Sashe 7
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
K'arfe takwas da rabi aka fara tafiya wurin dinner,amare da angwaye ba karamin kyau suka sha ba haka itama bilkisu ta hade cikin material din da fahad ya dinka mata tayi masifar kyau tasha head golden dama yau babu maganar mayafi daga ita har kawarta khulsum basu samu zama ba domin sune masu tsara komai.
Cikeda doki fahad yasha wankansa cikin blue din tissue sabo fil da hularsa samfurin minister wacce ta saku da asalin dinkin hannu yayi kyau har yagaji, turaren Amirul oad yayi amfani dashi ya gauraya da turaren black xxs nan fa yafito tsaf dashi saurayi kalar birni, bakin takalmi sau ciki yasaka yadauki agogo yafita lokacin karfe takwas daidai na dare, sai da yashiga cikin gida yayiwa su ayiyah sallama mamuh sai tsokanarsa take tana cewa yagaida budurwar tasa, su Mariya kam saida ya cafki Maryam ya zuba mata rankwashi sannan yafita domin sashi sukayi agaba da dariya da kus kus, yayansa Abba yana zaune akofar gida yafito, shi dinma kallonsa yayi cikeda tsokana yace,
"K'anina yau hira aka nufa ne?"
Dariya yayi yawuce yana fadin,
"Wallahi wani biki zanje"
"To adawo lafiya"
Saida ya amsa sannan yawuce, koda ya isa almukarram event center tuni har wurin ya dinke da jama'a sai kawo mutane akeyi a motoci yayinda wasu sukazo a keke napep wasu kuma da kafarsu ma suka shigo cikin wurin, abangaren fahad shima yabi sahun wadanda suka shigo da kafarsu domin tafe yake hannunshi daya cikin aljihun wandonshi dayan kuma yana latsa wayarshi ta hannu, duk wanda ya kalleshi kallo daya baya iya gamsar dashi har sai yakara na biyu.
Yana isa gaban hall din yayi tozali da yanmatan amare sunsha anko kowacce naji da kanta, ido yashiga ciccilawa yana son yaga ta ina zai hango tauraruwar tasa amma bai samu damar ganinta ba har aka gama shigewa cikin hall din nan shima yamaida wayarshi aljihu ya shiga, kusa da wasu samari su uku yaje ya zauna dama mazaunin mutum hudune domin kujerun guda hudune, gefensu kuma wasu matane suma zaune su hudu, bai kai minti biyu da zamaba ya hango bilkisu tana rikeda hannun khulsum da wasu abubuwa a hannunsu wanda bazai iya gane ko menene ba, ji yayi yana dana sanin yimata wannan dinkin domin jikinta babu ko mayafi amma fa tasha kyau har tagaji kayan sunyi mata dadas ajikinta dukkan shape dinta yafito masha Allah, goshinsa yadafe ya sunkuyar da kai sakamakon sara masan da yaji kan nasa yayi, hankalinsa bai kara tashi ba sai da ya hangota kan step taje wurin amaren suna yin kus wadda babu wanda zai fahimci me suke cewa domin wurin sautin kidane yake tashi ahankali cikin wakar Umar m Sharif ta ranar kuke jira....!, yayi nadamar yimata dinkin nan domin gani yake kamar kowa na wurin ita yake kallo, sai da kowa ya nutsu sannan aka fara gudanar da shirye shiryen da aka tsara, taro da addu'a aka fara budewa sannan aka gayyaci babbar yaya wato bilkisu domin tabada tarihin amarya amma guda daya daga ciki, abunku da yar jarida wacce tasaba nan tazo ta zayyano tarihin Hindu daga karshe tajuya tana kallon isma'il angonta,
"Ango amaryarka tana da kiriniya sosai ada musamman wurin zane domin gaba daya bangon dakinsu da jikin wardrobe dinsu zanen tsintsaye ne da ciyayi, muna addu'ar Allah yasa bazata Zane muku bangon dakunanku da zanen tattabaru ba...."
