Sashe 35
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zaro ido bilkisu tayi cikeda tashin hankali sakamakon jin sharrin da wise ke neman kulla mata, shi dai hamood bai sauraresu ba yayi waje da sauri,
"Ke mahaukaciyar inace? Me mijina yayi min da zan hada kai da wasu har in cutar dashi?" Bilkisu tafada tana huci,
"Karyar banza, mijina mijina... Mijinki a ina? Mijin da bai damu dakeba.... Sannan ni kika kira da mahaukaciya ko? To bari innuna miki ni din cikakkiyar mahaukaciya ce...."
Kafin Bilkisu tayi wani yunkuri sai jin abu tayi agoshinta tauuuu take hankalinta ya bar jikinta na wucin gadi, jin duka kawai tayi tako ina, ita ba ma'abociyar fada bace domin rabonta da dambe harta manta,ko lokacin da tana yarinya batayi rayuwar fada ba bare yanzu shiyasa wise tasamu galaba akanta kafin hamood yashigo tayi mata laga laga duk ta kumbura mata fuska ga goshinta dake tsiyayar da jini sakamakon kwada mata flate din silver da tayi awurin, dakyar hamood ya iya banbare Bilkisu daga hannun wise wacce keta faman gwarata abango duk ta yayyaga mata kayan dake jikinta, cikin bedroom dinta ya turata ya rufe sannan yazo ya kama Bilkisu yashigar da ita dakinta dake sama, suna shiga tafashe da wani irin kuka mai cin rai gamida ban tausayi.
****
Sosai jikin fahad yayi kyau kuma ya samu sauki sai dai har gobe akan magani yake kullum sai yasha wasu kwayoyin magani kanana guda uku, yana kwance shi kadai acikin daki domin ya abba yakoma makaranta wayarshi na hannunshi ya tsurawa pic din Bilkisu ido wanda aka yimata ranar bikinsu,
"Wai dagaske Bilkisu kin barni...? Dagaske shikenan narabu dake? Dan Allah Bilkisu kidawo gareni,ki tasheni daga wannan mummunan mafarkin da nakeyi.... Dan Allah ki tasheni kice mafarkine ba gaskiya ba, Bilkisu kice min duk abubuwan da suka faru acikin mafarki ne, wallahi ina sonki.... Ina sonki Bilkisu....."
Salim dake tsaye akansa kawai ido yazuba masa yana kallonsa aransa yana tambayar kansa wannan wacce irin jarrabawa ce abokinsa ke fama da ita? Wai har yanzu yakasa daina son Bilkisu, ohh Allah....,
Fauce wayar dake hannun fahad yayi sai lokacin fahad din yayi firgigit alamun dawowa daga duniyar tunani, kan screen din wayar salim ya kalla hoton Bilkisu ne rangadadau gashi nan tasha mutukar kyau girgiza kai salim yayi yazauna kusa da fahad wanda ke goge hawayen idonshi cikin dabara gudun kada salim din yagani sai dai kashh ya makaro domin salim din yajima da ganin hawayen da yake zubarwa tun lokacin da yashigo cikin dakin,
"Kasan Allah? Zaka kashe kanka abanza akan wata aba banza wai ita soyayya.... Ya zaka zauna kayita kukan zuci da na fili akan so? Wallahi idan baka daina wannan tunanin ba kadai ji abinda Dr yafada maka ko jiya da na rakaka yace idan har baka bar damuwa da tunane tunane ba wannan hawan jinin naka zai janyo maka ciwon zuciya...."
Sake goge hawayen yayi da bayan hannunshi yakawar da kanshi gefe batare da ya kalli salim ba ya runtse idanuwansa,
"Salim wallahi nayi kokarin yin hakan amma nagaza, nakasa cireta araina, nakasa daina tunaninta, nakasa daina ganinta acikin mafarkina, nakasa salim, nakasa, nakasa daina sonta..... Meyasa Bilkisu zatayi min haka?"
"Kai ai banza ne wallahi, anfada maka haka ake so? Anfada maka haka ake soyayya kamar za amutu idan aka rabu? Wallahi ka maida hankalinka, matar da tajima da mantawa ma dakai shine zaka zauna kana westing din time dinka abanza kana tunaninta..."
