoma ciki tayi kwanciyarta, haka tawuni adaki a kwance dolece kawai take tadata ango kuwa bashi yadawo gidanba sai dare saboda anata baki yan uwa da abokan arziki duk wanda yaje gidan ya Abba to gidan fahad zai zarto shiyasa husnah yau tasha baki har ta godewa Allah amma fa Sam bata ga bilkisu ba hakan yasa mata tunani aranta na anya kuwa ko lafiya?.
Lokacin da yadawo dakin Bilkisu yashiga har lokacin tana kwance bakinta akekashe alamun bata ci komaiba, zama yayi saman bedside drewar yana kallonta,
"Kinci abinci ne?" Wani kallo tajuya tayi masa sannan takawar da kanta duk sai yaga tayi masa wani iri kamar marar lafiya,
"Dan Allah kici abinci rabin raina..." Yafada yana dariya shiru tayi masa, tashi yayi yafita yana fita taja dan siririn tsaki tagyara kwanciyarta, shi kam yana can suna zuba love da husnah dan yana kwance dare dare akan kafafunta tana bashi labarin irin bakin da tasha yau, daga nan bai sake fitaba sai dai idan salla zaije, ana yin sallar ishah kuwa yarufe gida yashiga gida yana tunanin ya kamata ya hada husnah da Bilkisu inyaso ko gaisawace suyi, yana shiga dakin husnah yaga tasha wata kwalliyar kamar bata kwanciya bacci ba, saida suka gama hira suka ci abinci yayi shirin bacci sannan yashiga dakin Bilkisu, itama tuni tayi shirin baccin tana zaune tsakiyar gadonta tana cin abincin da aka kawo musu daga gidansu fahad,
"Billy husnah zata zo ta gaisheki..."
"Ina ciwo ne?" Ta tambaya batare da ta kalleshi ba,
"A'a" yabata amsa,
"To bana bukata, ko zamana takeyi agidan?
"Allah yabaki hakuri, inzo muci abincin?"
Nan kuma bata tankaba saboda taga nema yake ya maidata wata bi ta nan, yana fita ta tashi tamayar da kofarta ta kulle, daren yau dai babu laifi ta dan samu damar yin bacci da wuri saboda jiya batayi ba yayinda ango da amarya ke can suna debewa junansu kewa danma dai har yanzu amaryar bata samu tsarki ba amma duk da haka an aikata abinda ba arasa ba, fahad baiyi bacci da wuriba yanata tunani wato dan adam yana nashi ne Allah na nasa, shi ko acikin mafarki bai taba zaton cewa zaiyi tarayya da wata mace koma bayan Bilkisu ba ashe husnah matarsa ce bai saniba sai yanzu. Washe garima haka Bilkisu tawuni curr adaki abinci kuma daga gidansu fahad ake kawowa, gaba daya zaman gidan ya isheta ya gundireta yakuma gama fita akanta, saida husnah tayi kwana uku gidan sannan suka hadu, ita Bilkisu tafito ita kuma husnah na zaune falo da waya a hannunta tana yin game, sama sama suka gaisa Bilkisu tawuce kitchen tayi abinda zatayi tafito, daren ranar fahad ya sameta da maganar girki domin yakamata husnah tafara girkinta adaina kawo musu daga gidansu fahad acewarta shine yake tambayar Bilkisu ya abin zai kasance,
"Ni zan dafawa matarka abincin da zata ci? Tabdijam to wallahi bazai yuyu ba, kowa yayi girkinsa final.... "
_jiya yar dakina asked me wai sis ummy wacce irin kamace da yan Jami'a? I laugh over and over and over again then nace mata, yan gayu masu class kuma wayayyu saboda seriously duk wadda tayi jami'a zaki sameta komai nata is different tun daga mu'amalarta da mutane and so on, hatta a dressing dinta ma wallahi zaki fuskanci mai class ce babu baragada da yawan hayaniya shiyasa kukaji na siffanta husnah da haka, da nace kana ganinta zaka gane yar Jami'a ce what i mean is da zarar ka ganta kaga mace mai class kuma abar burgewa, and da nace tayi hudar kunne guda uku bawai fa ina nufin hakan baida kyau ba a'a kawai inaso innuna irin ta kure kwalliya da gayu mai yawa so dan Allah kar ayi min mummunar fahimta wallahi duk abinda nafada da kyakkyawar niyya nafada, tnx for ur love and support._
*_Ummi Shatu_*
*Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
50***Kuka take yi harda shessheka gaba daya ta jike pillow din da take kai, ga wani matsanancin ciwon kai wanda yafara damunta har tsawon karfe daya da kusan rabi takai tana wannan kukan,
Dai dai wannan lokaci shi kuma fahad na can tare da husna, lokacin da yashiga kishingide ya isketa ta dan fara bacci, tashinta yayi ta hanyar kama yan kafarta wadanda sukasha jan lalle da baki yana jansu ahankali, bude ido tayi tana kallonshi cikeda gajiya da tarin bacci,
"Ya fahad... Sai yanzu kadawo?"