Kowa na wurin saida ya dara nan ta sauka tabada abin maganar aka kira maama itama tabada tarihin auta minah. Duk inda tayi idanun fahad na kanta ji yake kamar yatashi yaje ya kareta mutane su daina kallonta amma babu damar hakan, lokacin da aka fara raba abinci da abin sha hirar matan dake zaune kusa dasu taja hankalinsa,
"Yanzu dai Yahanazu tagama auren yaranta saura maigado kuma babbar banza ko kunya bataji duk takai kannenta daki ita tana zaune agida..."
"Bakiga harda sake gyaran dakiba domin a tabbatar mana da ba ranar aure"
"Ai uwar tata ke daure mata kugu, idan taki fito da miji basai su hadata da duk wanda suka so ba..." Daya matar tafadi cikin takaici, idonshi ne yakai kan bilkisu wacce ke tsaka da hidimarta khulsum ta miko mata wayarta nan ta Karba ta nufi kofar baya, zip din rigarta ta baya ya dan sauka har hannun farar bra din jikinta ta dan leko amma saika lura dakyau zaka gani, cikin azama, kirjinsa yana fat fat yabi bayanta tana tsaye tana waya gadon bayanta duk awaje, cikeda kishi karara yatsaya abayanta ya kareta, jin tsayuwarshi yasata juyowa ta kelleshi bayan ta maida wayar kunnenta......
*_Ummi Shatu_*
© _HASKE WRITERS ASSO._
*KAMAR DA WASA....!*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*8*
*Mai fitarmin da book kiji tsoron Allah haka kuma wadanda ake turowa kuji tsoron Allah kudaina karanta min mutukar ba siya kikayi ba saboda kamar da wasa wannan karon na kudine,idan kina so ki biya ki karanta.*
***Sai da idanuwansu suka sarke da juna sannan tajanye nata ahankali bayan ta juya masa baya, bayan nata yake bi da kallo kasa kasa, jin takun tafiya abayansu alamun wani na zuwa yasashi saurin kai hannu kan zip din yayi sama dashi hakan yayi daidai da karasowar khulsum wurin, saurin matsawa baya yayi yayinda ita kuma Bilkisu tajuyo atsorace amma ganin khulsum tsaye bayanta tana waya yasata sauke ajiyar zuciya domin tagane itace taja zip dinta ko kadan bata kawo cewar fahad ne ba, ita kuwa khulsum bata ma san abinda ke faruwa ba kawai dai ta iskesu tsaye ne, yayinda gogan ke tsaye yayi mata kurr da ido hannayensa sanye duka cikin aljihun wandonsa.
Kusan tsawon mintuna biyar ta dauka tana wayar daga bisani sukayi sallama da hamood dinta takatse wayar tajuyo tana kallon fahad dan tuni khulsum tabar wurin,
Langabe kai yayi yana kallonta tamkar wani yaro,
"Kazo ashe?..."
"Uhm hajjaju nazo tun dazu"
Murmushi tayi tana duba wayar dake hannunta,
"Zaka jira atashi ai ko?"
Girgiza kai yayi har lokacin kansa langabe yake,
"Idan nayi dare sosai zaneni za ayi agida...!"
Ita abinma dariya yabata yanda yake yi mata wani shagwaba sai kace hudah,
"To yanzu ya za ayi?"
"Muje ciki amma nanda 10 minutes zan tafi"
"Ok babu damuwa muje..."
Sai da ya dan rausayar da kai sannan yawuce tabishi abaya, kai idan kaga yanda suka basar sai abin yabaka sha'awah tamkar wasu saurayi da budurwa,duk da hill din dake kafarta akafadarshi tsayinta ya tsaya ahaka suka kai tsakiyar hall din wanda tuni ya kancame kasancewar amaren sun fito suna takawa mc kuwa sai kiran sunan Bilkisu yake yana cewa yana son ganin babbar yaya wato adda bilkisu yayar amare.
