← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 57 OF 67

Sashe 57

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bata cemasa komaiba tayi kwanciyarta tabarshi yana aikin yanka dunkuna, washe gari saida yayiwa husna fada sosai akan koma me tayiwa Bilkisu to kar ta kara aikita irinsa saboda ba mate dinta bace, sannan yace tabata hakuri badan tasoba tabi umarninsa sukaje tabawa Bilkisu hakuri tun daga ranar zamansu yaki dadi saboda husnah gani take kamar fahad yafi son Bilkisu kai kamarma tsoranta yakeyi saboda duk dadin da sukeyi daga Bilkisu tashigo zai daina yauma suna falo suna soyayyarsu yanata goyata amma bilkisu na dawowa daga aiki yadaina da tayi magana sai cewa yayi bata ganin antynta ta dawo ai idan sukayi agabanta gani zatayi kamar sun cimata fuska wannan abu shine yakona mata rai har takasa jurewa saboda ko rikeshi tayi idan Bilkisu na wurin sai ya bata rai ita kuma bayan tadade da fara zargin kamar zamansu akwai wani abu saboda taga duk ranar kwanan Bilkisu da dinkunan da zaiyi yake tafiya dakinta acan zai raba dare yana yankawa amma ita ranar kwananta baya yin abu makamancin wannan. Ita kanta Bilkisu fa kawai tana zaune ne agidan bawai dan tana jin dadin zamanba musamman ma yanzu da taga husnah na neman hanyar da zata rainata tayi mata rashin kunya amma bata shiga shirginta, ranar da fahad zai dawo weekend wato ranar juma'a ranar ne yakama ranar sunan anty Fauziyya yayarsu wacce ta haifi yaronta namiji, su husnah tun safe aka shirya aka tafi sune yan aiki ita kam Bilkisu saida tadawo daga aiki sannan tashirya tatafi dama already tasiyo kayan barkarta. Lokacin da taje su husnah suna dakin mai jego an babbaje itada mutuniyar tata anty juwairiyya wacce ke kara hura mata kai tana zugata tana cewa sai yanzu fahad yayi aure ya auri daidai dashi amma da yawani tashi ya debo yayarsa, ai ko governor yazama itace first lady saboda itace yarinya wacce zasu tsufa tare, zama tayi gefen mai jego wacce keta lale marhabun da ita tare dasu anty asabe da nusaiba matar abba, tana rikeda jaririn anata cika mata gaba da kayan sanyi da abinci,batafi mintuna 20 da zuwaba taji husna na cewa,

"Ni alalen nan ce takasa isata anty juwaira..."

"Amarya ai ke wannan kwadayin mai daliline... Kinada cikakkiyar lafiya"

"Kai anty juwaira nifa ranar girkina ya fahad kwana yake yana yankan dinkuna..."

"Saboda tsabar rashin amfaninki..."

Dukansu da suke cikin dakin dariya sukayi banda Bilkisu wacce tasan da biyu husnah tafadi haka, wato habaici takeyi mata kenan, wai meyasa ita kishiya bata raina abin gori ne? Ta tambayi kanta gaba daya ji tayi gidan sunan ya isheta shiyasa ta yi musu sallama tayi tafiyarta gida, wannan karon bazata fadawa fahad ba amma wallahi takusa nunawa husnah true colour dinta, sai ta nuna mata ita ba sa'arta bace bawai ashekaru kawaiba har awurin mijin ai har gobe tana rikeda tutar soyayyar fahad duk da yayi watsi da ita bawai yana nufin yadaina sonta bane tunda duk lokacin da ranta yabaci agidan nakowa ma sai yabaci. Akule yadawo ya sameta ciki ciki sukayi magana yasake fita, bayan sallar ishah sai gasu tare husnah ya daukota daga gidan sunan dama adakinta yake ranar, bayan kwana biyu yakoma dakin Bilkisu dama akule take dashi saboda gorin da husnah tayi mata na wai kwana yake yi yana yankan dinki adakinta saboda batada amfani, ganin yashigo da atamfa a hannunshi yasata tashi zaune fuskarta adaure,

"Malam yaufa baza kayi min wannan yankan adakina ba... Idan yankan zakayi katafi falo Allah yabamu alkhairi"

Kallonta yayi da mamaki,

"Atamfa guda dayace fa..."