"Wai har kin fara bacci asma'u? Oya tashi kici abinci sai ki kwanta..."
Yafada yana janyo hannunta, kafada ta noke tamaida kanta ta kwantar saman pillow,
"Ni bana jin yunwa, kaci kayanka..."
Murmushi yayi ya matsa jikinta, ahankali yace,
"Ko kema kina jin tsorone?"
"Name?" Tafada tana bata rai,
"Kar kici min kazata kuma nace sai kin biyani......!"
Daga shi har ita dariya ce ta subuce musu ta harareshi sannan ta gyara kwanciyarta izuwa rigingine,
"U kid yourself sweetheart.... Good news da zan baka yanzu shine am off, soo allow me to sleep pls....."
Murmushi yayi yana shafar lallen hannunta,
"To kinga dadinma zagewa kici kaza kenan tunda ba biyana zakiyi ba, wake up pls"
Girgiza kai tayi tana lumshe idanuwanta,
"Na koshi wallahi, sai da safe zanci...."
"Ok, sleep tight my love, good night...."
Bata amsaba ta gyara kwanciyarta ta hanyar juyawa daya bangaren, shikam yunwa yakeji sosai saboda yau da yunwa yawuni throughout shiyasa ya zauna yaci rabin kaza yasha madara, tashi yayi yashiga bathroom yayi wanka yafito ita dai husnah ko kayan jikinta dakyar ta iya canjawa saboda tsabar bacci da gajiya,shiryawa yayi cikin kayan baccinsa maroon colour masu santsi sannan yatashi yafita, dakin Bilkisu yanufa saboda haka kawai yake jin zuciyarshi bata nutsu da yanayin da Bilkisu ke cikiba shiyasa yasake niyyar komawa dakinta yaganta,
Kamar amafarki taji bude kofa babu shiri ta hadiye kukanta ta toshe bakinta da hannunta guda daya, fitila ya kunna sannan cikin sassarfa yakarasa gaban gadon da take lullube ta wani tukunkune wuri daya,
"Billy....." Taji yafada cikin son jan magana amma sai tayi shiru kamar mai bacci,
"Billy tashi kiji.....kinji"
Nan dinma shiru tayi masa tana shasshekar kuka azuciyarta,
"Wai kina nufin kema kinyi bacci? Ok shikenan good night.....have a nice sweet dream"
Daga haka yajuya yaje ya kashe mata wutar yafita bayan yarufe mata kofa. Yana fita ta cigaba da shasshekar kukanta,kusan daren gaba daya bata samu runtsawa ba har saida asubah takawo jiki lokacinne bacci yasamu nasarar yin gaba da ita, su fahad kuwa tunda yabar dakin Bilkisu yana zuwa ya kwanta kusa da husnah babu jimawa yabi sahunta wurin yin bacci saboda tsabar gajiyar dake tattare dashi sallar asubah makara yayi dan sai wurin 6 sannan ya tashi, yana yin salla yasake kwanciya daidai lokacin ita kuma husnah ta tashi, wanka tayi ta caba ado ta sake kwanciya gefen fahad tana kallonsa yana ta sharar bacci hannunsa kan cikinsa, hamdala ta shiga yi ga ubangijin rahma dan ko yanzu ta mutu tasan Allah ya cika mata burinta, kasancewar jiya da yunwa ta kwana yasata jin cikinta yafara kiran ciroma babu shiri ta tashi tajanyo ledar da fahad yazo da ita adaren jiya, kaji guda biyune aciki amma yaci rabin guda daya sai fresh milk kwali biyu, fresh milk din tafara sha sannan taci rabin kazar da ya ajiye, rasa abinda zatayi tayi gashi takasa komawa bacci kuma lokacin karfe bakwai da wasu mintuna wadanda bazasu gaza biyar ba, tana nan kwance tana kallonsa har shima yafarka hada ido sukayi tayi masa gwalo, hannu ya mika mata amma sai ta gagara kama nashi saboda yau jinta take awani takure duk da ba yau tafara kama hannunshi ba amma dai na yau ya banbanta da na kullum, jikinsa ya matso da ita yana tsokanarta da idanuwanshi,
"Kin ci abinci?" Ya tambayeta ahankali, daga kai tayi sannan tace "ehh"
"Husnah kenan wai duk kinyi laushi why? Dan Allah kidaina tsorona,bari ma ki gani wanka zanyi infita..." Daga haka yatashi yawuce toilet kafin yafito ta dan gyaggyara dakin duk da babu wani datti da yayi sai dai dan abinda ba arasaba. Falo ta dan leka tana sa ran ko zata ga matar gidan amma shiru babu motsin kowa, kafin takoma daki fahad yashirya saima da ta daidaci cewar ya shirya sannan tashiga dakin, yana tsaye gaban mirror dinta yana karya hularshi da zai saka,
"Ya fahad ina kwana?" Tafada tana murmushi sannan tana kallonsa,
"Lafiya lau husnatah, ya bakunta?"
