Sashe 23
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Katse wayar tayi tana kwafa wato danma yasamu ta tambayeshi shine harda wani hanawa, bata je dinba ta koma gida ta dan huta sannan ta tada shirin dafa alala domin yau shi take kwadayi, shi kuwa fahad ba karamin fasuwa kansa yayiba bilkisu ta kirashi tana neman izini yanzu sake jin kansa yake yi amatsayin boss, bai lura da fushin da husna keyiba tunda ta fahimci matarsa ce ta kira. La'asar sakaliya yakoma gida bilkisu na falo tana bacci dan kwanciya tayi kuma bacci yayi gaba da ita riga ce ajikinta body hug da yar skirt marar nauyi amma tasa karamin hijab, bai tasheta ba yawuce yazubo abinci alala yagani yasha kwai da vegetables sai kamshi yake guda hudu yazubo yazauna yatashi dasu sannan yashiga wanka agurguje yafito yasa kayan ball dinsa lokacin bilkisu tatashi karar wayarta ne yatadata meenah ce ta kirata,
Kallonsa tayi daga sama har kasa,
"Kai da islamiyya ma kashiga wallahi tafi maka wannan zuwa filin kwallon"
Murmushi yayi yazauna yana saka safa da combos dinshi,
"Hajjaju kenan, tunda kince inshiga to zan shiga din"
Bata kara cewa komai ba shima haka har yagama yatashi yafita.
Haka zaman nasu yaci gaba da kasancewa,watansu daya da aure taje gida tawuni cur har dare lokacin ana sa ran ganin watan Ramadan nanda kwanaki uku zuwa hudu ammah kuwa mahaifiyarta har yau bata taka taje gidan ba, duk wata siyayya da suke bukata fahad ya kokarta ya iyota dama ba wasu kaya masu yawa bane domin sunada kayan abinci enough kawai dai sai dan abinda ba arasa ba, ranar da aka tashi da azumi ranar bilkisu tatashi da period asanyaye take komai sakamakon ciwon da mararta ke danyi mata kadan, ruwan zafi ta dafa tasha lipton ko zataji dan dama dama shi dai gogan yana kwance abinsa yanata bacci shiyasa bata yarda ta dafa komai ba tabari har saida yatashi yayi wanka yafita duk yayi wani kalar tausayi kamar yauce ranar farko da yafara azumin, saida ta tabbatar yafita sannan tatashi ta dora indomie, ta juye indomie din tana soya kwai sai gashi yadawo yamanta key din drewar shagonsu wadda suke ajiye kayan mutane aciki idan ankawo musu dinki,
Jin kamshi ya cika gidan yasashi binta kitchen din bayan ya dauki key din,
"Ranki yadade ke bakya azuminne ko kema yar ganin watance?"
Banza tayi dashi taci gaba da abinda takeyi amma harga Allah bataso yasan bata azumi ba,
"Ko dai.....!"
Juyowa tayi ta antaya masa harara hakan tasa yayi shiru,
"Allah yabaki hakuri mantawa nayi ashe suhur zakiyi, ayi suhur lafiya"
Bai jira tajiyo ba yagudu yabar gidan yana dariya, shi dai yasha jin malamai suna cewa mata masu al'ada basa azumi wato itama hajjaju yau hakan take kenan, tunda yabar gidan bai dawoba sai da aka kusa shan ruwa, a kitchen ya jiyota tana aiki shikam yau duk yayi laushi ga uban dinkunan da ya yanyanka shiyasa can ma yabarosu sai bayan ansha ruwa zai koma yafara hadawa. Yajima akwance ga kayan da yazo dasu amma yakasa tashi yakai mata ita kuma bata san yadawo ba, saida ta dora kosai kafin man yayi zafi tafito daukar wayarta zata kirashi tace yataho mata da mayonnaise taganshi kwance, yau kam an zuba rana ga zafi shiyasa azumin ke wahalar da mutane, kamar zatayi dariya amma ta danne ta wuce tana yimasa sannu, bayan tadawo ta dauki ledar da yashigo da ita tawuce kitchen wanda fruits ne aciki yasiyo, dakyar ya iya tashi yayi wanka lokacin yaji karfin jikinsa, yana gaban mirror zaune yaji wayarshi na kara, ganin salim ne yasashi dauka bayan yayi tagumin dole,
"Abokina gani nan zanzo asha ruwa dani fa..."