Bilkisu ai jaka ta balle tashiga cikin kannen nata tana yimusu ruwan sabbin nairori suma suna yimata, su hudu gwanin sha,awa domin harda maama kamar abin hadin baki kuma sai hudah da mina suka soma kuka harda maama, ita kanta ji tayi kwalla tana taho mata shiri tabar cikin filin ta nufi hanyar fita, daga inda yake zaune yana ganin duk abinda ke faruwa abisa dukkan alamu akwai shakuwa mai girman gaske tsakaninta da kannen nata, tashi yayi yabi bayanta, kamar yadda yazata kafin ya cimmata har ta ida ficewa. Abakin kofar hall din yaganta kan baranda ta jingina da bango,
"Haba hajjaju da girmanki..."
Juyowa tayi suka hada ido idanuwanta har sun danyi ja,murmushin karfin hali tayi,
"Badai har zaka tafiba?"
"Ehh gaskiya wucewa zanyi kar gida su rufe min kofa"
Wannan yaron yanada abin dariya ta ayyana hakan acikin zuciyarta bayan ta sake murmusawa,
"To shikenan nagode, yanzu muje gaban waccan motar inbaka naka hasafin..."
Dan kada idanuwanshi yayi,
"Nidai gaskiya kibarshi, yanzu sai kowa yasan nazo biki? Bana son daukar kaya..."
Murmushi tayi tajuyo sosai tana kallonsa,
"To shikenan Allah ya kiyaye hanya nagode"
"Ba rakiya?"
Wani murmushin tayi har saida hakoranta suka bayyana tasauka tana nuna masa hanya alamar suje, jerawa sukayi har kusa da gate nan tajuya takoma ciki amma me tana zuwa gaban hall din taji yace,
"Saida safe atashi lafiya"
Juyowa tayi cikeda mamakin sake biyota din da yayi amma kafin tayi magana har yajuya yatafi, ciki takoma inda aka cigaba da hidima ba atashi daga wannan dinner ba sai karfe goma sha daya saura ahakanma dan abbansu ya iyo waya yace lallai lallai atashi haka ne nan aka rufe taro da addu'a aka tashi kowa yanufi gida. Fahad kuwa koda yakoma gida raba dare yayi yana sakawa da kuncewa kawai tunanin bilkisu ne ke azalzalar ruhinsa, harga Allah yakamu da mugun sonta to amma bashida tabbacin ko akwai wanda ta tsayar amatsayin mijin aure, yajima yana juyi har dai daga karshe yaji muryar yaya Abba yana cewa,
"Yau meke neman hana dan kanina bacci??"
"SO" yafada acikin zuciyarsa amma azahiri sai yajuya ya kalleshi ta cikin hasken kwan lantarkin da basu kasheba,
"Babu abinda zai hanani bacci kawai dai nagajine..."
"To idan kahuta sai ka kashe mana wutar muyi bacci ko?"
Murmushi fahad yayi bayan yatashi zaune,
"Gaskiya nifa bazan iya bacci aduhu ba harga Allah.."
"To nikuma bazan iya bacci da haskeba, Allah yakawo mu kuma..."
Dariya fahad yayi yana jan pillow dinshi,
"Kuma ahakan kasan har kaguwa nake kazo weekend saboda mu cigaba da fada akan rufe kofar toilet da budewa duk da dai kana hanani bacci..."
Dariya shima yaya Abba yayi yagyara kwanciyarsa yana fuskantar fahad din,
"The same thing da yake faruwa dani kenan duk time din da nakoma school wallahi wani lokacin har dariya drama dinmu kebani abokaina suyita tambayata idan sunga ina dariya ni kadai daga karshe dai nasanar dasu kai natuno kullum sai munyi fada saboda ni bana son haske kai kuma baka son duhu sannan ni bana iya kwana har gari yawaye ban shiga toilet yakai sau uku ba gashi kaikuma k'ara kadance ke tada kai daga bacci gashi kofar k'ara take dashi..."
