Sashe 6
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bata jira abinda meenan zata ceba takatse wayar ta cilla cikin jaka sai lokacin fahad ya dauke idonshi daga kanta,
"Am muga dinkunan...."
Fito dasu yashiga yi daya bayan daya, nan bilkisu tasoma santinsu tana yabawa dasu domin ba karamin tsaruwa sukayi ba koda tazo kan nata ai sai ta raina nasu mamaa domin har na amaren bafin nata kyau yayiba gashi dinkin yafitar da shape mai kyau,
"Kai amma fa dinkin sunyi kyau gaskiya nasamu tailor insha Allah daga yanzu kai zan rinka baiwa dinkuna na"
"To hajiya Allah yakawoki"
Daga haka yadauko babbar leda yafara ninke kayan yana zubawa aciki tana tayishi sai yabon dinkin take, daf da zasu gama zuba dinkin cikin leda ya dubeta ta kasan ido,
"Hajiya ba zaki gayyaceni bikin ba kuma?"
Murmushi bilkisu tayi,
"To ai sai dai ingayyaceka daurin aure"
"Ai ban san angwayenba"
"To zan gayyaceka dinner"
Sai da ya dan bude idanuwanshi sosai sannan ya marairaice murya,
"To ai idan nazo baza abarni inshiga ba tunda babu wanda yasanni"
Murmushi ta kumayi ta mika hannu zata dauki ledar kayan amma sai ya hanata yaci gaba da rikewa,
"Karka damu kowa zai shiga tunda bamu raba gate pass ba"
"To shikenan zanzo insha Allah hajiya.... Kodan inga yanda kayan nan zasuyi miki domin zanso ingansu ajikinki"
Ya karashe maganar ciki ciki ta yadda bazata jiba, ai kuwa bata ji dinba tadai ji abinda yafada dafarko amma daga karshe bata jiba, tana kokarin daukar kayan ya hanata ya daukar mata yana fadin,
"A'a hajiya bari na rakaki dashi"
"Ok nagode amma ina son shiga kasuwa ne akwai abinda zan siya"
"Karki damu babu komai muje"
"To nagode"
Handbag dinta ta dauka suka fito yana biye da ita, suna fitowa hamza na zuwa dan haka fahad bai rufe shagonba yawuce yabi bayanta, har cikin kasuwar ya rakata ta kammala siyan kayan kamshin sannan suka fito bakin titi inda zata hau napep, shine yatsaya domin tare mata amma duk wanda yatare sai yaga da namiji aciki sai yace suje da haka har yatare kusan guda uku ana hudunne yaga namiji daya mace daya, cemata yayi ta zagaya ta saitin macen saita zauna, hakan kuwa tayi ya kinkimi kayanta ya mika mata tana yimasa godiya, baice mata komaiba sai murmushin da yake aika mata dashi can akasan ranshi kuma yana cewa,
"Zanyi missing dinki"
Yana tsaye har saida yaga sun kule sannan yakoma shago, yana shiga da kamshinta yasoma yin arangama nan ya lumshe idanuwanshi aranshi yafurta,
"Kamshinki yafi na kowacce mace"
Zama kawai yayi saman benci yakasa cigaba da aikin da yafara, sai hamza yake tayawa hira wanda ke kan kekenshi yana dinka wani leshi, ahaka yar nacin nasa husna tazo ta sameshi, shifa yarinyar nan har mamaki take bashi kamar ba daliba ba yawonta yayi yawa yakan kasa gane lokacin da take shiga class, yana mata dinkin yana daddaure fuska ita kuwa ko ajikinta dan sai zuba take kamar kanyar da bata da zaki.
