Sashe 33
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Haba hamood ina zakaje awannan daren? Ita wannan din wacece? Menene matsayinta agareka? Meye hadinka da ita da har zatazo ta fitar dakai daga cikin gidanka a wannan daren....?"
Bai samu damar amsa mata tarin tambayoyin da ta jero masa ba sai kwaya daya inda yafurta,
"Matata ce....."
Kafin bilkisu tayi magana wise ta rigata,
"Kana bata min lokaci fa..."
Bai sake bi takan bilkisu ba yawuce gaba wise na biye dashi kamar wani danta, akan idon bilkisu suka shiga motar wise suka bar gidan, kallonta ta maida kan agogo karfe 1 saura nadare......
*Dan Allah idan har kin san baki siyaba karki karanta min littafi domin na siyarwa ne.*
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA....!.*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*30*
****Zama bilkisu tazame tayi awurin tana dafe kanta da hannunta guda daya wanda yasha kunshi radau,
"Wannan wacce irin masiface? Adaren amarcina za azo atafi min da miji abarni ni kadai....."
Agogo tasake kalla nan ta kura masa ido kamar tana son gano amsar tambayarta awurinne domin ko kiftawa batayi, tsabar bakin cikima ko tsoro nemarsa tayi ta rasa dadinta daya dai gidan akwai mai gadi, ganin zaman da take babu abinda zai amfana mata yasata tashi dakyar kanta yayi mata masifar nauyi taja kafarta wadda ta tari jini saboda tsabar zama atakure tawuce cikin bedroom, tana kwanciya idanuwanta suka kai kan wayoyin hamood guda biyu dake kashe ajiye kan bedside drewar sai agogonshi na azurfa wani abu taji yataho ya soke mata zuciyarta sai kuka kamar anbude bakin fanfo, har asubah takai tana hawaye domin tarasa gane da wacce kalma zata kira wannan abinda yafaru shin da wulakanci zata kirashi ko kuma da tozarci?.
Har asuba bata samu ta runtsa ba saida tayi salla ne bacci ya kwasheta nan kan rug din da tayi sallar, bacci tayi mai cikeda mafarkai daban daban wanda takasa tunawa bayan ta tashi, wanka tayi ta shirya duk zuciyarta akuntace domin tana cikin matsananciyar damuwa, sake kwanciya tayi domin bata san me zatayi ba kwata kwata ahaka har rana tafara yi nan yunwa tasoma damunta, fita tayi zuwa falon dake kasa,abubuwan da hamood yashigo dasu adaren jiya su ta dan kakkarima taci tsabar bakin ciki ko wayarta bata kunna ba domin bata bukatar kowa ya kirata. Karfe sha biyu da wani abu su iyallo sukazo itada dasu Hindu sun rakota zatayi ma bilkisu sallama saboda ayau zata koma garko, su elmustapha ne suka kawosu shiyasa bilkisu ta dan samu ta warware daga kuncin da take ciki domin ko ba komai ganin yan gidansu yasata farin ciki,
"To shikuma mamuda yake ko hamidan yana ina?"
Iyallo tajefeta da tambaya tana tsaka da kwankwadar lemon kankana mai sanyi, saida kowa yayi dariya jin sunan da iyallo ta kakabawa hamood,
"Yanzun nan yafita iyallo dan bamu san zakuzo bane ma da babu inda zaije sai ya jiraku...."
"Allah sarki ai babu komai, nidai abinda zan fada miki shine kinga dai ke yanzu ba yarinya bace, dan haka ke zaki yiwa kanki fada basai kin jira wani yayi miki ba, kiyi hakuri ki zamanki adakinki kamar sauran yan uwanki..... Allah yakawo kazantar daki, mai gado kema Allah yabaki magaji, Allah yabaki yara masu albarka kisamu na aike....." Ajiye lemon hannunta tayi tahau matsar ido nan maama ta dunguri meenah suka hada kai suna kuskus,
"Hajiya iyallo to kuma menene abin kuka?... Kufa matsalata daku bakwa rabo da koke koke...." Inji emustapha,
"Ai sabgar mata akwai ban haushi malam.... Komai abin kukane... Suyita yiwa mutane kuka akan abinda bai kai yakawo ba" El'ameen yakarbe zancen,
"Kai naci gidanku.....kai mai sunan malam jakar ubaka..."
