← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 67

Sashe 10

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wata sanyayyar ajiyar zuciya ya ajiye sannan yayi magana cikin taushin murya,

"So nake muyi aure irin wanda kowa yake, sannan bana bukatar ko sisinki kibarni inyi komai kamar yadda kowanne ango keyi..."

"Na amince..." Tabashi amsa,

"Yawwa ko kefa to shikenan insha Allah babu matsala zan fara shiri daga yau dinnan, Allah yawuce mana gaba"

"Amin"

Daga haka sukayi sallama, kowannensu zama yayi yana tunanin abinda zai tunkara, ita dai bilkisu dawowar hamood take hararowa bayan tayi wannan auren na wucin gadi yayinda shikuma fahad anasa bangaren yanda zaije ya tunkari su Ayiyah da maganar aure yake tunani.....

*_Ummi Shatu_*

© _*HASKE WRITERS ASSO.*_

*KAMAR DA WASA...!*

_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*

*11*

*Littafin kamar da wasa na kudine dan Allah idan har kinada bukata to kibiya kudi kisiya sai ki karanta.*

***Da tunanin ta yadda zai jewa su ayiyah da maganar aurenshi yashirya, bakin jeans yasaka da jar t shirt mai dogon hannu kamar koda yaushe saida yasha turarenshi wadanda suka zauna ajikin kayanshi sannan yafito daga dakinnsu yana taje sumar kanshi da karamin cumb wanda keys dinshi ke makale jiki. Tsayawa cak yayi yana tunanin ina yadace yanufa ahalin yanzu,

Waje yayi domin baida bukatar shiga cikin gidan yanzu, zama yayi kan dakali yana cigaba da taje gashinsa daga karshe yasaka cumb din cikin aljihu yazaro wayarsa ya leka instagram daga nan yashiga facebook, sakon husna yagani hakan yasashi jan dan karamin tsaki,

"Wannan yarinyar ko mayya sai haka..."

Chaten yaci gaba dayi har magrib yana zaune awannan wurin yana ganin masu wucewa daga can cikin gida yashiga yayi alwala yafito yawuce masallaci bayan an idar da salla yanufi gidan yaya Asabe babbar yayarsu wadda ke aure acan ladanai, tana tsakar gida itada yaranta guda biyar wasu nayin homework wasu kuma na game a wayarta ita kuma tana marking din test din yara domin malamar makarantace awata private school dake unguwar, ganinsa yasata ajiye abinda takeyi tana yimasa sannu da zuwa yaran kuma nayi masa oyoyo,

Kan babbar tabarmar da suke kai yahau ya zauna yana rikeda humaira wacce itace karama dan ko tafiya bata faraba,

"Autan ayiyah daga ina haka?"

"Anty wallahi yau takanas nazo miki dan wallahi akwai magana"

Dariya tayi takalli 'yarta mai sunan ayiyah yar kimanin shekaru 9 tace,

"Ilham jeki ki kawowa uncle fahad ruwa da lemo mai sanyi kinji sai kizo ki zubo masa abinci idan kin kawo"

Saida taga tashin ilham sannan ta maida hankalinta gareshi,

"Meyake faruwa?"

"Anty aure nasamo amma ban fada agidaba tukunna"

Dariya ita abinma yabata saboda jin abinda yace domin ai fahad yarone, nawama yake da har zaiyi maganar aure yanzu?

"Fahad aure kuma? Wai dagaske kake koda wasa?"

"Dagaske nake Allah"

Kafin takara magana ilham takaraso dauke da aiken da tayi mata nan ta karba ta mika masa gabanshi ta ajiye sannan ta kalleshi,

"Amma fahad aure yanzu anya baka ballowa kanka ruwa ba? Haba fahad inama laifin kakoma karatunka yar degree dinnan da kowa keyi kaima kaje kayi inyaso idan kagama sai kayi maganar Auren amma yanzu dududu nawa kake? Ai ko Abba bana jin zai jajibo aure yanzu bare kai, shiyasa tun jimawa nake cemaka kakoma karatu amma kaki...."

Murmushi yayi bayan ya kwankwadi lemon dake hannunshi,

"Anty inada burin komawa karatu amma gaskiya ba yanzuba..."

"Sai yaushe? Saika Tarawa kanka nauyi yayi maka yawa? Ai tun yanzu yadace kakoma da baka da nauyin kowa amma haka kawai kaki karatu?"