***
Haka al'amura suka cigaba da tafiya, abangaren su bilkisu dai kowa kagani acikin hidima yake domin biki yazo gaba daya gidansu angyarashi ansake masa sabon fenti sannan kayan falon amma suma ansakesu tun daga kan kujeru har tv da labulaye da sauransu, ada carpert ne malale afalon amma yanzu tiles akasa mai tsada sai katuwar plasma tv da aka manna abango ga kujeru kirar royal chairs nan falon ammi ya dawo tamkar na yarinya duk da tanata rokon Abba akan yabar gyaran haka yaji da kayan dakin yara domin aurar da yanmata biyu lokaci daya ba wasa ba amma yace itama so yake yadawo da ita amarya ai kuwa hakance tafaru domin gidan ba karamin kyau yayiba dan hatta dakin bilkisu Abba yagyare mata shi ansake mata labulaye sabbi sannan ansaka mata tv yar madaidaiciya abangon dake kallon gadonta sannan gefe ga dan fridge dinta ga uban fenti da dakin yasha nan daki yafito yayi fes dashi. Ana saura kwana biyu biki dakyar bilkisu tasamu ta tafi saloon da kunshi itada kawarta khulsum ba ita tadawo gidaba sai karfe biyar saura tana shiga dakinta tajiyo sallamar mutanen garko wato su iyallo, kasancewar daga ita sai daurin kirji yasa bata fitoba domin tana jiyo maganar ya mudan da alama shine yakawo su. Kai tsaye iyallo dakin bilkisu tashiga lokacin ita kuma tana toilet, ganin irin gyaran da dakin yasha yasata rike haba tana tafa hannaye tana zuba salati,
"Ah lallai wannan shine zama daram wato babu ma ranar tashi, irin wannan daki haka kamar agidan miji? Tab... To Allah yasawwaka, iye... Lallai.... Duniya sabuwa"
Juyawa tayi tabar dakin tafita ta nufi cikin gidan wato falon amma wadda ke can tana gaggaisawa da baki domin iyallo ba ita kadai tazo ba su wurin takwas sukazo ciki harda yayarta inna maigado takwarar bilkisu da kuma yayanta guda biyu wato kannen Abba gwaggo uwa da yafendo sai "yayansu,nan tazauna tana tabe taben baki da harare harare, sama sama ta amsa gaisuwar amma nan da nan aka cikasu da ruwa, lemo da abinci tunda dama ansan da zuwansu, shi dai ya mudan bai wani jimaba yakoma yabarsu anan. Bilkisu sarai taji abinda iyallo take fada lokacin da tashigo dakinta, tana wanka tana zancen zuci,
"Su iyallo trouble maker ansauka, haka kuma za ayita fama har sai ranar da kika bar gidan nan, Allah yarabamu lafiya"
Da zancen zuci tagama wankan tafito, ta shirya agaggauce tana saka kaya su Hindu na shigowa shiyasa koda tafito tare suka rankaya falon amma........
*_Ummi Shatu_*
© _*HASKE WRITERS ASSO.*_
*KAMAR DA WASA....!*
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*7*
***Su maama sai yaba kunshin nata sukeyi yayinda ita kuma take yaba kwarewar mai gyaran jikinsu domin kwana uku kacal da fara yimusu har ta sauya musu kamanni, Hindu da maama sarakan rashin kunya ganin takalmansu iyallo tuni suka tura dan kwali gaban goshi duk da hararar da bilkisu keyi musu haka suka dauke kai, itace tafara shiga cikin falon uwar harara iyallo ta tarbeta da ita tana tabe baki sabanin inna mai gado da ta washe hakora tana yimata lale tamkar zata goya bilkisu dan murna da tsantsar kaunar da take yimata, suna tsaka da gaisawa su maama suka shigo, maganar iyallo ita ta katse kowa daga gaishe gaishen da akeyi,
"Ke samodara daga ina kika tafi kika bar yar labibiyar yarinya dan tsabar rashin hankali?"
Dauke kai maama tayi saboda tasan da ita take bata amsa mata ba ta nufi inna maigado domin duk sunfi sakewa da ita,
"Yanzu ke kuma dan Allah bakiji kunyaba? Kiduba ki gani duk kannenki sunyi aure sun barki, gaku nan ku hudun duk kanku daya" Iyallo tafada tana hararar bilkisu, ai rufe bakin iyallo keda wuya Hindu ta dora,
"Kuji iyallon nan da takura, to dan munyi aure mun barta sai me? Kuma ma naga ba wuce shekarun auren tayiba..."