Dariya fahad yayi yana kokarin kwanciya,
"To ai idan baka nan alla alla nake kadawo kaci gaba da bude kofar"
Cikeda doki fahad yasha wankansa cikin blue din tissue sabo fil da hularsa samfurin minister wacce ta saku da asalin dinkin hannu yayi kyau har yagaji, turaren Amirul oad yayi amfani dashi ya gauraya da turaren black xxs nan fa yafito tsaf dashi saurayi kalar birni, bakin takalmi sau ciki yasaka yadauki agogo yafita lokacin karfe takwas daidai na dare, sai da yashiga cikin gida yayiwa su ayiyah sallama mamuh sai tsokanarsa take tana cewa yagaida budurwar tasa, su Mariya kam saida ya cafki Maryam ya zuba mata rankwashi sannan yafita domin sashi sukayi agaba da dariya da kus kus, yayansa Abba yana zaune akofar gida yafito, shi dinma kallonsa yayi cikeda tsokana yace,
"K'anina yau hira aka nufa ne?"
Dariya yayi yawuce yana fadin,
"Wallahi wani biki zanje"
"To adawo lafiya"
Saida ya amsa sannan yawuce, koda ya isa almukarram event center tuni har wurin ya dinke da jama'a sai kawo mutane akeyi a motoci yayinda wasu sukazo a keke napep wasu kuma da kafarsu ma suka shigo cikin wurin, abangaren fahad shima yabi sahun wadanda suka shigo da kafarsu domin tafe yake hannunshi daya cikin aljihun wandonshi dayan kuma yana latsa wayarshi ta hannu, duk wanda ya kalleshi kallo daya baya iya gamsar dashi har sai yakara na biyu.
Yana isa gaban hall din yayi tozali da yanmatan amare sunsha anko kowacce naji da kanta, ido yashiga ciccilawa yana son yaga ta ina zai hango tauraruwar tasa amma bai samu damar ganinta ba har aka gama shigewa cikin hall din nan shima yamaida wayarshi aljihu ya shiga, kusa da wasu samari su uku yaje ya zauna dama mazaunin mutum hudune domin kujerun guda hudune, gefensu kuma wasu matane suma zaune su hudu, bai kai minti biyu da zamaba ya hango bilkisu tana rikeda hannun khulsum da wasu abubuwa a hannunsu wanda bazai iya gane ko menene ba, ji yayi yana dana sanin yimata wannan dinkin domin jikinta babu ko mayafi amma fa tasha kyau har tagaji kayan sunyi mata dadas ajikinta dukkan shape dinta yafito masha Allah, goshinsa yadafe ya sunkuyar da kai sakamakon sara masan da yaji kan nasa yayi, hankalinsa bai kara tashi ba sai da ya hangota kan step taje wurin amaren suna yin kus wadda babu wanda zai fahimci me suke cewa domin wurin sautin kidane yake tashi ahankali cikin wakar Umar m Sharif ta ranar kuke jira....!, yayi nadamar yimata dinkin nan domin gani yake kamar kowa na wurin ita yake kallo, sai da kowa ya nutsu sannan aka fara gudanar da shirye shiryen da aka tsara, taro da addu'a aka fara budewa sannan aka gayyaci babbar yaya wato bilkisu domin tabada tarihin amarya amma guda daya daga ciki, abunku da yar jarida wacce tasaba nan tazo ta zayyano tarihin Hindu daga karshe tajuya tana kallon isma'il angonta,
"Ango amaryarka tana da kiriniya sosai ada musamman wurin zane domin gaba daya bangon dakinsu da jikin wardrobe dinsu zanen tsintsaye ne da ciyayi, muna addu'ar Allah yasa bazata Zane muku bangon dakunanku da zanen tattabaru ba...."
