← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 67

Sashe 63

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tunda fahad yatafi tafara wata irin kiba ta lokaci daya ada ita yan shafal ce amma yanzu duk tabi tacike tako ina harda dan kumatu tayi acikin satikan da basufi biyu ba ga shining da fatarta keyi da wani lightening na musamman ita harga Allah ta zaci ko man da ta sauyane ya karbeta,su maama dukansu lokacin da suka hadu agida da suka ganta santin canjawar da tayi suka rinka yi hakama khulsum ita dai bata kawo komai ba. Ranar asabar tana gida babu aiki ranar khulsum taje asibitin su mijinta ta dawo tabiyo ta gidan, adaki suka kule suna ta shan chapter husnah kam halin nata data saba tayi taje ta labe musu tana jin hirar da sukeyi ta hamood tsohon mijin Bilkisu har khulsum nacewa taganshi rannan a asibitin su abban Khalifa sai Bilkisu tace may be maganin HIV yaje siya ita dai Allah ne yakareta da tuni ya yaba mata jaraba, ai husnah najin haka ta rufe baki cikeda mamaki, da gudu takoma daki takira anty juwairiyya tana fada mata abinda kunnenta yaji nan fa juwaira tarinka famfa ta tana cewa karta yarda wallahi taje gidansu fahad ta tada maganar dan duk yanda akayi iyayenshi da yayyenshi basu san da maganar ba waya sanima ko itama bilkisun tana da ita karta yarda tabar maganar nan, ai suna gama waya husnah ta shirya tsaf dama lokacin yammace ta sulale tafita tanufi gidansu fahad ita Bilkisu lokacin ma khulsum tatafi tabarta tsaye gaban mirror tana karewa kanta kallo tana so tagano kibar da su khulsum keta cewa wai tayi da kuma haske......

*_Ummi Shatu_*
*Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*

54****Bilkisu bata san meyake faruwa ba sai sha'anin gabanta kawai take tayi tana sake kallon kanta bayan tafito daga wanka, dagaske kam ta dan sake murmurewa ba kamar da ba lokacin da tana tsaka da ramar nan kamar wata majinyaciya amma yanzu kayanta ma duk nema suke suyi mata kadan saboda matsarta sukeyi. Husnah kam lokacin da taje gidansu fahad iya ayiyah da mamuh tasamu kadai suna girkin abincin dare suna dafa tuwon biski miyar karkashi shiru tayi bata fadi abinda yakawota ba har magrib saida baba yadawo sannan tace wurinsa tazo dama karar fahad da Bilkisu takawo, tambayarta baba yayi mesuka yimata nan tafara kora jawabi,

"Baba dama ya fahad ne da matarsa..... Ni gaskiya munafurtata sukayi saboda kwata kwata ban san cewa Bilkisu nada HIV ba sai yau......"

Ai daga mamuh har ayiyah dake zaune awurin dukansu kirji suka dafe cikin razani da tashin hankali sukace,

"HIV...?" Suka fada cikin hadin baki,

"Ehh wallahi mama dama ashe tanada ita shine ta boye bata fada ba...."

"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un..... HIV kuma? To aini koda wasa mahaifinta bai sanar dani hakaba... Sannan shima fahad din baiyi min maganar ba"

"Nima baba bai fada minba dan lokacin bikinmu ma da nace yayi test sai cemin yayi wai yayi shi bashida matsalar genotype da sauran cutukan zamani dake hana aure..."

"To yanzu shi fahad din yasani? Ina nufin yasan matar tasa tanada HIV?"

"Wallahi baba yasani, da saninsa kawai boye muku yayi dan karku hanashi zama da ita, kuma kowa yasan mijinta nada shima yanada HIV din amma ahaka ya fahad yace wai sai ya zauna da ita"

Shiru dukkaninsu sukayi na wucin gadi shi baba ma gaba daya yarasa abinda zaice sai hada zufa yakeyi lallai kuwa idan hakane fahad kuruciya na yawo dashi, waye yafada masa ana irin wannan makauniyar soyayyar akashe kai?

Su mamuh kuwa har yanzu basu daina salati da sallallami ba, kallon husnah baba yayi sannan yace,

"Asma'u abinda nakeso dake kitashi kitafi gidanki kije ki zauna, shikuma zan kirashi zaizo, idan yazo zamu san matakin da zamu dauka"

Sunkuyar dakai tayi cikeda ladabin karya tace,

"To shikenan baba.... Nagode Allah yakara girma"

Sallama tayi dasu mamuh suna cemata ta tsaya tatafi da tuwon biski tace a'a bata iya ciba, cikin jimami tatafi tabarsu kowa yayi shiru suna tunanin mafita.

Bilkisu na falo sanye da doguwar riga yar kanti tana kallo husnah tashigo tawani dauke kanta bata kalli inda bilkisu takeba tawuce daki jimm kadan tafito tashiga kitchen tana cewa,

"Su tsohuwar guzuma dai ankusa abar gidan da aketa tunkaho dashi ana huhhura hanci..... Ashe ana makale da kabari salamu alaikum..."