Dariya el'ameen yayi yamike yana gyara earpiece din dake kunnensa,
"Oho dai idanma kin zagi ubana ai danki kika zaga...."
Salati iyallo tafara yi tana fadan wai ita ba danta ta zaga ba domin danta dan albarkane yakaita hajji yakaita umarah sannan yagina mata gida mai kyau dan haka babu abinda zatace dashi sai Allah yayi albarka, duk da bilkisu natare da damuwa amma caftar su iyallo da jikokinta tasata nishadi ba kadan ba, kayan zakin da suka kawo mata cikin bokitai suka shigar mata kitchen sannan suka tafi ai kuwa ji tayi kamar ta dora hannu aka tafasa ihu. Har kofar gida ta rakasu saida taga tafiyarsu sannan takoma ciki, kwanciya ta sake yi saida aka kira sallar azahar sannan tatashi, tana cikin yin sallar taji zuwan wasu bakin shiyasa ta hanzarta ta idar tafito, yan gidansu hamood ne da matar uncle dinsa da yaran gidan guda biyar sudinma sallama suka zo yimata saboda zasu koma birnin tarayya ayau, basu wani jima ba shiyasa ko snacks din da takawo musu basu ciba sai packaging dinshi tayi musu suka tafi dashi. Ahaka takarasa wuninta cikin rashin walwala da bacin rai har dare babu hamood babu labarinsa gashi yabar wayoyinsa duk agida bare ta tuntubeshi taji a ina yake. Daren yauma sai bacci barawo amma tajima batayi bacciba tanata sakawa da kuncewa, washe gari ma hakance ta kasance hamood shiru har kirjin azahar dai dai lokacin khulsum tazo tanata tsokanar bilkisu ita dai bata da tacewa saboda damuwar dake cikin ranta tafi gaban kwatantawa,
"Wai ina angonne inyi masa tsiya, shikenan sai ya boye min kawata ko awaya inkasa samunta?"
Murmushin yake na dole bilkisu tayi tace,
"Ai kuwa yafice tun sassafe saboda yanada uzuri kin san kamfanin saida motocin uncle dinsa shike kula dashi to shine aka kirashi...."
"Ahhh cewa zakiyi yatafi yasamo muku kudi dai labour..."
Dariyar da ta tsaya a iya fatar baki kadai tayi,da taimakon khulsum suka dan girka abinci bayan tabawa mai gadi yaje ya iyo mata cefane, har yamma khulsum na gidan tana bata labarin saurayinta wanda take son aure, ita dai bilkisu kawai tana zaune ne amma gaba daya tunaninta na ga hamood kacokan tana ta son sanin inda yatafi, daf da magriba khulsum tatafi nan kuma taci gaba da zaman kadaici da damuwa.
Wasa wasa saida hamood yayi kwanaki hudu sannan sai gashi da ranar Allah yashigo yasha farar shadda kal sabuwa fil da hula harda dan farin glashinsa na ido dayake shima kyakkyawane babu laifi domin black beauty ne ga hanci, mikewa bilkisu tayi cikeda fushi ta juya masa baya alamun tana cikin bacin rai, kamota yayi yadora akan cinyarsa,
"Hamood ashe haka amana da soyayya suka ce?"
"Sweetheart.... Kiyi hakuri.... Tun farko ban sanar dake cewa inada mata ba wallahi babu yanda zanyi ne.... Hadin iyaye ne shiyasa kawai ban fito na fada miki ba...."
"Ni hamood ba wannan ne damuwata ba, damuwata shine yaza ayi adaren amarcinmu wata mata tazo ta tisaka agaba tatafi dakai kuma wai kabita baka dawoba saida ka shafe kwanaki hudu..... Saboda Allah kun yimin adalci?"