Kowa na wurin saida ya dara nan ta sauka tabada abin maganar aka kira maama itama tabada tarihin auta minah. Duk inda tayi idanun fahad na kanta ji yake kamar yatashi yaje ya kareta mutane su daina kallonta amma babu damar hakan, lokacin da aka fara raba abinci da abin sha hirar matan dake zaune kusa dasu taja hankalinsa,
"Yanzu dai Yahanazu tagama auren yaranta saura maigado kuma babbar banza ko kunya bataji duk takai kannenta daki ita tana zaune agida..."
"Bakiga harda sake gyaran dakiba domin a tabbatar mana da ba ranar aure"
"Ai uwar tata ke daure mata kugu, idan taki fito da miji basai su hadata da duk wanda suka so ba..." Daya matar tafadi cikin takaici, idonshi ne yakai kan bilkisu wacce ke tsaka da hidimarta khulsum ta miko mata wayarta nan ta Karba ta nufi kofar baya, zip din rigarta ta baya ya dan sauka har hannun farar bra din jikinta ta dan leko amma saika lura dakyau zaka gani, cikin azama, kirjinsa yana fat fat yabi bayanta tana tsaye tana waya gadon bayanta duk awaje, cikeda kishi karara yatsaya abayanta ya kareta, jin tsayuwarshi yasata juyowa ta kelleshi bayan ta maida wayar kunnenta......
*_Ummi Shatu_*
© _HASKE WRITERS ASSO._
*KAMAR DA WASA....!*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*8*
*Mai fitarmin da book kiji tsoron Allah haka kuma wadanda ake turowa kuji tsoron Allah kudaina karanta min mutukar ba siya kikayi ba saboda kamar da wasa wannan karon na kudine,idan kina so ki biya ki karanta.*
***Sai da idanuwansu suka sarke da juna sannan tajanye nata ahankali bayan ta juya masa baya, bayan nata yake bi da kallo kasa kasa, jin takun tafiya abayansu alamun wani na zuwa yasashi saurin kai hannu kan zip din yayi sama dashi hakan yayi daidai da karasowar khulsum wurin, saurin matsawa baya yayi yayinda ita kuma Bilkisu tajuyo atsorace amma ganin khulsum tsaye bayanta tana waya yasata sauke ajiyar zuciya domin tagane itace taja zip dinta ko kadan bata kawo cewar fahad ne ba, ita kuwa khulsum bata ma san abinda ke faruwa ba kawai dai ta iskesu tsaye ne, yayinda gogan ke tsaye yayi mata kurr da ido hannayensa sanye duka cikin aljihun wandonsa.
Kusan tsawon mintuna biyar ta dauka tana wayar daga bisani sukayi sallama da hamood dinta takatse wayar tajuyo tana kallon fahad dan tuni khulsum tabar wurin,
Langabe kai yayi yana kallonta tamkar wani yaro,
"Kazo ashe?..."
"Uhm hajjaju nazo tun dazu"
Murmushi tayi tana duba wayar dake hannunta,
"Zaka jira atashi ai ko?"
Girgiza kai yayi har lokacin kansa langabe yake,
"Idan nayi dare sosai zaneni za ayi agida...!"
Ita abinma dariya yabata yanda yake yi mata wani shagwaba sai kace hudah,
"To yanzu ya za ayi?"
"Muje ciki amma nanda 10 minutes zan tafi"
"Ok babu damuwa muje..."
Sai da ya dan rausayar da kai sannan yawuce tabishi abaya, kai idan kaga yanda suka basar sai abin yabaka sha'awah tamkar wasu saurayi da budurwa,duk da hill din dake kafarta akafadarshi tsayinta ya tsaya ahaka suka kai tsakiyar hall din wanda tuni ya kancame kasancewar amaren sun fito suna takawa mc kuwa sai kiran sunan Bilkisu yake yana cewa yana son ganin babbar yaya wato adda bilkisu yayar amare.