"Ke kika kulata ma, wai wani nan munyi kai daya da ita to ai halittar tatace mai kyau shiyasa har ba a iya banbance itace babba cikinmu....kum...."
Tsawar da ammah ta daka musune yasa maama yin shiru bata karasa fadar abinda tayi niyya ba nan amma tashiga yimusu fada ta inda take shiga bata nan take fitaba, ita kuwa iyallo cewa take,
"Rabu dasu kibarsu su zageni kamar yadda suka saba, fitsararru dama me suka iya inbanda rashin kunya da rashin arziki? To wallahi bari uban naku yazo..."
Inna maigado ce tasoma tausarta tana bata hakuri ita dasu yafendo, su Hindu kuwa ko ajikinsu asalima tashi sukayi suka bar wurin suka wuce dakinsu.
***
Tunda su iyallo suka zo kowa yashiga takura acikin gidannan gata da fadan tsiya ga sa ido gashi bata iya gani tayi shiru komai tagani sai tayi magna,abinda inna maigado bata iyaba kenan shiyasa kullum cikin yimata fada take wannan dalilinne yasa su bilkisu basa son zuwa garko wurin iyallo saboda fadanta da masifa su maama ne kadai daidai da ita domin basa bar mata.
Haka dai aka cigaba da lallabawa, gida ya cika dam da yan uwan Abba da amma domin itama ana igobe sa lalle yan uwanta suka zo daga dawakin tofa, mota uku suka ciko da yayyenta da kannenta da sauran 'yayan yan uwa, bilkisu kam yanzu tazama ba zama domin har tafi amaren zama busy, ko hamood dinta sai yar hi hi sukeyi, haka shima fahad yanzu bai fiya samunta ba duk da hakan yana sakashi cikin damuwa amma yazaiyi dolensa ya hakura.
Ranar alhamis aka fara gudanar da biki domin ranar ne sakun lalle anan unguwarsu gidan aminin babansu mai sabulu anan akayi kamun kamar yadda al'ada ta tanadar,amare sunsha kyau mutuka cikin shigar da sukayi ta ruwan bula, itama bilkisu itada mama wani leshi suka saka dan ubansu sai walwali suke, an cashe mutuka sannan anwarwasa haka aka tashi kowa cike da farin ciki, agajiye likis bilkisu takoma gida bayan sallar magriba ga dakinta ma cike yake da baki dole sai dakin Abba taje tayi shirin bacci dayake har lokacin shi bai shigoba, ko takan wayoyinta bata biba taje ta kwanta adakinsu meenah domin ta huta.
Washe gari aka daura aure kuma ranar ne zasu gabatar da dinner party dinsu a al-mukarram event center,tun safe amare basu samu zama ba hakama bilkisu bayan an idar da sallar juma'a a babban masallacin dake cikin unguwar tasu ta hotoro aka daura auren, auren Hindu da angonta Mus'ab aka fara daurawa kasancewar itace babba akan sadaki naira dubu talatin sannan aka daura na meenah da angonta Isma'il itama akan naira dubu talatin,gidansu kancame yake da hada hadar jama'a koda akazo yin albishir din daura auren iyallo yada magana tai tayi da habaice habaice duk inda bilkisu tawuce kuwa ko amma ko su Hindu sai ta rakasu da harara su kam basu san tanayiba domin sabgar gabansu sukeyi, maama cema da hudah tayi kashi taje tana cire mata pampers iyallo tazo zata isheta da fadan akan me zatazo gaban rijiya tana yiwa mutane kazanta, ita kuwa maama ta gurmuda mata baki tana farfara ido rankwashi iyallo takai mata tana fadin,
"Fitsararriya yau dinma fitsarar zakiyi min abainan nasi?"
Maama bata kulataba ta sabi yarta tayi falon amma wadda ke can itada danginta da abokan arziki sukuwa su iyallo tasu tawagar ta yan garko suna sitting room.