Ita Bilkisu sam bata gane abinda husnah ke nufi ba shiyasa da taji hayaniyarta na neman damunta tatashi takoma daki ta kwanta taci gaba da kallonta, lokacin kwanciya nayi tai azamar kashe wayarta saboda bata son nacin fahad. Ranar juma'a da yamma saiga fahad yadawo mamaki abin yabawa Bilkisu saboda shi da yayita cewa sai sun nemeshi kafin su ganshi amma shine yakasa hakuri yadawo? Hamdala tarinka yiwa Allah da ba adakinta yake ba yana dakin husnah dan haka suje can su karaci fitinarsu, shi kuma lokacin da yaga Bilkisu mamakin yar kibar da yaga tayi yarinka yi sai taba mata kumatu yake wadanda suka fara luhu luhu gashi ba laifi komai na jikinta ya sake dan bunkasa,wani zumudi yafara yi na son sake kasancewa da ita kawai yana son yasamu dama ne amma ahalin yanzu babu dan ranar husnah ce shiyasa yana fita Bilkisu tatashi tarufe dakinta tayi kwanciyarta. A bangaren husnah kuwa ko da wasa bata nunawa fahad ga abinda wai taje ta shirya ba lafiya lafiya suka kwana amma da safe tun kafin yatashi daga bacci baba yakirashi awaya yace anjima kadan yana son ganinshi shida su bilkisu, tunanin duniya fahad yayishi wai ko zai samu yagano dalilin da yasa baba ke nemansu amma sai yakasa, juyawa yayi yakalli husnah yafada mata cewar ta shirya anjima zasuje gida baba na son ganinsu daga nan yamike yafita, dakin Bilkisu yashiga har lokacin ita bata tashi daga bacci ba tana tunkunkune cikin bargo, zama yayi gefenta yaja kumatunta nan tabude ido ta kalleshi,

"Kitashi ki shirya zamuje gida baba na kiranmu..."

Gabanta taji yafadi,

"Lafiya?"

"Ehh to lafiyar kenan dai...."

"Allah yasa..."

Sake jan kumatunta yayi sannan yatashi yafita, tashi itama tayi tashiga wanka.

K'arfe 8 nasafe suka gama shirunsu tsaf a niyyar fahad yasamo musu napep su tafi gaba daya amma sai husnah tace ita kawai suje a machine din fahad inyaso sai tahau napep, wannan dalilinne yasa tafiyar tasu ta bambanta kafin suje tuni husnah taje tasake tsara karya da gaskiya harda su kukanta wai fahad baya adalci yafi son Bilkisu kuma itace take bashi umarni komai sai abinda tace shi zaiyi yanzu ma adakinta yake amma maimakon yasamo musu napep su taho gaba daya sai yaki yace wai Bilkisu zai dauko ita kuma taje tahau napep, kowa dake zaune wurin abin baiyi masa dadiba nan baba yashiga bata hakuri, tana nan zaune tagama kukan munafurcinta sai gasu fahad, su mariya najin Bilkisu suka fito sukaje da gudu suka rungumeta abin yasake baiwa husnah haushi,duk da tahada karya da gaskiya tafada hakan bai hana su ayiyah yiwa Bilkisu kyakkyawar tarba ba. Saida aka gama gaisawa sannan baba yacewa fahad,

"Fahad meyasa baka adalci tsakanin matanka? Haka ake zaman aure ko mu haka kataso kaga munayi a wannan gidan?"

"Baba menayi?"

"Asma'u maimaita abinda kika zo kika fada mana....."

"Baba tsoronta yakeyi sai abinda tace masa yakeyi, kuma ma ashe tsohon mijinta yanada HIV amma ahaka ya fahad ya aureta shiyasa lokacin bukinmu da nace muje muyi test yaki zuwa yace wai yayi anan...."

Hangame baki fahad yayi cikeda mamaki ita kuwa Bilkisu har tafara halin nata na saurin kuka,

"Bilkisu abinda tafada gaskiya ne wai tsohon mijinki nada HIV"

"Ehh gaskiyane baba..." Bilkisu tafada cikin kuka, kafin baba yayi magana fahad yace,

"Amma baba ai ita bata da ita.... Wallahi kawai tada zaune tsaye ne irin na husnah....."

"Ba tada zaune tsaye bane gaskiyane nidai kawai aje ayi test dan kaima kila kana da ita" husnah tafada tana hararar fahad,

"Ya isa, kai fahad katashi ka debesu gaba daya kuje kuyi test inyaso abinda duk sakamako yanuna ku kawo min...... Ku tashi kuje"

Sam abinda baba yafada bai yiwa husnah dadiba ita so tayi ace suna zuwa iyayen su rufesu da fada sannan suce fahad sai yarabu da ita, Bilkisu kam sai faman hawaye takeyi tana kukan zuci ahaka suka tashi suka fita, kallon bilkisu yayi cikin fada yace,

"Daina yimin kukan nan, kar na kara jinsa...."

Share hawayenta tayi tai shiru husnah na bayansu, juyawa yayi ya kalleta,

"Ke kuma tunda kin zama uwar mutane sai ki kaimu asibitin da yadace...." Tasan gatse yayi mata amma duk da haka sai ta fadawa mai napep asibitin da zai kaisu, lokacin da sukaje asibitin babu mutane dayawa dayake private ne kuma weekend ne, nan aka debi jinin kowa amma bilkisu saida fahad yariketa sannan tabari aka dauki jinin har lokacin kuka takeyi kadan kadan. Sun dan jima suna jiran result sannan aka kawo musu gaba daya suka tafi ko budawa basuyi ba,gidansu fahad suka koma suka kaiwa baba result din shi da kansa yabuda yagani sannan yadago yana kallonsu,

"To kamar yadda sakamako dai ya nuna kowannenku lafiya kalau yake.... Allah yakara rufa asiri, sannan wannan kar yakawo fitina atsakaninku kubarshi amatsayin kawar da zato"

"Baba ni so nake tafada mana a Inda taji ance bilkisu tanada HIV"

"Ai zancen duniya baya buya..." Husnah tafada tana murguda baki,

"A'a fahad, abar maganar nan haka kaji, kar Ku kara tada maganar nan...
Allah yayi muku albarka"
Chapter 63 · 0% Book details