Tashi zaune fahad yayi yana fuskantar salim,
"Malam karka sake ka zage ni ko ka zagar min mata..."
Dariya salim yayi wacce tasake kular da fahad,
"Lallai kuwa, kasan wani abu? Ai dai pics dinta kake zama kullum kasaka agaba kana kallo ko? To insha Allah daga yau zaka daina, kai wai mekakeson jawowa kanka ne? Ciwon zuciya ko tabin hankali? Anya wannan bilkisun ba asiri tayi maka ba kuwa? Wallahi karaba kanka da soyayya..."
Daga haka yamike zai fita daga dakin,
"Dallah malam ban wayata..."
Juyawa salim yayi ya kalleshi,
"An hanaka, ai wallahi ko zan baka wayar nan sai nagoge hotunan Bilkisu gaba daya...."
Tun kafin yakarasa fahad yadaka tsalle yabishi amma ina bai iya cimmasa ba domin aguje yabar gidan har kofar gida fahad yabishi ganin bazai iya kamashi ba yasa ya hakura yatsaya yarike waist yana haki gashi baya son fita cikin unguwa ahaka domin daga shi sai gajeren wando da t shirt, cikin gida yakoma yashiga daki yayi wanka yashirya sai faman fushi yake, aransa yana cewa idan har salim yagoge masa hotunan Bilkisu to zasu samu babbar matsala, yana shiryawa yana tunani, adaki yayi sallar la'asar sannan yashiga cikin gida wurinsu ayiyah, mariya na shirin tafiya islamiyya yayinda maryam tuni har ta dade acan, dundu ya zuba mata yana fadin,
"Uwar nauyi kullum kece karshen tafiya makaranta kiga maryam tajima da tafiya amma ke sai kinyi makarar da kika saba..."
"Ya fahad Allah hadda na tsaya yi idan naje ban iyaba dukana za ayi.."
"Wai zaki wuce kitafi ko sai nayi ball dake..."
Dasauri tawuce tabar gidan bayan tasaka takalminta, falon mamuh ya leka tana kwance tana jin shirin wasan kwaikwayo mai suna madubi hoton kowa wanda ake gabatarwa atashar freedom radio,
"Mamuh dan Allah me zan samu? Allah yunwa nakeji"
Dagowa tayi ta kalleshi,
"Au ai nazaci baka janye yajin aikin cin abincin da kakeyi ba, shiyasa yau ban raba dakai ba tunda naga ko anbaka baci kakeyi ba..."
Dariya yayi yasaki labulen bayan yakarasa shiga cikin dakin,
"Nidai dan Allah abani wani abu inci kar kuma ulcer ta kamani"
Mikewa zaune tayi tana rage karar sautin radion ta,
"Ai dole abaka abinci dan auta, gaka kuma shagwababbe.... Ohh su fahad ankasa daina baci..."
Shidai yana jinta baice komai ba har ta miko masa kwanon abincin, dan waken fulawa ne subil subil dashi kanana kanana nan tamiko masa robar yaji da ta mai da maggi, dama yau ayiyah bata nan tana can kura tatafi biki kuma sai gobe zata dawo,
"Wai mamuh dan Allah meke rage damuwa ne? Menene maganinta?"
Saida tagyara zamanta takashe radion da take sauraro gaba daya sannan ta amsa masa,
"Fahad hakuri da addu'a sune suke jagorancin maganin kowacce damuwa, duk abinda yasamu bawa mutukar zaiyi hakuri kuma zaiyi addu'a to da yardar Allah zakaga ubangiji ya yaye masa damuwarsa... Kowa na duniya da kagani yanada damuwarsa daban wacce ke damunsa sai dai kawai fadane bazai yiba amma idan da ace wani zai fito yafada maka damuwarsa sai kaga kai taka damuwar bata kai kazauna kana damuwa ba... Hakuri da addu'a sune mafita acikin rayuwa"
Rufe kwanon dan waken yayi yana gyada kai alamun gamsuwa, kallonsa tayi tana harararsa,
"Meke nan kayi? Wai kana nufin har kaci?"