Bilkisu ai jaka ta balle tashiga cikin kannen nata tana yimusu ruwan sabbin nairori suma suna yimata, su hudu gwanin sha,awa domin harda maama kamar abin hadin baki kuma sai hudah da mina suka soma kuka harda maama, ita kanta ji tayi kwalla tana taho mata shiri tabar cikin filin ta nufi hanyar fita, daga inda yake zaune yana ganin duk abinda ke faruwa abisa dukkan alamu akwai shakuwa mai girman gaske tsakaninta da kannen nata, tashi yayi yabi bayanta, kamar yadda yazata kafin ya cimmata har ta ida ficewa. Abakin kofar hall din yaganta kan baranda ta jingina da bango,
"Haba hajjaju da girmanki..."
Juyowa tayi suka hada ido idanuwanta har sun danyi ja,murmushin karfin hali tayi,
"Badai har zaka tafiba?"
"Ehh gaskiya wucewa zanyi kar gida su rufe min kofa"
Wannan yaron yanada abin dariya ta ayyana hakan acikin zuciyarta bayan ta sake murmusawa,
"To shikenan nagode, yanzu muje gaban waccan motar inbaka naka hasafin..."
Dan kada idanuwanshi yayi,
"Nidai gaskiya kibarshi, yanzu sai kowa yasan nazo biki? Bana son daukar kaya..."
Murmushi tayi tajuyo sosai tana kallonsa,
"To shikenan Allah ya kiyaye hanya nagode"
"Ba rakiya?"
Wani murmushin tayi har saida hakoranta suka bayyana tasauka tana nuna masa hanya alamar suje, jerawa sukayi har kusa da gate nan tajuya takoma ciki amma me tana zuwa gaban hall din taji yace,
"Saida safe atashi lafiya"
Juyowa tayi cikeda mamakin sake biyota din da yayi amma kafin tayi magana har yajuya yatafi, ciki takoma inda aka cigaba da hidima ba atashi daga wannan dinner ba sai karfe goma sha daya saura ahakanma dan abbansu ya iyo waya yace lallai lallai atashi haka ne nan aka rufe taro da addu'a aka tashi kowa yanufi gida. Fahad kuwa koda yakoma gida raba dare yayi yana sakawa da kuncewa kawai tunanin bilkisu ne ke azalzalar ruhinsa, harga Allah yakamu da mugun sonta to amma bashida tabbacin ko akwai wanda ta tsayar amatsayin mijin aure, yajima yana juyi har dai daga karshe yaji muryar yaya Abba yana cewa,
"Yau meke neman hana dan kanina bacci??"
"SO" yafada acikin zuciyarsa amma azahiri sai yajuya ya kalleshi ta cikin hasken kwan lantarkin da basu kasheba,
"Babu abinda zai hanani bacci kawai dai nagajine..."
"To idan kahuta sai ka kashe mana wutar muyi bacci ko?"
Murmushi fahad yayi bayan yatashi zaune,
"Gaskiya nifa bazan iya bacci aduhu ba harga Allah.."
"To nikuma bazan iya bacci da haskeba, Allah yakawo mu kuma..."
Dariya fahad yayi yana jan pillow dinshi,
"Kuma ahakan kasan har kaguwa nake kazo weekend saboda mu cigaba da fada akan rufe kofar toilet da budewa duk da dai kana hanani bacci..."
Dariya shima yaya Abba yayi yagyara kwanciyarsa yana fuskantar fahad din,
"The same thing da yake faruwa dani kenan duk time din da nakoma school wallahi wani lokacin har dariya drama dinmu kebani abokaina suyita tambayata idan sunga ina dariya ni kadai daga karshe dai nasanar dasu kai natuno kullum sai munyi fada saboda ni bana son haske kai kuma baka son duhu sannan ni bana iya kwana har gari yawaye ban shiga toilet yakai sau uku ba gashi kaikuma k'ara kadance ke tada kai daga bacci gashi kofar k'ara take dashi..."
Dariya fahad yayi yana kokarin kwanciya,
"To ai idan baka nan alla alla nake kadawo kaci gaba da bude kofar"