"Kiyi hakuri sweetheart...ai ban sanar da ita bane shiyasa amma nayiwa tufkar hanci hakan bazata kara faruwa ba...."
Duk da haka nunawa tayi bata hakura ba nan yasoma lallashinta wanda daga karshe lallashin yasoma canja salo domin gaba daya ya canja akalarsa izuwa wani fannin daban, bedroom din dake cikin falon suka yiwa shigar bazata domin farantawa junansu, al'amari yafara nisa amma kuma sai me kwata kwata hamood ji yayi baida kuzarin da zai iya aiwatar da wani abu awannan lokaci domin gaba daya halittarsa bata koda motsi tamkar lagwanin da yayi shekara acikin kalanzir yayi laushi haka yazama nanfa wani tashin hankali da damuwa da bacin rai suka dirar musu daga bilkisu harshi domin kowa anasa hasashen laifin dan uwansa yake gani kokuma matsalar kowa gani yake daga daya bangaren ne banasa ba.......
*Kamar da wasa na siyarwa ne, me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA....!*
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*31*
****Cikin fushi da bacin rai hamood yafice daga cikin dakin yakoma falo daga shi sai gajeren wando, sam batayi yunkurin binsa ba saboda ita dinma cike take da bacin rai, kusan mintuna ishirin ta debe ahaka kafin tatashi saboda jin anata kiraye kirayen sallar la'asar, lokacin da tafito falon abinda idanuwanta suka gane mata yayi masifar razanata, hamood zaune yadora daya akan daya idanuwansa jajur hannunsa rikeda tabar sigari yana busawa shiyasa gaba daya falon ya turnuke da warin sigarin,
Gabansa taje gabanta sai faduwa yake zuciyarta na bugawa,
"Hamood.... Meye haka kakeyi? Subhanallahi dama kana shan sigari.....?"
"Idan raina yabaci ba.... Ai dole nasha sigari mai gado... Irin wannan zafi da kika hada min ai yazama confirm in dan wartsake...."
Gaba daya ita rasa ma abinda zatace tayi saboda mamaki da takaici shiyasa kawai tawuce sama tashiga dakinta tayi wanka tazo tayi salla tana idarwa ta sauko amma wayam babu hamood wato har yasake komawa inda yafito batare da yayi mata sallama ba ko? Ta ayyana hakan acikin ranta, sosai taji hakan yayi mata ciwo, kitchen tawuce ta debo snacks tazo ta zauna taci. Zaman kadaici tayi har dare yayi tanata zuba idon hamood shiru gashi bai dauki wayoyinshi ba kai asalima tunda yashigo gidan bai leka ko cikin bedroom ba iyakscinsa bedroom din da ke kasa, har lokacin bacci yayi taje ta kwanta hamood bai shigo cikin gidanba ita kanta gaba daya takasa bacci daren wannan rana sai misalin karfe 12 nadare hamood yashigo cikin gidan cikin yanayin da yakara tsorata bilkisu game dashi domin acikin maye yashigo har dakinta yafado yana hada hanya yana layi,
Cikin zazzare ido tamike zaune tana kallonsa bakinta yana rawa,
"Hamood.... Innalillahi.... Wai dama kana shaye shaye ne? Haba hamood meyasa zakayi min haka? Wannan wacce irin rayuwace?...."
Cikin maye ya nunata da dan yatsa,
"Babu ruwanki da rayuwata..... Ko kabarinmu daya? Bana son takurawa...."
Mikewa tsaye tayi cikeda damuwa da bacin rai,
"Ai ko ba kabarinmu daya ba yazama dole infada maka gaskiya amatsayina na abokiyar zamanka, yau kwata kwata kwananmu hudu zuwa biyar da aure amma gashi nan munanan dabi'unka sun fara bayyana... Seriously am highly disappointed....."
Ai kafin tarufe bakinta ya dauketa da wani gigitaccen mari, dafe kuncinta tayi cikeda mamaki baki abude tana kallonsa,nan ya nunata da dan yatsa,
"Idan kika kara zagina sai na ballaki....."