"Anty asabe nidai kawai kiyi min fatan alkhairi"

"To shikenan Allah ya tabbatar da alkhairi, ga abinci nan kaci"

Yajima agidan dan acanma yayi sallar isha'i sannan yatafi gida, akofar gida yaja burki yanemi wuri ya zauna yakira bilkisu,

Fitowarta kenan daga wanka tadauki wayar tana kokarin zama agefen gadonta,

"Ya akayi?" Shine abinda tace lokacin data daga wayar,

"Babu komai, ina wuni?"

Ajiyar zuciya tasauke aranta tana jin tafiyarsu zatazo daidai dashi domin da alama sai yanda tayi dashi,

"Lafiya lau dama nima ina son kiranka, gobe idan Allah yakaimu inaso kazo domin zaka gaisa da ammah sannan zakazo kagaida Abba ma"

"Babu matsala Allah yakaimu amma da kamar yaushe zanzo?"

"Koda yaushe kazo ma babu matsala koda yamma koda daddare"

"Tom zanzo da daddaren dan gaskiya kunyar zuwa da yamma nake"

Murmushi tayi amma bata bari yajiba tace,

"Shikenan Allah yakaimu"

"Amin kiyi bacci cikin aminci da farin ciki,saida safe"

"Allah yakaimu"

Daga haka takashe wayar ta ajiye gefe, koda tagama shirin bacci sai kuma tunani ya addabi ruhinta wato kamar da wasa karamar magana na shirin tabbata dakyar tasamu ta fidda tunanin aranta tayi bacci. Shima fahad da tunanin abin ya kwana aransa shi yanzu babban abinda ke fadar masa da gaba tayadda iyayenshi zasu amince yayi auren nan alhalin ga Abba nan agabanshi wanda shi yadade ma da budurwar amma har yau ba afara maganar aureba. Washe gari bilkisu bataje aikiba domin bata da aiki,tana dakin ammah tana gyarawa bayan tagama wanke toilet taji sallamar maama atsakar gida,

"Yar halak" tafada azuciyarta, babu jimawa sai gasu sun shigo itada huda wadda ke gudu dan tazo wurin bilkisu,

"Sannu Adda, kawo intayaki"

Sakar mata mooper din tayi ta dauki hudah dake rungume da ita,

"Ina kwana Adda labour?"

"Lafiya lau Maman hudah, wallahi yanzu nake tunaninki nake cewa to ko inje gidanki tunda ba fita aiki zanyi ba?"

"Wallahi nima daku na tashi shiyasa muna tashi nacewa abban hudah tare zamu fito idan zaije office yasauke mu"

"Ai kuwa kin kyauta, nasan daga nan har dare kuna nan kamar yadda aka saba"

Dariya maama tayi tace,

"Abinda kema kin sani adda labour"

Kinkimar hudah bilkisu tayi suka koma falo wurin ammah nan maama tafito ta samesu.

Da daddare misalin karfe 8 fahad yayi mata waya cewar yakaraso dama lokacin tana daki tanata faman caba ado kamar gaske, maama dai na kwance tana lallaba hudah tana kallonta, mayafi tadauka tafita tana zuba kamshi dama tun yamma ta fadawa ammah fahad zaizo gaishesu,

Kamar koda yaushe yana tsaye hannunsa daya cikin aljihu yana sanye da farar shadda sabuwa fil tasha bakin aiki wannan dalilinne yasashi sanya bakar hula da bakin takalmi,

"Yaron akwai daukar wanka babu laifi matsalarshi daya yayi yaro dayawa" tafada cikin zuciyarta,

"Barka da fitowa, ina yini?"

Yace da ita yana kallonta,

"Lafiya lau, muje ko?"

Jerawa sukayi zuwa cikin gidan, wurin ammah suka fara zuwa tana zaune afalo lullube cikin mayafi, akunyace yacire sau cikin kafarsa yashiga falon daga shi sai bakar safa akafar tashi, zama yayi kanshi akasa yana gaidata, itama ammahn kanta akasa ta amsa bata ko daga kaiba bare ta kalleshi, hakan da sukai sai yabawa maama da bilkisu dariya nan kowa yayi tasa aboye, duk jinsa yayi yatakura shiyasa ko ruwa yakasa sha daga karshe yamike yafita bayan ya ajiyewa ammah kudi, bin bayansa bilkisu tayi domin takaishi wurin Abba.