"Sai kazo to"
Daga haka yakatse wayar duk atunaninshi da wasa salim yake bayan yagama shiryawa yasa three quarter da t shirt yafito falo yasake kwanciya babu jimawa yaji ana knocking akasalance yaje yabude salim din kuwa yagani dagaske, cikin murmushi ya mika masa hannu sukayi musabaha yashigo dashi har falo,bedroom yashiga yadauko hijab din bilkisu yabita kitchen, ya dora mata saman kafadarta, juyowa tayi ta kalleshi yau baya magana saboda azumi na dukanshi,
"Salim ne yazo" abinda ya iya fada kenan yajuya yafita, saida tagama komai sannan aka kira salla, fruit salad ne bata jima da gamawa ba lokacin kayan ta tattaro gaba daya ta kawo musu falo har lokacin gogan akwance yake yakasa tashi shiyasa salim ya kalleta yana dariya bayan sun gaisa yace,
"Hajjaju wannan fa yau sai kinzo kin dagashi dan yakasa tashi"
Dariya tayi takoma kitchen takawo sauran kayan ta ajiye musu sannan ta kalli fahad wanda ke kwance rub da ciki,
"Tashi kasha ruwan mana...."
Hannu yamika mata saboda ganin idon salim bata kiba takama nashi yatashi zaune azuciyarsa yana cewa,
"Wannan badan ansha ruwaba ai sunan azumina karyayye irin wannan laushi haka"
Kunu ta zuba masa ta mika masa sannan tace,
"Karka sha abu mai sanyi yanzu sai an dan jima, kafara shan mai zafi tukunna"
Kai yadaga mata shi dai salim tuni yahada tea dinsa yana sha da kosai, juyawa tayi tawuce daki tabasu wuri tana zuwa tashiga wanka. Su fahad kuwa bayan ciki ya dan dauka fanfon waje sukaje sukayi alwala sannan sukazo sukayi salla bayan sun idar suka dora da ciye ciyensu sai lokacin bakin fahad yabude sunata hira da salim, bilkisu na fitowa sanye da hijab har kasa tanata zuba kamshi fahad ya kalleta ya dage girarshi guda daya cikeda tsokana yace,
"Hajjaju sannu da shan ruwa, ansha ruwa lafiya?"
Ita dashi sun san meyake nufi amma shi salim bai saniba shiyasa shima yayi mata sannu da shan ruwan, iya na salim din kawai ta amsa tawuce kitchen tazubo dankali da kosai tafito,
"Ranki yadade sannu da shan ruwa fa naketa yimiki amma kin shareni laifin me nayi?"
"Yawwa sannu"
Murmushi yayi ya saci kallonta ta zabga masa harara, tana jinsu sai surutu sukeyi kasancewar sun koshi, suna gamawa suka mike zasu fita, kaya fahad yaje yasauya sannan suka fice yana sake tsokanarta,
"Hajjaju yau mun kai daya ko?"
"Goma aka kai" Tafada cikin gatse,
Dariya yayi yaja hannun salim suka fita, itama wurinda suka ci abincin ta zauna ta kintsa sannan ta kwashe kayan takai kitchen tawuce daki,takardar hutunta take son turawa ta mail domin daga gobe ko jibi take son farawa.....