"Am muga dinkunan...."
Fito dasu yashiga yi daya bayan daya, nan bilkisu tasoma santinsu tana yabawa dasu domin ba karamin tsaruwa sukayi ba koda tazo kan nata ai sai ta raina nasu mamaa domin har na amaren bafin nata kyau yayiba gashi dinkin yafitar da shape mai kyau,
"Kai amma fa dinkin sunyi kyau gaskiya nasamu tailor insha Allah daga yanzu kai zan rinka baiwa dinkuna na"
"To hajiya Allah yakawoki"
Daga haka yadauko babbar leda yafara ninke kayan yana zubawa aciki tana tayishi sai yabon dinkin take, daf da zasu gama zuba dinkin cikin leda ya dubeta ta kasan ido,
"Hajiya ba zaki gayyaceni bikin ba kuma?"
Murmushi bilkisu tayi,
"To ai sai dai ingayyaceka daurin aure"
"Ai ban san angwayenba"
"To zan gayyaceka dinner"
Sai da ya dan bude idanuwanshi sosai sannan ya marairaice murya,
"To ai idan nazo baza abarni inshiga ba tunda babu wanda yasanni"
Murmushi ta kumayi ta mika hannu zata dauki ledar kayan amma sai ya hanata yaci gaba da rikewa,
"Karka damu kowa zai shiga tunda bamu raba gate pass ba"
"To shikenan zanzo insha Allah hajiya.... Kodan inga yanda kayan nan zasuyi miki domin zanso ingansu ajikinki"
Ya karashe maganar ciki ciki ta yadda bazata jiba, ai kuwa bata ji dinba tadai ji abinda yafada dafarko amma daga karshe bata jiba, tana kokarin daukar kayan ya hanata ya daukar mata yana fadin,
"A'a hajiya bari na rakaki dashi"
"Ok nagode amma ina son shiga kasuwa ne akwai abinda zan siya"
"Karki damu babu komai muje"
"To nagode"
Handbag dinta ta dauka suka fito yana biye da ita, suna fitowa hamza na zuwa dan haka fahad bai rufe shagonba yawuce yabi bayanta, har cikin kasuwar ya rakata ta kammala siyan kayan kamshin sannan suka fito bakin titi inda zata hau napep, shine yatsaya domin tare mata amma duk wanda yatare sai yaga da namiji aciki sai yace suje da haka har yatare kusan guda uku ana hudunne yaga namiji daya mace daya, cemata yayi ta zagaya ta saitin macen saita zauna, hakan kuwa tayi ya kinkimi kayanta ya mika mata tana yimasa godiya, baice mata komaiba sai murmushin da yake aika mata dashi can akasan ranshi kuma yana cewa,
"Zanyi missing dinki"
Yana tsaye har saida yaga sun kule sannan yakoma shago, yana shiga da kamshinta yasoma yin arangama nan ya lumshe idanuwanshi aranshi yafurta,
"Kamshinki yafi na kowacce mace"
Zama kawai yayi saman benci yakasa cigaba da aikin da yafara, sai hamza yake tayawa hira wanda ke kan kekenshi yana dinka wani leshi, ahaka yar nacin nasa husna tazo ta sameshi, shifa yarinyar nan har mamaki take bashi kamar ba daliba ba yawonta yayi yawa yakan kasa gane lokacin da take shiga class, yana mata dinkin yana daddaure fuska ita kuwa ko ajikinta dan sai zuba take kamar kanyar da bata da zaki.