Ashagwabe yadaga kai yana bata fuska saboda yasan halin mamuh yanzu sai tace sai yacinye shikuma yanzu kwata kwata baya iya cin abinci sosai domin ba dadinsa yake jiba,
"Wallahi sai ka cinye abincin nan fahad... Shiyasa dama ban bayar ankai maka dakiba dan ba lallai kaciba kokuma kaci kwaya biyar kabaiwa almajirai sauran kazo kayi karyar kaine ka cinye..."
Tamkar zaiyi kuka yanata yamutsa fuska yasake jan kwanon gabansa yana ci, mamuh sai kara yimasa Nasiha take cikin hikima kan muhimmancin hakuri da kuma yarda da kaddara, kamar yadda tace saida ya cinye dan waken nan tass sannan yatashi cikinsa acunkushe dan tsabar koshi, ai fasa hawa babur dinsa yayi sai akasa yafita, shagonsu yaje fuskarsa babu yabo babu fallasa dama yanzu haka yakoma bai cika walwala ba, yana saman tebur din da suke yanka dinkuna tj yana yanka wani swiss material shikuma fahad yana guiding dinshi yanda yadace yayi yankan salim yazo, sallamarsa kadai fahad ya amsa daga nan yadauke kai dariya salim yayi yadafa kafadarsa,
"Abokina ga wayarka..."
"Ai da ka rike gaba daya kaga saika kasheni da hujja..."
Dariya maganar tabawa salim ya kalleshi,
"Ga dai mai neman kasheka can shiyasa nagoge hotunanta dan nafuskanci wallahi sonta na iya zama ajalinka idan har kayi wasa..."
"To idan tazama ajalin nawa sai me? Ina ruwanka?"
"Da ruwana mana tunda mu zata jawa asara kullum baka da aiki sai dai kasa hotonta agaba kullum kayita kallo kana hawaye... Allah prince kashiga hankalinka karage son nan da kake yimata saboda ina tsoron kar ciwon nan naka yasake tsananta..."
Banza fahad yayi dashi yawarci wayarsa yasoma duba folder din da hotunan Bilkisu suke amma duk empty wato salim dagaske yake yagoge din kenan? Goshi yadafe yana jin bacin ransa yana karuwa, duk maganganun da salim keyi masa baya tankawa dan yadau fushi sosai dashi daga karshe ma bar masa wurin yayi yasauka kasa yashiga masallaci yayi kwanciyarsa sai da lokacin salla yayi sannan yafita yayi alwala, bayan an idar da salla yafito salim na bayansa yamika masa hannu suyi musabaha amma yaki, shi salim ma dariya fahad kebashi wallahi, sanin idan yaje gida tunanine zai addabi ruhinsa yasashi tunanin inda yadace yaje kamar yaje wurin husnah sai kuma yatuna ashe sufa yan school of nursing 6 nayi ake rufe musu gate bashiga ba fita, majalissin marigayi sheikh ja'afar yaje inda wasu dalibansa guda biyu ke gabatar da darasi kowacce rana daga bayan sallar magrib zuwa lokacin sallar ishah sosai hakan yadebe masa kewa bayan an idar da salla yatashi zuciyarsa wasai sai dan abinda ba arasa ba, salim sai kiran wayarsa yakeyi amma yaki dagawa daga karshe kuma kiran husnah yashigo itama bai dauka ba har saida kiran yakatse sannan ya kirata, a dakalin dake kofar gidansu yazauna sunata waya da husnah basu taba doguwar waya irin ta yauba har wurin karfe 9,baya son shiga gida yanzu domin yasan muddin sukayi ido hudu da mamuh sai tasashi yaci tuwon dare shikuma akoshe cikinsa yake, yana kokarin tashi yaya Auwal yafito daga cikin gidan wato babban yayansu mijin anty fauziyya,
"Lahh.... Yaya yaushe kashigo gari?"
"Ba tun dazu naketa jiranka agida baka shigo ba... Wai yanzu me kake shiryawa ne?"
"Yaya karatu fa zan koma"
"A ina?"
"Wai da maryam abacha nakeson tafiya ko Ogun state ance akwai wata private university acan..."