Bai samu damar amsa mata tarin tambayoyin da ta jero masa ba sai kwaya daya inda yafurta,
"Matata ce....."
Kafin bilkisu tayi magana wise ta rigata,
"Kana bata min lokaci fa..."
Bai sake bi takan bilkisu ba yawuce gaba wise na biye dashi kamar wani danta, akan idon bilkisu suka shiga motar wise suka bar gidan, kallonta ta maida kan agogo karfe 1 saura nadare......
*Dan Allah idan har kin san baki siyaba karki karanta min littafi domin na siyarwa ne.*
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA....!.*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*30*
****Zama bilkisu tazame tayi awurin tana dafe kanta da hannunta guda daya wanda yasha kunshi radau,
"Wannan wacce irin masiface? Adaren amarcina za azo atafi min da miji abarni ni kadai....."
Agogo tasake kalla nan ta kura masa ido kamar tana son gano amsar tambayarta awurinne domin ko kiftawa batayi, tsabar bakin cikima ko tsoro nemarsa tayi ta rasa dadinta daya dai gidan akwai mai gadi, ganin zaman da take babu abinda zai amfana mata yasata tashi dakyar kanta yayi mata masifar nauyi taja kafarta wadda ta tari jini saboda tsabar zama atakure tawuce cikin bedroom, tana kwanciya idanuwanta suka kai kan wayoyin hamood guda biyu dake kashe ajiye kan bedside drewar sai agogonshi na azurfa wani abu taji yataho ya soke mata zuciyarta sai kuka kamar anbude bakin fanfo, har asubah takai tana hawaye domin tarasa gane da wacce kalma zata kira wannan abinda yafaru shin da wulakanci zata kirashi ko kuma da tozarci?.
Har asuba bata samu ta runtsa ba saida tayi salla ne bacci ya kwasheta nan kan rug din da tayi sallar, bacci tayi mai cikeda mafarkai daban daban wanda takasa tunawa bayan ta tashi, wanka tayi ta shirya duk zuciyarta akuntace domin tana cikin matsananciyar damuwa, sake kwanciya tayi domin bata san me zatayi ba kwata kwata ahaka har rana tafara yi nan yunwa tasoma damunta, fita tayi zuwa falon dake kasa,abubuwan da hamood yashigo dasu adaren jiya su ta dan kakkarima taci tsabar bakin ciki ko wayarta bata kunna ba domin bata bukatar kowa ya kirata. Karfe sha biyu da wani abu su iyallo sukazo itada dasu Hindu sun rakota zatayi ma bilkisu sallama saboda ayau zata koma garko, su elmustapha ne suka kawosu shiyasa bilkisu ta dan samu ta warware daga kuncin da take ciki domin ko ba komai ganin yan gidansu yasata farin ciki,
"To shikuma mamuda yake ko hamidan yana ina?"
Iyallo tajefeta da tambaya tana tsaka da kwankwadar lemon kankana mai sanyi, saida kowa yayi dariya jin sunan da iyallo ta kakabawa hamood,
"Yanzun nan yafita iyallo dan bamu san zakuzo bane ma da babu inda zaije sai ya jiraku...."
"Allah sarki ai babu komai, nidai abinda zan fada miki shine kinga dai ke yanzu ba yarinya bace, dan haka ke zaki yiwa kanki fada basai kin jira wani yayi miki ba, kiyi hakuri ki zamanki adakinki kamar sauran yan uwanki..... Allah yakawo kazantar daki, mai gado kema Allah yabaki magaji, Allah yabaki yara masu albarka kisamu na aike....." Ajiye lemon hannunta tayi tahau matsar ido nan maama ta dunguri meenah suka hada kai suna kuskus,
"Hajiya iyallo to kuma menene abin kuka?... Kufa matsalata daku bakwa rabo da koke koke...." Inji emustapha,
"Ai sabgar mata akwai ban haushi malam.... Komai abin kukane... Suyita yiwa mutane kuka akan abinda bai kai yakawo ba" El'ameen yakarbe zancen,
"Kai naci gidanku.....kai mai sunan malam jakar ubaka..."