*Dan Allah idan har baki biya kudin littafin nanba karki karanta hakkin wasu domin na siyarwa ne.*
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO*
*KAMAR DA WASA....!*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*23*
***Bai samu yadawo gidanba sai wurin karfe 10 bilkisu duk tsoro ya isheta domin bata taba zama agidan ita kadai da daddare ba,tana daki tarufe da key yashigo kwankwasa mata kofa yayi dakyar ta tashi ta bude dan tsoro tana ganin shine ta harareshi,cikin alamun atsorace take tafurta,
"Ina kaje kakai dare haka?"
"Ranki yadade daga shago nake wallahi, bayan mun fita daga nan salla mukaje mukayi daga can kuma shine naje gida nayiwa su ayiyah barka da shan ruwa shine nawuce shago"
Bashi hanya tayi yawuce ciki tana cewa
"To gaskiya kar ka kara kaiwa haka awaje"
"To ranki yadade"
Falo yasake fitowa yawuce kitchen yazubo abinci yaci sannan yayi shirin bacci, da asuba itace ta tasheshi ya tashi yayi suhur, kallonta yayi tana kwance kan gado tana shirin yin wani baccin bayan yayi brush yafito,
"Nima anya gobe zanyi azumin nan kuwa? To naga wadanda suka fini ma basayi"
Tana jinsa tayi biris dashi daga karshe yafice yaje yayi suhur din saida yayi sallar asubah sannan ya kwanta. Washe gari tafara hutunta kamar yadda ta nema, kullum tare suke shan ruwa da salim ranar da akayi azumi na biyar sukaje gidansu fahad suka yimusu sannu da shan ruwa bayan Bilkisu ta siya musu kayan tea, shi kuwa fahad kayan marmari yasiya musu suka kai musu washe gari kuma suka je gidansu Bilkisu can dinma kayan marmarin fahad yasiya cikin manyan ledoji suka kai ita surukuntar fahad da ammah dariya take bata domin basa sakewa da juna, har karfe 9 nadare suna gidan wurin goma suka dawo gida. Bilkisu sai da tasha azumi bakwai ana takwas ta dauka danma ranar ansamu ni'ima agari dan har ruwa aka sheka shiyasa bata wani jishi ba sosai, bayan ansha ruwa fahad ya fara halin nasa na tsokana, har bedroom yabita yabar salim afalo,
"Hajjaju yau wasu takwas suka kaifa wasu kuma bakwai wasu shida ke kuma first ramadan yau"
Harararshi tayi ta gyara zamanta,
"Kafita daga idona..."
Ficewa yayi daga dakin gaba daya yana dariya, akwana atashi haka azumin yafara tafiya domin har anfara lissafin salla, duk kannenta babu wadda batazo ba ita da mijinta sunyi mata barka da shan ruwa ba, azumi yaraba tsakiya abba ya aiko musu da kaya kaca kaca kayan tea ne, kayan abinci da sauransu ba ita kadaiba harsu mamaa kowa ya aika masa dashi. Tunda salla ta taho fahad yazama busy domin aiki yayi musu yawa dama duk karshen azumi ashago suke kwana su kwana suna aiki amma wannan karon saboda bilkisu yahakura sai dai yataho da kayan gida yayita yankawa da safe idan yafita sai ya dinka, ana saura kwana biyar salla yake tambayarta wai ita bazata yi dinkin salla ba ehh tace masa kawai, har ana igobe salla bai samu kansa ba cefane ma sai yaro yatura yace yaje tafada masa duk abinda take bukata sai yazo yabashi kudin yaje yasiyo yakai mata, zamansa agidan yanzu kalilan ne, dawowarta daga kunshi kenan itada khulsum dan aiken yazo list tayi tabashi na abubuwan da take bukata domin shinkafa ma ita zata dafa ranar sallar ba tuwoba. Fahad bai dawo gidanba sai 11 nadare domin acanma yasha ruwa yau, ido biyu yasamu bilkisu batayi bacciba domin itama duk vegetables din da zata bukata ta zauna ta gyara gamawarta kenan yashigo amutukar gajiye,atamfa yar ubansu ya dinko mata dark pink mai zanen agogo ajiki, karba tayi tana kallon dinkin da yayi mata riga da skirt fitted, daga atamfar har dinkin sunyi mata kyau,
"Thank you..." Tafada cikin nuna alamun jin dadi, bai amsaba ya kalleta,
"Duk wannan kwalliyar ni aka yiwa?"