Dariya tayi tazauna agefen gadon tana kallonsa ta cikin mirror shima kallonta yayi yasakar mata murmushi sannan yajiyo,
"Bari induba hajjaju ko ta tashi..." Kai ta daga masa hakan yabashi damar wucewa yafita, dakin Bilkisu yabude yashiga da sallama akan labbansa, tana zaune gefen gado tana shafa mai da alama daga wanka tafito sai dai fuskarta duk a dan kumbure,
"Ashe kin tashi? Yakike?", dan tsuke fuskarta tayi saboda tasan rainin wayon nashi yazo yimata inbanda haka menene nashi na wani cemata yatake, jin bata tanka masa ba kuma taki kallonshi yasashi dan matsawa gab da ita,
"Billy yakika tashi...?"
Sam kin yarda ta kalleshi tayi saboda bata son yaga yanayin da idanuwanta ke ciki, har yagama neman maganarshi yafita bata tanka ba kuma bata kalleshi ba, wurin husnah yakoma yayi mata sallama yafita. Fitarshi babu jimawa su Anty Fauziyya sukazo da sauran yan uwan husnah wadanda suka kwana agidansu fahad, food flask din da aka zubowa kowa breakfast dinshi daban, anty asabe ce tashiga wurin Bilkisu takai mata nata, basu dade agidanba suka tafi sai lokacin da zasu tafi sannan Bilkisu tafito ta rakasu bakin kofa sannan takoma ciki tayi kwanciyarta, haka tawuni adaki a kwance dolece kawai take tadata ango kuwa bashi yadawo gidanba sai dare saboda anata baki yan uwa da abokan arziki duk wanda yaje gidan ya Abba to gidan fahad zai zarto shiyasa husnah yau tasha baki har ta godewa Allah amma fa Sam bata ga bilkisu ba hakan yasa mata tunani aranta na anya kuwa ko lafiya?.
Lokacin da yadawo dakin Bilkisu yashiga har lokacin tana kwance bakinta akekashe alamun bata ci komaiba, zama yayi saman bedside drewar yana kallonta,
"Kinci abinci ne?" Wani kallo tajuya tayi masa sannan takawar da kanta duk sai yaga tayi masa wani iri kamar marar lafiya,
"Dan Allah kici abinci rabin raina..." Yafada yana dariya shiru tayi masa, tashi yayi yafita yana fita taja dan siririn tsaki tagyara kwanciyarta, shi kam yana can suna zuba love da husnah dan yana kwance dare dare akan kafafunta tana bashi labarin irin bakin da tasha yau, daga nan bai sake fitaba sai dai idan salla zaije, ana yin sallar ishah kuwa yarufe gida yashiga gida yana tunanin ya kamata ya hada husnah da Bilkisu inyaso ko gaisawace suyi, yana shiga dakin husnah yaga tasha wata kwalliyar kamar bata kwanciya bacci ba, saida suka gama hira suka ci abinci yayi shirin bacci sannan yashiga dakin Bilkisu, itama tuni tayi shirin baccin tana zaune tsakiyar gadonta tana cin abincin da aka kawo musu daga gidansu fahad,
"Billy husnah zata zo ta gaisheki..."
"Ina ciwo ne?" Ta tambaya batare da ta kalleshi ba,
"A'a" yabata amsa,
"To bana bukata, ko zamana takeyi agidan?
"Allah yabaki hakuri, inzo muci abincin?"
Nan kuma bata tankaba saboda taga nema yake ya maidata wata bi ta nan, yana fita ta tashi tamayar da kofarta ta kulle, daren yau dai babu laifi ta dan samu damar yin bacci da wuri saboda jiya batayi ba yayinda ango da amarya ke can suna debewa junansu kewa danma dai har yanzu amaryar bata samu tsarki ba amma duk da haka an aikata abinda ba arasa ba, fahad baiyi bacci da wuriba yanata tunani wato dan adam yana nashi ne Allah na nasa, shi ko acikin mafarki bai taba zaton cewa zaiyi tarayya da wata mace koma bayan Bilkisu ba ashe husnah matarsa ce bai saniba sai yanzu. Washe garima haka Bilkisu tawuni curr adaki abinci kuma daga gidansu fahad ake kawowa, gaba daya zaman gidan ya isheta ya gundireta yakuma gama fita akanta, saida husnah tayi kwana uku gidan sannan suka hadu, ita Bilkisu tafito ita kuma husnah na zaune falo da waya a hannunta tana yin game, sama sama suka gaisa Bilkisu tawuce kitchen tayi abinda zatayi tafito, daren ranar fahad ya sameta da maganar girki domin yakamata husnah tafara girkinta adaina kawo musu daga gidansu fahad acewarta shine yake tambayar Bilkisu ya abin zai kasance,
"Ni zan dafawa matarka abincin da zata ci? Tabdijam to wallahi bazai yuyu ba, kowa yayi girkinsa final.... "