"Ita dinfa, wallahi bazaka yankata adakin nanba, sai dai kakoma can inda kafito kaje kayanka, ko acan din haka kakeyi? Wato saini da aka rainawa wayo ko? To wallahi bazai yuyuba..."

Shi gaba daya yanzu yakasa gane kan Bilkisu kullum awuya take jira kawai take ya tabata suyi rikici duk ta tada masa da hankali shikuma baya son tanka mata saboda husnah yasan tana iya ji ai kuwa kamar yasani dan husnah na labe tana saurarensu,

"Allah yabaki hakuri bari na ajiye"

"A ina? Wallahi kaji narantse atamfar nan bazata kwana cikin dakin nanba mayarta can inda ka dauko...."

Juyawa yayi yafita, husnah najin alamun fitowarshi taruga zuwa dakinta ta kwanta, yana shiga ya jefa atamfar kan akwatunanta yajuya yafita. Zaman dai duk babu dadi gaba daya Bilkisu tasake ramewa duk ta kare atsaye ita wallahi da ace abbanta zai yarda haya zata kama tabar wannan gidan amma tasan ko tafada su Ammah bazasu yarda ba ga yanzu wani sabon iskanci da husnah ta tsira duk ranar girkinta sai ta rinka boye fahad ko Bilkisu nason ganinshi indai yana bacci bazata tasoshi ba sai tace wai dan tsabar rashin tausayi baza abar mutum yahuta ba yaje shago yadawo, shiyasa duk abun yafita ran Bilkisu ko zaman falo bata cika yiba dama kallo ke zaunar da ita da taga abin da rainin hankali sai tasa aka siyo mata babbar plasma sabuwa da receiver da komai aka kafa mata acikin bedroom dinta bayan ta falonta amma fa kallo daya zaka yimata kagane takasa da akiba. Sauki daya yanzu suka samu dukansu basa zama agida saboda husnah takoma makaranta ammafa kusan kullum sai sunzo da kawayenta su Fa'iza suna yadarwa Bilkisu magana sai dai bata fiya jinsuba saboda idan acikin bedroom take zaka isketa ta kunna tv shiyasa bata fiya jiyo hayaniyar da take gudana afalo ba kuma abinda ta lura duk ranar da fahad ke gari husnah bata wannan iskancin bata kawo kowa amma idan baya nan to kullum tare da friends dinta suke zuwa har magrib suna tare, yau ita Bilkisu tana gida bata fita aikiba saboda ciwon mara take yi kamar me kusan tun lokacin da ta fara period bata taba ciwon Mara mai azabar wannan ba shiyasa ko fita batayi ba, saida taji ya lafa mata sannan ta shiga kitchen zata dafa ruwan zafi tana sanye da doguwar riga marar nauyi da hula baka, tana kitchen su husnah suka shigo su uku tana ji husnah na cemusu wai su shiga kitchen su dafa musu abinda suke so, ganin Bilkisu na ciki sai suka fara rashin mutuncin nasu,

"Kawata ya babynmu? Meyake so ne?" Inji fa'iza,

"Ai wai dama kawarmu har mun samu karuwa?" Inji Ruky,

"Tun wanne zamani? Ai ni ba juya bace wallahi kuma sannan matar so ce shiyasa cikin kankanin lokaci aka dirka min ciki, yanzu inajin yayi 2 months da yan kwanaki...."