Yafada cikeda tsokana,
"Kai kasani..."
Dariya yayi yawuce bathroom domin watsa ruwa. Bayan yafito ya dauki shirgin shimfidarsa yafita,
"Ni wai ko tausayina ma ba ayi kullum akoroni falo hmmm"
Kallonsa tayi daga sama har kasa,
"Kai da islamiyya ma kashiga wallahi tafi maka wannan zuwa filin kwallon"
Murmushi yayi yazauna yana saka safa da combos dinshi,
"Hajjaju kenan, tunda kince inshiga to zan shiga din"
Bata kara cewa komai ba shima haka har yagama yatashi yafita.
Haka zaman nasu yaci gaba da kasancewa,watansu daya da aure taje gida tawuni cur har dare lokacin ana sa ran ganin watan Ramadan nanda kwanaki uku zuwa hudu ammah kuwa mahaifiyarta har yau bata taka taje gidan ba, duk wata siyayya da suke bukata fahad ya kokarta ya iyota dama ba wasu kaya masu yawa bane domin sunada kayan abinci enough kawai dai sai dan abinda ba arasa ba, ranar da aka tashi da azumi ranar bilkisu tatashi da period asanyaye take komai sakamakon ciwon da mararta ke danyi mata kadan, ruwan zafi ta dafa tasha lipton ko zataji dan dama dama shi dai gogan yana kwance abinsa yanata bacci shiyasa bata yarda ta dafa komai ba tabari har saida yatashi yayi wanka yafita duk yayi wani kalar tausayi kamar yauce ranar farko da yafara azumin, saida ta tabbatar yafita sannan tatashi ta dora indomie, ta juye indomie din tana soya kwai sai gashi yadawo yamanta key din drewar shagonsu wadda suke ajiye kayan mutane aciki idan ankawo musu dinki,
Jin kamshi ya cika gidan yasashi binta kitchen din bayan ya dauki key din,
"Ranki yadade ke bakya azuminne ko kema yar ganin watance?"
Banza tayi dashi taci gaba da abinda takeyi amma harga Allah bataso yasan bata azumi ba,
"Ko dai.....!"
Juyowa tayi ta antaya masa harara hakan tasa yayi shiru,
"Allah yabaki hakuri mantawa nayi ashe suhur zakiyi, ayi suhur lafiya"
Bai jira tajiyo ba yagudu yabar gidan yana dariya, shi dai yasha jin malamai suna cewa mata masu al'ada basa azumi wato itama hajjaju yau hakan take kenan, tunda yabar gidan bai dawoba sai da aka kusa shan ruwa, a kitchen ya jiyota tana aiki shikam yau duk yayi laushi ga uban dinkunan da ya yanyanka shiyasa can ma yabarosu sai bayan ansha ruwa zai koma yafara hadawa. Yajima akwance ga kayan da yazo dasu amma yakasa tashi yakai mata ita kuma bata san yadawo ba, saida ta dora kosai kafin man yayi zafi tafito daukar wayarta zata kirashi tace yataho mata da mayonnaise taganshi kwance, yau kam an zuba rana ga zafi shiyasa azumin ke wahalar da mutane, kamar zatayi dariya amma ta danne ta wuce tana yimasa sannu, bayan tadawo ta dauki ledar da yashigo da ita tawuce kitchen wanda fruits ne aciki yasiyo, dakyar ya iya tashi yayi wanka lokacin yaji karfin jikinsa, yana gaban mirror zaune yaji wayarshi na kara, ganin salim ne yasashi dauka bayan yayi tagumin dole,
"Abokina gani nan zanzo asha ruwa dani fa..."