"Kai dalla rufewa mutane baki, kaje kayi applying a federal university Kaduna kacike D E saboda karka makara, kaga kusa da gidane kacike duk course din da ranka keso...,sai da safe"
"To shikenan yaya agaida su anty"
"Ke mahaukaciyar inace? Me mijina yayi min da zan hada kai da wasu har in cutar dashi?" Bilkisu tafada tana huci,
"Karyar banza, mijina mijina... Mijinki a ina? Mijin da bai damu dakeba.... Sannan ni kika kira da mahaukaciya ko? To bari innuna miki ni din cikakkiyar mahaukaciya ce...."
Kafin Bilkisu tayi wani yunkuri sai jin abu tayi agoshinta tauuuu take hankalinta ya bar jikinta na wucin gadi, jin duka kawai tayi tako ina, ita ba ma'abociyar fada bace domin rabonta da dambe harta manta,ko lokacin da tana yarinya batayi rayuwar fada ba bare yanzu shiyasa wise tasamu galaba akanta kafin hamood yashigo tayi mata laga laga duk ta kumbura mata fuska ga goshinta dake tsiyayar da jini sakamakon kwada mata flate din silver da tayi awurin, dakyar hamood ya iya banbare Bilkisu daga hannun wise wacce keta faman gwarata abango duk ta yayyaga mata kayan dake jikinta, cikin bedroom dinta ya turata ya rufe sannan yazo ya kama Bilkisu yashigar da ita dakinta dake sama, suna shiga tafashe da wani irin kuka mai cin rai gamida ban tausayi.
****
Sosai jikin fahad yayi kyau kuma ya samu sauki sai dai har gobe akan magani yake kullum sai yasha wasu kwayoyin magani kanana guda uku, yana kwance shi kadai acikin daki domin ya abba yakoma makaranta wayarshi na hannunshi ya tsurawa pic din Bilkisu ido wanda aka yimata ranar bikinsu,
"Wai dagaske Bilkisu kin barni...? Dagaske shikenan narabu dake? Dan Allah Bilkisu kidawo gareni,ki tasheni daga wannan mummunan mafarkin da nakeyi.... Dan Allah ki tasheni kice mafarkine ba gaskiya ba, Bilkisu kice min duk abubuwan da suka faru acikin mafarki ne, wallahi ina sonki.... Ina sonki Bilkisu....."
Salim dake tsaye akansa kawai ido yazuba masa yana kallonsa aransa yana tambayar kansa wannan wacce irin jarrabawa ce abokinsa ke fama da ita? Wai har yanzu yakasa daina son Bilkisu, ohh Allah....,
Fauce wayar dake hannun fahad yayi sai lokacin fahad din yayi firgigit alamun dawowa daga duniyar tunani, kan screen din wayar salim ya kalla hoton Bilkisu ne rangadadau gashi nan tasha mutukar kyau girgiza kai salim yayi yazauna kusa da fahad wanda ke goge hawayen idonshi cikin dabara gudun kada salim din yagani sai dai kashh ya makaro domin salim din yajima da ganin hawayen da yake zubarwa tun lokacin da yashigo cikin dakin,
"Kasan Allah? Zaka kashe kanka abanza akan wata aba banza wai ita soyayya.... Ya zaka zauna kayita kukan zuci da na fili akan so? Wallahi idan baka daina wannan tunanin ba kadai ji abinda Dr yafada maka ko jiya da na rakaka yace idan har baka bar damuwa da tunane tunane ba wannan hawan jinin naka zai janyo maka ciwon zuciya...."
Sake goge hawayen yayi da bayan hannunshi yakawar da kanshi gefe batare da ya kalli salim ba ya runtse idanuwansa,
"Salim wallahi nayi kokarin yin hakan amma nagaza, nakasa cireta araina, nakasa daina tunaninta, nakasa daina ganinta acikin mafarkina, nakasa salim, nakasa, nakasa daina sonta..... Meyasa Bilkisu zatayi min haka?"
"Kai ai banza ne wallahi, anfada maka haka ake so? Anfada maka haka ake soyayya kamar za amutu idan aka rabu? Wallahi ka maida hankalinka, matar da tajima da mantawa ma dakai shine zaka zauna kana westing din time dinka abanza kana tunaninta..."
Tashi zaune fahad yayi yana fuskantar salim,
"Malam karka sake ka zage ni ko ka zagar min mata..."