"Ai wasu ba juya bane kawai duniyancine ke hanasu haihuwa..." Ruky tafada tana dariya, Bilkisu na jinsu tana kokarin juye ruwan zafinta,

"Ehh mana ai dama wasu ba wucema shekarun haihuwar sukayiba kawai tsabar iskancin da suka shuka ne awaje suka yita shan pills suna abortion da haka suka kashe mahaifar...." Husnah tafada tana dariya harda shewa, kashe gas dinta tayi ta dauki tea flask dinta tafita, aganinta rashin class da rashin tunanine zai sata tanka musu saboda yaran da basufi meenah ba karamar kanwarta akanme zata tsaya tayi kace nace dasu? Tana shiga daki tazauna tarasa abinda keyi mata dadi kawai sai tafara kuka kukanne yasaukar mata da zazzabi mai zafi dama gashi bata jin dadin jikinta agaskiya tagaji da wannan rainin wayon dan haka barin gidan fahad zatayi inyaso yazauna da husnan, text ta tura masa cewar ita gida zata tafi, tunda yaga text dinta yasan ba lafiyaba duk da shima din tsakaninsu akwai rashin jituwa amma ai lafiya suka rabu yasan may be itada husnah ne, tun kafin tafada masa abinda yafaru yaji ransa yabaci, aranar yabaro kaduna yadawo gida bayan sallar magrib sai gashi, kowacce na dakinta,dakin Bilkisu yashiga ya sameta zaune tsaf cikin shirinta dama shi take jira tasan yana hanyar zuwa,idanuwanta kadai yakalla yasan tasha kuka,

"Bilkisu meya faru?"

"Kasan me? Nagaji da zama da matarka, kawai ni ka sawwake min inbar mata gidan, ni sa'arta ce da zata rinka kawo kawayenta suna haduwa su zageni? Ni nataba yimata haka? Yarinyar nan yau harda suce waini juyace,kuma wai....." Wani kukan tasake fashewa dashi cikin sauri yazauna kusa da ita ya kwantar da ita kan kirjinsa akaro nafarko,

"Am sorry.... Stop shading your tears... Fada min abinda yafaru wai me?"

Kasa magana tayi sai sautin kukanta dake tashi cikin dakin har lokacin tana rungume ajikinsa yana shafar gadon bayanta, saida yabatar tagama kukan ta dan tsagaita sannan yayi magana,

"Me tace miki bayan haka?"

"Cewa fa sukayi wai saida nagama yawon iskancina nasha pills da abortion sannan na aureka shiyasa wai har yanzu ban haihuba..."

Ji yayi ranshi yabaci sosai kwata kwata bai taba zaton husnah zatayi masa hakaba, sakinta taji yayi ahankali sannan yamike yafita......

Yau banyi editing ba kuyi hakuri da spelling mistakes

*_Ummi Shatu_*

*Littafina na kudine me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*

51***Amutukar fusace yashiga dakin husnah, ransa idan yayi dubu to ya baci yau, tana kwance rub da ciki da waya a hannunta tana rubuta assignment, figota yayi ya finciko ta, atsorace tabishi yana rike da ita yana janta har dakin Bilkisu wacce ke zaune har lokacin bata daina kukaba, jin tahowarsu tareda husnah yasata saurin hadiye kukanta ta goge fuskarta, banko kofar fahad yayi yatura husnah yana huci,

"Husnah.... Maimaita abinda kuka fada mata keda kawayenki...."

Zaro ido husnah tayi kafin ta dora hannu aka,

"Nashiga uku ni asma'u...
Anty me mukace miki? Nida wa? Ni yau ma da babu inda naje shine zakiyi min karya ki hada min sharri....." Tun kafin ta rufe bakinta taji wani wawan mari wanda ko tantama batayi fahad ne ya dauketa dashi dan ransa yakai makura wurin baci gaba daya idanuwansa sun juye daga farare zuwa jajaye,

"Waye yake yimiki karyar? Sa'arkice ita? Kifada min abinda yafaru ko inyi ball dake....."

"Ni wallahi karya take yimin... Karya ne.... Bance mata komai ba amma dan tsabar munafurci shine zata hadani dakai saboda tana bakin cikin muna zama lafiya... Wallahi karya tak...."

"Idan kika kara cewa karya take yimiki wallahi sai na fasa miki baki... Dama bakida mutunci ban saniba? Matar tawa zaki saka agaba kirinka zagi? Sa'arki ce? Ni kin taba ganin na zageta? Zaki fada min abinda yafaru ko sai nayi wasan kura dake?...... Ki fada min inda kika ganta tana zubar da ciki ko tana shan pills kamar yadda kuka ce....."
Chapter 57 · 0% Book details