"Sai kazo to"
Daga haka yakatse wayar duk atunaninshi da wasa salim yake bayan yagama shiryawa yasa three quarter da t shirt yafito falo yasake kwanciya babu jimawa yaji ana knocking akasalance yaje yabude salim din kuwa yagani dagaske, cikin murmushi ya mika masa hannu sukayi musabaha yashigo dashi har falo,bedroom yashiga yadauko hijab din bilkisu yabita kitchen, ya dora mata saman kafadarta, juyowa tayi ta kalleshi yau baya magana saboda azumi na dukanshi,
"Salim ne yazo" abinda ya iya fada kenan yajuya yafita, saida tagama komai sannan aka kira salla, fruit salad ne bata jima da gamawa ba lokacin kayan ta tattaro gaba daya ta kawo musu falo har lokacin gogan akwance yake yakasa tashi shiyasa salim ya kalleta yana dariya bayan sun gaisa yace,
"Hajjaju wannan fa yau sai kinzo kin dagashi dan yakasa tashi"
Dariya tayi takoma kitchen takawo sauran kayan ta ajiye musu sannan ta kalli fahad wanda ke kwance rub da ciki,
"Tashi kasha ruwan mana...."
Hannu yamika mata saboda ganin idon salim bata kiba takama nashi yatashi zaune azuciyarsa yana cewa,
"Wannan badan ansha ruwaba ai sunan azumina karyayye irin wannan laushi haka"
Kunu ta zuba masa ta mika masa sannan tace,
"Karka sha abu mai sanyi yanzu sai an dan jima, kafara shan mai zafi tukunna"
Kai yadaga mata shi dai salim tuni yahada tea dinsa yana sha da kosai, juyawa tayi tawuce daki tabasu wuri tana zuwa tashiga wanka. Su fahad kuwa bayan ciki ya dan dauka fanfon waje sukaje sukayi alwala sannan sukazo sukayi salla bayan sun idar suka dora da ciye ciyensu sai lokacin bakin fahad yabude sunata hira da salim, bilkisu na fitowa sanye da hijab har kasa tanata zuba kamshi fahad ya kalleta ya dage girarshi guda daya cikeda tsokana yace,
"Hajjaju sannu da shan ruwa, ansha ruwa lafiya?"
Ita dashi sun san meyake nufi amma shi salim bai saniba shiyasa shima yayi mata sannu da shan ruwan, iya na salim din kawai ta amsa tawuce kitchen tazubo dankali da kosai tafito,
"Ranki yadade sannu da shan ruwa fa naketa yimiki amma kin shareni laifin me nayi?"
"Yawwa sannu"
Murmushi yayi ya saci kallonta ta zabga masa harara, tana jinsu sai surutu sukeyi kasancewar sun koshi, suna gamawa suka mike zasu fita, kaya fahad yaje yasauya sannan suka fice yana sake tsokanarta,
"Hajjaju yau mun kai daya ko?"
"Goma aka kai" Tafada cikin gatse,
Dariya yayi yaja hannun salim suka fita, itama wurinda suka ci abincin ta zauna ta kintsa sannan ta kwashe kayan takai kitchen tawuce daki,takardar hutunta take son turawa ta mail domin daga gobe ko jibi take son farawa.....
*Dan Allah idan har baki biya kudin littafin nanba karki karanta hakkin wasu domin na siyarwa ne.*
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO*
*KAMAR DA WASA....!*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*23*
***Bai samu yadawo gidanba sai wurin karfe 10 bilkisu duk tsoro ya isheta domin bata taba zama agidan ita kadai da daddare ba,tana daki tarufe da key yashigo kwankwasa mata kofa yayi dakyar ta tashi ta bude dan tsoro tana ganin shine ta harareshi,cikin alamun atsorace take tafurta,
"Ina kaje kakai dare haka?"