Dariya el'ameen yayi yamike yana gyara earpiece din dake kunnensa,
"Oho dai idanma kin zagi ubana ai danki kika zaga...."
Salati iyallo tafara yi tana fadan wai ita ba danta ta zaga ba domin danta dan albarkane yakaita hajji yakaita umarah sannan yagina mata gida mai kyau dan haka babu abinda zatace dashi sai Allah yayi albarka, duk da bilkisu natare da damuwa amma caftar su iyallo da jikokinta tasata nishadi ba kadan ba, kayan zakin da suka kawo mata cikin bokitai suka shigar mata kitchen sannan suka tafi ai kuwa ji tayi kamar ta dora hannu aka tafasa ihu. Har kofar gida ta rakasu saida taga tafiyarsu sannan takoma ciki, kwanciya ta sake yi saida aka kira sallar azahar sannan tatashi, tana cikin yin sallar taji zuwan wasu bakin shiyasa ta hanzarta ta idar tafito, yan gidansu hamood ne da matar uncle dinsa da yaran gidan guda biyar sudinma sallama suka zo yimata saboda zasu koma birnin tarayya ayau, basu wani jima ba shiyasa ko snacks din da takawo musu basu ciba sai packaging dinshi tayi musu suka tafi dashi. Ahaka takarasa wuninta cikin rashin walwala da bacin rai har dare babu hamood babu labarinsa gashi yabar wayoyinsa duk agida bare ta tuntubeshi taji a ina yake. Daren yauma sai bacci barawo amma tajima batayi bacciba tanata sakawa da kuncewa, washe gari ma hakance ta kasance hamood shiru har kirjin azahar dai dai lokacin khulsum tazo tanata tsokanar bilkisu ita dai bata da tacewa saboda damuwar dake cikin ranta tafi gaban kwatantawa,
"Wai ina angonne inyi masa tsiya, shikenan sai ya boye min kawata ko awaya inkasa samunta?"
Murmushin yake na dole bilkisu tayi tace,
"Ai kuwa yafice tun sassafe saboda yanada uzuri kin san kamfanin saida motocin uncle dinsa shike kula dashi to shine aka kirashi...."
"Ahhh cewa zakiyi yatafi yasamo muku kudi dai labour..."
Dariyar da ta tsaya a iya fatar baki kadai tayi,da taimakon khulsum suka dan girka abinci bayan tabawa mai gadi yaje ya iyo mata cefane, har yamma khulsum na gidan tana bata labarin saurayinta wanda take son aure, ita dai bilkisu kawai tana zaune ne amma gaba daya tunaninta na ga hamood kacokan tana ta son sanin inda yatafi, daf da magriba khulsum tatafi nan kuma taci gaba da zaman kadaici da damuwa.
Wasa wasa saida hamood yayi kwanaki hudu sannan sai gashi da ranar Allah yashigo yasha farar shadda kal sabuwa fil da hula harda dan farin glashinsa na ido dayake shima kyakkyawane babu laifi domin black beauty ne ga hanci, mikewa bilkisu tayi cikeda fushi ta juya masa baya alamun tana cikin bacin rai, kamota yayi yadora akan cinyarsa,
"Hamood ashe haka amana da soyayya suka ce?"
"Sweetheart.... Kiyi hakuri.... Tun farko ban sanar dake cewa inada mata ba wallahi babu yanda zanyi ne.... Hadin iyaye ne shiyasa kawai ban fito na fada miki ba...."
"Ni hamood ba wannan ne damuwata ba, damuwata shine yaza ayi adaren amarcinmu wata mata tazo ta tisaka agaba tatafi dakai kuma wai kabita baka dawoba saida ka shafe kwanaki hudu..... Saboda Allah kun yimin adalci?"