***
Haka al'amura suka cigaba da tafiya, abangaren su bilkisu dai kowa kagani acikin hidima yake domin biki yazo gaba daya gidansu angyarashi ansake masa sabon fenti sannan kayan falon amma suma ansakesu tun daga kan kujeru har tv da labulaye da sauransu, ada carpert ne malale afalon amma yanzu tiles akasa mai tsada sai katuwar plasma tv da aka manna abango ga kujeru kirar royal chairs nan falon ammi ya dawo tamkar na yarinya duk da tanata rokon Abba akan yabar gyaran haka yaji da kayan dakin yara domin aurar da yanmata biyu lokaci daya ba wasa ba amma yace itama so yake yadawo da ita amarya ai kuwa hakance tafaru domin gidan ba karamin kyau yayiba dan hatta dakin bilkisu Abba yagyare mata shi ansake mata labulaye sabbi sannan ansaka mata tv yar madaidaiciya abangon dake kallon gadonta sannan gefe ga dan fridge dinta ga uban fenti da dakin yasha nan daki yafito yayi fes dashi. Ana saura kwana biyu biki dakyar bilkisu tasamu ta tafi saloon da kunshi itada kawarta khulsum ba ita tadawo gidaba sai karfe biyar saura tana shiga dakinta tajiyo sallamar mutanen garko wato su iyallo, kasancewar daga ita sai daurin kirji yasa bata fitoba domin tana jiyo maganar ya mudan da alama shine yakawo su. Kai tsaye iyallo dakin bilkisu tashiga lokacin ita kuma tana toilet, ganin irin gyaran da dakin yasha yasata rike haba tana tafa hannaye tana zuba salati,
"Ah lallai wannan shine zama daram wato babu ma ranar tashi, irin wannan daki haka kamar agidan miji? Tab... To Allah yasawwaka, iye... Lallai.... Duniya sabuwa"
Juyawa tayi tabar dakin tafita ta nufi cikin gidan wato falon amma wadda ke can tana gaggaisawa da baki domin iyallo ba ita kadai tazo ba su wurin takwas sukazo ciki harda yayarta inna maigado takwarar bilkisu da kuma yayanta guda biyu wato kannen Abba gwaggo uwa da yafendo sai "yayansu,nan tazauna tana tabe taben baki da harare harare, sama sama ta amsa gaisuwar amma nan da nan aka cikasu da ruwa, lemo da abinci tunda dama ansan da zuwansu, shi dai ya mudan bai wani jimaba yakoma yabarsu anan. Bilkisu sarai taji abinda iyallo take fada lokacin da tashigo dakinta, tana wanka tana zancen zuci,
"Su iyallo trouble maker ansauka, haka kuma za ayita fama har sai ranar da kika bar gidan nan, Allah yarabamu lafiya"
Da zancen zuci tagama wankan tafito, ta shirya agaggauce tana saka kaya su Hindu na shigowa shiyasa koda tafito tare suka rankaya falon amma........
*_Ummi Shatu_*
© _*HASKE WRITERS ASSO.*_
*KAMAR DA WASA....!*
_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*
*7*
***Su maama sai yaba kunshin nata sukeyi yayinda ita kuma take yaba kwarewar mai gyaran jikinsu domin kwana uku kacal da fara yimusu har ta sauya musu kamanni, Hindu da maama sarakan rashin kunya ganin takalmansu iyallo tuni suka tura dan kwali gaban goshi duk da hararar da bilkisu keyi musu haka suka dauke kai, itace tafara shiga cikin falon uwar harara iyallo ta tarbeta da ita tana tabe baki sabanin inna mai gado da ta washe hakora tana yimata lale tamkar zata goya bilkisu dan murna da tsantsar kaunar da take yimata, suna tsaka da gaisawa su maama suka shigo, maganar iyallo ita ta katse kowa daga gaishe gaishen da akeyi,
"Ke samodara daga ina kika tafi kika bar yar labibiyar yarinya dan tsabar rashin hankali?"
Dauke kai maama tayi saboda tasan da ita take bata amsa mata ba ta nufi inna maigado domin duk sunfi sakewa da ita,
"Yanzu ke kuma dan Allah bakiji kunyaba? Kiduba ki gani duk kannenki sunyi aure sun barki, gaku nan ku hudun duk kanku daya" Iyallo tafada tana hararar bilkisu, ai rufe bakin iyallo keda wuya Hindu ta dora,
"Kuji iyallon nan da takura, to dan munyi aure mun barta sai me? Kuma ma naga ba wuce shekarun auren tayiba..."