Afalon Abba sukaja birki ya kalleta fuskarsa cikeda annuri,

"Ban daiyi rashin kunya ba ai ko?"

"Da kayi me?"

"Dana zo mana"

"Uhmm zancen kakeso"

Murmushi yayi baice komaiba har Abba yashigo daga can wata kofa wadda da alama itace hanyar bedroom dinshi,mikewa tsaye fahad yayi Abba na zuwa ya durkusa kasa da niyyar gaisheshi amma sai Abban ya ruko kafadarshi yana bubbuga bayanshi ahaka suka gaisa, sannan Abba yajashi kan kujera mai zaman mutum uku, abin gwanin burgewa Abba sai janshi yakeyi da hira yana yimasa tambayoyi dangane da tushensu cikin barkwanci da dabara irinta manya daga karshe Abba yace yana son ganin mahaifinsa, duk da yaji dadin ganin Abba da hirar da sukeyi amma yakasa sakin jiki duk atakure yake jinsa dan haka cikeda girmamawa da alkunya yayiwa Abba sallama yafito dama bilkisu tuni ta dade da zamewa tafice, koda yafito tsaye ya sameta tana yin waya da kanwarta mina ganinsa yasata yiwa Mina sallama ta juyo tana kallonsa,

"Ya kukayi?"

"Cewa yayi inturo mahaifina zai gana dashi"

Ajiyar zuciya ta sauke batace komai ba tayi masa alama da hannu suje ta rakashi, shi dinma baice komai ba yawuce tana biye dashi a second gate sukayi kicibus dasu Hindu itada mai gidanta wanda yazo daukarta ganin su bilkisu sun fito yasata komawa domin yiwa Abba sallama dama su take jira sufito. Gaisawa sukayi da mijinta da fahad daga nan suka wuce waje,

"Yanzu menene next abu da kake ganin zamuyi?"

"Bari dai infara yiwa babanmu maganar tukunna inyaso sai sauran su biyo baya..."

Sallama yayi mata yahau roba roba din da yazo dashi na salim yatafi, ciki takoma ta iske Hindu na jiranta nan tafara yimata santin haduwar da fahad yayi tana cewa,

"Su iyallo masu fatan tsiya to zasuga mijinki yawuce tunaninsu"

Ita dai bilkisu dariya tayi daga nan sukayi sallama tashige gida sukuma suka tafi.

Adaren ranar bayan fahad yakoma gida yasamu baba da maganar a turakarshi, dafarko shi kansa kunya abin yabashi shiyasa yarasa ta inda zai fara sanar da baba, kawai sai yaji kunyar yacewa baba aure yakeso yaje ya nema masa dakyar dai yadaure yace,

"Baba dama.....dama akwai wata..... da nake zuwa wurinta..... to yau naje ingaida mahaifinta...... shine.....shine.... yace wai yana son ganinka...."

Shiru baba yayi ya zuba masa ido hakan yasashi kara yin kasa da kansa, mamuh kuwa dake tsaye bakin kofa wacce shigowarta kenan kuma da alama taji komai tafa hannu tafara yi tana rafka salati.....

*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO*
_(Home of expert & perfect writers)_

*KAMAR DA WASA....!*

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

*12*

*Kamar da wasa na siyarwa ne yar uwa idan kinada bukata kisiya saiki karanta.*

***Ji yayi jikinsa yayi mutukar sanyi hakan yasashi yarda aransa cewar iyayen nashi ba lallai su amince da batun nasaba,

"Yanzu kai fahad har kafara maganar aure? Ahh lallai zamani yazo...." Inji mamuh, kasa yasake yi da kansa, dariyar baba yajiyo daga bisani yaji yana fadin,

"Ai ba auren akace za adaura ba kawai dai mahaifin yarinyar ne ke son ganawa dani, menene na saurin karaya kodai baki shirya aurar da d'an nakiba?"

Dariya itama tayi takarasa shigowa cikin dakin ta nemi wuri ta zauna,

"Bahaka bane baban asabe ko gobe akace mu fito muna iya fitowa tunda yarona ba zaman banza yakeba yana da sana'arsa"

"Gashi babarsa tana adashi..." Baba yafada cikin raha,

"Ni yaushe rabona da adashi baban fahad?"
Chapter 10 · 0% Book details