Dariya salim yayi wacce tasake kular da fahad,
"Lallai kuwa, kasan wani abu? Ai dai pics dinta kake zama kullum kasaka agaba kana kallo ko? To insha Allah daga yau zaka daina, kai wai mekakeson jawowa kanka ne? Ciwon zuciya ko tabin hankali? Anya wannan bilkisun ba asiri tayi maka ba kuwa? Wallahi karaba kanka da soyayya..."
Daga haka yamike zai fita daga dakin,
"Dallah malam ban wayata..."
Juyawa salim yayi ya kalleshi,
"An hanaka, ai wallahi ko zan baka wayar nan sai nagoge hotunan Bilkisu gaba daya...."
Tun kafin yakarasa fahad yadaka tsalle yabishi amma ina bai iya cimmasa ba domin aguje yabar gidan har kofar gida fahad yabishi ganin bazai iya kamashi ba yasa ya hakura yatsaya yarike waist yana haki gashi baya son fita cikin unguwa ahaka domin daga shi sai gajeren wando da t shirt, cikin gida yakoma yashiga daki yayi wanka yashirya sai faman fushi yake, aransa yana cewa idan har salim yagoge masa hotunan Bilkisu to zasu samu babbar matsala, yana shiryawa yana tunani, adaki yayi sallar la'asar sannan yashiga cikin gida wurinsu ayiyah, mariya na shirin tafiya islamiyya yayinda maryam tuni har ta dade acan, dundu ya zuba mata yana fadin,
"Uwar nauyi kullum kece karshen tafiya makaranta kiga maryam tajima da tafiya amma ke sai kinyi makarar da kika saba..."
"Ya fahad Allah hadda na tsaya yi idan naje ban iyaba dukana za ayi.."
"Wai zaki wuce kitafi ko sai nayi ball dake..."
Dasauri tawuce tabar gidan bayan tasaka takalminta, falon mamuh ya leka tana kwance tana jin shirin wasan kwaikwayo mai suna madubi hoton kowa wanda ake gabatarwa atashar freedom radio,
"Mamuh dan Allah me zan samu? Allah yunwa nakeji"
Dagowa tayi ta kalleshi,
"Au ai nazaci baka janye yajin aikin cin abincin da kakeyi ba, shiyasa yau ban raba dakai ba tunda naga ko anbaka baci kakeyi ba..."
Dariya yayi yasaki labulen bayan yakarasa shiga cikin dakin,
"Nidai dan Allah abani wani abu inci kar kuma ulcer ta kamani"
Mikewa zaune tayi tana rage karar sautin radion ta,
"Ai dole abaka abinci dan auta, gaka kuma shagwababbe.... Ohh su fahad ankasa daina baci..."
Shidai yana jinta baice komai ba har ta miko masa kwanon abincin, dan waken fulawa ne subil subil dashi kanana kanana nan tamiko masa robar yaji da ta mai da maggi, dama yau ayiyah bata nan tana can kura tatafi biki kuma sai gobe zata dawo,
"Wai mamuh dan Allah meke rage damuwa ne? Menene maganinta?"
Saida tagyara zamanta takashe radion da take sauraro gaba daya sannan ta amsa masa,
"Fahad hakuri da addu'a sune suke jagorancin maganin kowacce damuwa, duk abinda yasamu bawa mutukar zaiyi hakuri kuma zaiyi addu'a to da yardar Allah zakaga ubangiji ya yaye masa damuwarsa... Kowa na duniya da kagani yanada damuwarsa daban wacce ke damunsa sai dai kawai fadane bazai yiba amma idan da ace wani zai fito yafada maka damuwarsa sai kaga kai taka damuwar bata kai kazauna kana damuwa ba... Hakuri da addu'a sune mafita acikin rayuwa"
Rufe kwanon dan waken yayi yana gyada kai alamun gamsuwa, kallonsa tayi tana harararsa,
"Meke nan kayi? Wai kana nufin har kaci?"