"Ke kika kulata ma, wai wani nan munyi kai daya da ita to ai halittar tatace mai kyau shiyasa har ba a iya banbance itace babba cikinmu....kum...."
Tsawar da ammah ta daka musune yasa maama yin shiru bata karasa fadar abinda tayi niyya ba nan amma tashiga yimusu fada ta inda take shiga bata nan take fitaba, ita kuwa iyallo cewa take,
"Rabu dasu kibarsu su zageni kamar yadda suka saba, fitsararru dama me suka iya inbanda rashin kunya da rashin arziki? To wallahi bari uban naku yazo..."
Inna maigado ce tasoma tausarta tana bata hakuri ita dasu yafendo, su Hindu kuwa ko ajikinsu asalima tashi sukayi suka bar wurin suka wuce dakinsu.
***
Tunda su iyallo suka zo kowa yashiga takura acikin gidannan gata da fadan tsiya ga sa ido gashi bata iya gani tayi shiru komai tagani sai tayi magna,abinda inna maigado bata iyaba kenan shiyasa kullum cikin yimata fada take wannan dalilinne yasa su bilkisu basa son zuwa garko wurin iyallo saboda fadanta da masifa su maama ne kadai daidai da ita domin basa bar mata.
Haka dai aka cigaba da lallabawa, gida ya cika dam da yan uwan Abba da amma domin itama ana igobe sa lalle yan uwanta suka zo daga dawakin tofa, mota uku suka ciko da yayyenta da kannenta da sauran 'yayan yan uwa, bilkisu kam yanzu tazama ba zama domin har tafi amaren zama busy, ko hamood dinta sai yar hi hi sukeyi, haka shima fahad yanzu bai fiya samunta ba duk da hakan yana sakashi cikin damuwa amma yazaiyi dolensa ya hakura.
Ranar alhamis aka fara gudanar da biki domin ranar ne sakun lalle anan unguwarsu gidan aminin babansu mai sabulu anan akayi kamun kamar yadda al'ada ta tanadar,amare sunsha kyau mutuka cikin shigar da sukayi ta ruwan bula, itama bilkisu itada mama wani leshi suka saka dan ubansu sai walwali suke, an cashe mutuka sannan anwarwasa haka aka tashi kowa cike da farin ciki, agajiye likis bilkisu takoma gida bayan sallar magriba ga dakinta ma cike yake da baki dole sai dakin Abba taje tayi shirin bacci dayake har lokacin shi bai shigoba, ko takan wayoyinta bata biba taje ta kwanta adakinsu meenah domin ta huta.
Washe gari aka daura aure kuma ranar ne zasu gabatar da dinner party dinsu a al-mukarram event center,tun safe amare basu samu zama ba hakama bilkisu bayan an idar da sallar juma'a a babban masallacin dake cikin unguwar tasu ta hotoro aka daura auren, auren Hindu da angonta Mus'ab aka fara daurawa kasancewar itace babba akan sadaki naira dubu talatin sannan aka daura na meenah da angonta Isma'il itama akan naira dubu talatin,gidansu kancame yake da hada hadar jama'a koda akazo yin albishir din daura auren iyallo yada magana tai tayi da habaice habaice duk inda bilkisu tawuce kuwa ko amma ko su Hindu sai ta rakasu da harara su kam basu san tanayiba domin sabgar gabansu sukeyi, maama cema da hudah tayi kashi taje tana cire mata pampers iyallo tazo zata isheta da fadan akan me zatazo gaban rijiya tana yiwa mutane kazanta, ita kuwa maama ta gurmuda mata baki tana farfara ido rankwashi iyallo takai mata tana fadin,
"Fitsararriya yau dinma fitsarar zakiyi min abainan nasi?"
Maama bata kulataba ta sabi yarta tayi falon amma wadda ke can itada danginta da abokan arziki sukuwa su iyallo tasu tawagar ta yan garko suna sitting room.