"Ranki yadade daga shago nake wallahi, bayan mun fita daga nan salla mukaje mukayi daga can kuma shine naje gida nayiwa su ayiyah barka da shan ruwa shine nawuce shago"
Bashi hanya tayi yawuce ciki tana cewa
"To gaskiya kar ka kara kaiwa haka awaje"
"To ranki yadade"
Falo yasake fitowa yawuce kitchen yazubo abinci yaci sannan yayi shirin bacci, da asuba itace ta tasheshi ya tashi yayi suhur, kallonta yayi tana kwance kan gado tana shirin yin wani baccin bayan yayi brush yafito,
"Nima anya gobe zanyi azumin nan kuwa? To naga wadanda suka fini ma basayi"
Tana jinsa tayi biris dashi daga karshe yafice yaje yayi suhur din saida yayi sallar asubah sannan ya kwanta. Washe gari tafara hutunta kamar yadda ta nema, kullum tare suke shan ruwa da salim ranar da akayi azumi na biyar sukaje gidansu fahad suka yimusu sannu da shan ruwa bayan Bilkisu ta siya musu kayan tea, shi kuwa fahad kayan marmari yasiya musu suka kai musu washe gari kuma suka je gidansu Bilkisu can dinma kayan marmarin fahad yasiya cikin manyan ledoji suka kai ita surukuntar fahad da ammah dariya take bata domin basa sakewa da juna, har karfe 9 nadare suna gidan wurin goma suka dawo gida. Bilkisu sai da tasha azumi bakwai ana takwas ta dauka danma ranar ansamu ni'ima agari dan har ruwa aka sheka shiyasa bata wani jishi ba sosai, bayan ansha ruwa fahad ya fara halin nasa na tsokana, har bedroom yabita yabar salim afalo,
"Hajjaju yau wasu takwas suka kaifa wasu kuma bakwai wasu shida ke kuma first ramadan yau"
Harararshi tayi ta gyara zamanta,
"Kafita daga idona..."
Ficewa yayi daga dakin gaba daya yana dariya, akwana atashi haka azumin yafara tafiya domin har anfara lissafin salla, duk kannenta babu wadda batazo ba ita da mijinta sunyi mata barka da shan ruwa ba, azumi yaraba tsakiya abba ya aiko musu da kaya kaca kaca kayan tea ne, kayan abinci da sauransu ba ita kadaiba harsu mamaa kowa ya aika masa dashi. Tunda salla ta taho fahad yazama busy domin aiki yayi musu yawa dama duk karshen azumi ashago suke kwana su kwana suna aiki amma wannan karon saboda bilkisu yahakura sai dai yataho da kayan gida yayita yankawa da safe idan yafita sai ya dinka, ana saura kwana biyar salla yake tambayarta wai ita bazata yi dinkin salla ba ehh tace masa kawai, har ana igobe salla bai samu kansa ba cefane ma sai yaro yatura yace yaje tafada masa duk abinda take bukata sai yazo yabashi kudin yaje yasiyo yakai mata, zamansa agidan yanzu kalilan ne, dawowarta daga kunshi kenan itada khulsum dan aiken yazo list tayi tabashi na abubuwan da take bukata domin shinkafa ma ita zata dafa ranar sallar ba tuwoba. Fahad bai dawo gidanba sai 11 nadare domin acanma yasha ruwa yau, ido biyu yasamu bilkisu batayi bacciba domin itama duk vegetables din da zata bukata ta zauna ta gyara gamawarta kenan yashigo amutukar gajiye,atamfa yar ubansu ya dinko mata dark pink mai zanen agogo ajiki, karba tayi tana kallon dinkin da yayi mata riga da skirt fitted, daga atamfar har dinkin sunyi mata kyau,
"Thank you..." Tafada cikin nuna alamun jin dadi, bai amsaba ya kalleta,
"Duk wannan kwalliyar ni aka yiwa?"
Yafada cikeda tsokana,
"Kai kasani..."
Dariya yayi yawuce bathroom domin watsa ruwa. Bayan yafito ya dauki shirgin shimfidarsa yafita,
"Ni wai ko tausayina ma ba ayi kullum akoroni falo hmmm"