Ashagwabe yadaga kai yana bata fuska saboda yasan halin mamuh yanzu sai tace sai yacinye shikuma yanzu kwata kwata baya iya cin abinci sosai domin ba dadinsa yake jiba,
"Wallahi sai ka cinye abincin nan fahad... Shiyasa dama ban bayar ankai maka dakiba dan ba lallai kaciba kokuma kaci kwaya biyar kabaiwa almajirai sauran kazo kayi karyar kaine ka cinye..."
Tamkar zaiyi kuka yanata yamutsa fuska yasake jan kwanon gabansa yana ci, mamuh sai kara yimasa Nasiha take cikin hikima kan muhimmancin hakuri da kuma yarda da kaddara, kamar yadda tace saida ya cinye dan waken nan tass sannan yatashi cikinsa acunkushe dan tsabar koshi, ai fasa hawa babur dinsa yayi sai akasa yafita, shagonsu yaje fuskarsa babu yabo babu fallasa dama yanzu haka yakoma bai cika walwala ba, yana saman tebur din da suke yanka dinkuna tj yana yanka wani swiss material shikuma fahad yana guiding dinshi yanda yadace yayi yankan salim yazo, sallamarsa kadai fahad ya amsa daga nan yadauke kai dariya salim yayi yadafa kafadarsa,
"Abokina ga wayarka..."
"Ai da ka rike gaba daya kaga saika kasheni da hujja..."
Dariya maganar tabawa salim ya kalleshi,
"Ga dai mai neman kasheka can shiyasa nagoge hotunanta dan nafuskanci wallahi sonta na iya zama ajalinka idan har kayi wasa..."
"To idan tazama ajalin nawa sai me? Ina ruwanka?"
"Da ruwana mana tunda mu zata jawa asara kullum baka da aiki sai dai kasa hotonta agaba kullum kayita kallo kana hawaye... Allah prince kashiga hankalinka karage son nan da kake yimata saboda ina tsoron kar ciwon nan naka yasake tsananta..."
Banza fahad yayi dashi yawarci wayarsa yasoma duba folder din da hotunan Bilkisu suke amma duk empty wato salim dagaske yake yagoge din kenan? Goshi yadafe yana jin bacin ransa yana karuwa, duk maganganun da salim keyi masa baya tankawa dan yadau fushi sosai dashi daga karshe ma bar masa wurin yayi yasauka kasa yashiga masallaci yayi kwanciyarsa sai da lokacin salla yayi sannan yafita yayi alwala, bayan an idar da salla yafito salim na bayansa yamika masa hannu suyi musabaha amma yaki, shi salim ma dariya fahad kebashi wallahi, sanin idan yaje gida tunanine zai addabi ruhinsa yasashi tunanin inda yadace yaje kamar yaje wurin husnah sai kuma yatuna ashe sufa yan school of nursing 6 nayi ake rufe musu gate bashiga ba fita, majalissin marigayi sheikh ja'afar yaje inda wasu dalibansa guda biyu ke gabatar da darasi kowacce rana daga bayan sallar magrib zuwa lokacin sallar ishah sosai hakan yadebe masa kewa bayan an idar da salla yatashi zuciyarsa wasai sai dan abinda ba arasa ba, salim sai kiran wayarsa yakeyi amma yaki dagawa daga karshe kuma kiran husnah yashigo itama bai dauka ba har saida kiran yakatse sannan ya kirata, a dakalin dake kofar gidansu yazauna sunata waya da husnah basu taba doguwar waya irin ta yauba har wurin karfe 9,baya son shiga gida yanzu domin yasan muddin sukayi ido hudu da mamuh sai tasashi yaci tuwon dare shikuma akoshe cikinsa yake, yana kokarin tashi yaya Auwal yafito daga cikin gidan wato babban yayansu mijin anty fauziyya,
"Lahh.... Yaya yaushe kashigo gari?"
"Ba tun dazu naketa jiranka agida baka shigo ba... Wai yanzu me kake shiryawa ne?"
"Yaya karatu fa zan koma"
"A ina?"
"Wai da maryam abacha nakeson tafiya ko Ogun state ance akwai wata private university acan..."
"Kai dalla rufewa mutane baki, kaje kayi applying a federal university Kaduna kacike D E saboda karka makara, kaga kusa da gidane kacike duk course din da ranka keso...,sai da safe"
"To shikenan yaya agaida su anty"