"Kiyi hakuri sweetheart...ai ban sanar da ita bane shiyasa amma nayiwa tufkar hanci hakan bazata kara faruwa ba...."
Duk da haka nunawa tayi bata hakura ba nan yasoma lallashinta wanda daga karshe lallashin yasoma canja salo domin gaba daya ya canja akalarsa izuwa wani fannin daban, bedroom din dake cikin falon suka yiwa shigar bazata domin farantawa junansu, al'amari yafara nisa amma kuma sai me kwata kwata hamood ji yayi baida kuzarin da zai iya aiwatar da wani abu awannan lokaci domin gaba daya halittarsa bata koda motsi tamkar lagwanin da yayi shekara acikin kalanzir yayi laushi haka yazama nanfa wani tashin hankali da damuwa da bacin rai suka dirar musu daga bilkisu harshi domin kowa anasa hasashen laifin dan uwansa yake gani kokuma matsalar kowa gani yake daga daya bangaren ne banasa ba.......
*Kamar da wasa na siyarwa ne, me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA....!*
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*31*
****Cikin fushi da bacin rai hamood yafice daga cikin dakin yakoma falo daga shi sai gajeren wando, sam batayi yunkurin binsa ba saboda ita dinma cike take da bacin rai, kusan mintuna ishirin ta debe ahaka kafin tatashi saboda jin anata kiraye kirayen sallar la'asar, lokacin da tafito falon abinda idanuwanta suka gane mata yayi masifar razanata, hamood zaune yadora daya akan daya idanuwansa jajur hannunsa rikeda tabar sigari yana busawa shiyasa gaba daya falon ya turnuke da warin sigarin,
Gabansa taje gabanta sai faduwa yake zuciyarta na bugawa,
"Hamood.... Meye haka kakeyi? Subhanallahi dama kana shan sigari.....?"
"Idan raina yabaci ba.... Ai dole nasha sigari mai gado... Irin wannan zafi da kika hada min ai yazama confirm in dan wartsake...."
Gaba daya ita rasa ma abinda zatace tayi saboda mamaki da takaici shiyasa kawai tawuce sama tashiga dakinta tayi wanka tazo tayi salla tana idarwa ta sauko amma wayam babu hamood wato har yasake komawa inda yafito batare da yayi mata sallama ba ko? Ta ayyana hakan acikin ranta, sosai taji hakan yayi mata ciwo, kitchen tawuce ta debo snacks tazo ta zauna taci. Zaman kadaici tayi har dare yayi tanata zuba idon hamood shiru gashi bai dauki wayoyinshi ba kai asalima tunda yashigo gidan bai leka ko cikin bedroom ba iyakscinsa bedroom din da ke kasa, har lokacin bacci yayi taje ta kwanta hamood bai shigo cikin gidanba ita kanta gaba daya takasa bacci daren wannan rana sai misalin karfe 12 nadare hamood yashigo cikin gidan cikin yanayin da yakara tsorata bilkisu game dashi domin acikin maye yashigo har dakinta yafado yana hada hanya yana layi,
Cikin zazzare ido tamike zaune tana kallonsa bakinta yana rawa,
"Hamood.... Innalillahi.... Wai dama kana shaye shaye ne? Haba hamood meyasa zakayi min haka? Wannan wacce irin rayuwace?...."
Cikin maye ya nunata da dan yatsa,
"Babu ruwanki da rayuwata..... Ko kabarinmu daya? Bana son takurawa...."
Mikewa tsaye tayi cikeda damuwa da bacin rai,
"Ai ko ba kabarinmu daya ba yazama dole infada maka gaskiya amatsayina na abokiyar zamanka, yau kwata kwata kwananmu hudu zuwa biyar da aure amma gashi nan munanan dabi'unka sun fara bayyana... Seriously am highly disappointed....."
Ai kafin tarufe bakinta ya dauketa da wani gigitaccen mari, dafe kuncinta tayi cikeda mamaki baki abude tana kallonsa,nan ya nunata da dan yatsa,
"Idan kika kara zagina sai na ballaki....."